Showing 135001 words to 138000 words out of 145203 words
na son horashi kaɗan ba. Haka ya gama magiyar sa ya bar wajen....
Bayan kwana biyar da haukar Naomi Pastor ya bada shawaran a je a bawa wanda ta yiwa magani haƙuri saboda idan su ka yafe hakan zai sa Naomi ta samu sauƙi.
Mrs Comfort, Pastor Chukwudi da Saint Janet suka je gidan su Najeeb. Maigadi ne ya sanar da su Farida tana gidan au Najeeb, su ka karɓi address a wajen shi su ka wuce chan...
Mrs Comfort kuka ta dinga yi wiwiwi a gaban su Farida tana roƙon su gafartawa Naomi. Daddy ya ari bakin Najeeb da Farida ya ce sun yafe, Najeeb ya haɗe rai dan shi plan ɗin shi ma sai Naomi ta je jail.
Pastor ya mu su godiya sannan su ka tafi. Duk da wannan yafiya da aka yi bai sa Naomi ta warke ba. Kwana biyu da dawowar su daga gidan su Najeeb ta tsere daga gidan Pastor ta shiga gari. Wasa-wasa aka baza neman ta amma har sati guda ba labarin inda ta ke...
.........................
Shirye-shiryen bikin Sabreen ake yi duk da kuwa Sabreen da Lukman ɗin sun amince akan ba za ayi hidima ba amma Mom da Farida sun ƙi. Wata guda aka saka har yanzu kuma saura sati uku.
Fitowarta kenan daga wanka ta kalleshi zaune akan gado. Mantawa ma ta yi ba tarufe ƙofan ba.
"Ni fa ba na so ana shigo mini ɗaki ba izini"
A hankali ya taso ya zo ya tsugunna gaban ta ya kamo hannunta biyu ya riƙe gam. Kallon sa ta ke yi yadda idon sa yai ja.
"Aysherh I cant, ba zan iya ba. Kafin 3 months ɗin nan zan iya mutuwa idan ba kya tareda ni. Please ki manta da komai ki dawo gida mu cigaba da rayuwar mu. I promised to make it up to you, ba zan sake ɗaukan sakatariya ma ce ba, yalla yarinyace ko tsohuwa. Zan dage da addu'an dare saboda kar wata ta kuma samun galaba a kaina. Zan yi duk abinda ki ka ce amma please come back to me. I love you"
Ya kai hannun ta kan kirjin sa ya ce " My heart beats for you Aysherh, only for you. Ki taimakeni ki taimaki zuciyata kar rashin ki kusa da ni ya min illa. Na ɗauka zan iya jurewa amma Wallahi ba zan iya ba, its being 2 weeks amma gani na ke kamar 2 years ne. I miss you Aysherh, I miss us. Please my Queen..."
*team Farida kun karɓi haƙurin Najeeb ko ya?*
Skt 57
"Ka yi haƙuri amma ba zan koma yanzu ba" ta faɗa a hankali duk da kuwa maganganun sa sun karya ma ta zuciya.
Ya cize leɓen sa na ƙasa yana huci, bayan 'yan daƙiƙai ya miƙe tsaye ya ce "tunda abinda ki ke so kenan zan jira ki"...
Ba ta iya ɗaga ido akan sa ba har ya fita daga ɗakin.
Anya ta ma sa adalci kuwa? Ta tambayi kan ta. Sai dai kuma ta rasa gane amsar da za ta bawa kan ta...
Yinin ranan sai sintiri ta ke tsakanin falo da ɗaki amma Najeeb bai dawo ba. Washe gari ma bai zo gidan ba...
Su uku ne a dining su na cin breakfast lokacin da Najeeb ya shigo. Kwana biyu kenan bai zo gidan ba.
Wajen Mom ya je ya gaisheta, ta shafa gashin sa tareda ma sa peck a goshi.
Ya duba Sabreen ya ce "amarya ya shirye-shirye"
Sabreen ta yi murmushi ta ce "shiri ai sai su Mom da Ayshah, su ke ta komai"
"Allah ya kaimu lokacin"
Mom ta amsa da amin yayinda Sabreen ta sunkuyar da kai tana murmushi.
"Zan wuce Abuja, i'll be there for two days"
Mom da Sabreen su ka ma sa addu'ar Allah ya kiyaye.
Farida tunda ya zo ta ke binsa da ido amma bai ko kalli wajen da ta ke ba.
Ganin ya juya zai tafi ya sa ta yi saurin sake mug ɗin tea da ta riƙe, Mug ɗin ya faɗi kan tile ya ɗan fashe.
"Ouch...Ouch ... Wayyo zafi..." Farida ta faɗa saboda tea ɗin ya ɗan fetsu ma ta.
"Sannu Ayshah, sannu, ba ki ji ciwo ba ko?" Mom ta faɗi tana ƙoƙarin riƙe hannun Farida.
Farida kam idon ta na kan Najeeb wanda ta ke tunanin zai zo da gudu ya dubata. Sai taga saɓanin haka tsayawa kawai yana kallon ta.
Ɗan gyaran murya yai ya ce " na tafi"
Farida na jin haka ta fashe da kuka.
Sabreen mi za ta yi banda dariya. Mom ma dariyan ta ke son yi amma ta gimtse.
Har ya fita Farida bata dena kuka ba. Sabreen ta ce "someone is missing her husband"
Farida ta kalleta ta galla ma ta harara. Mom kam yi ta yi kaman ba ta san sunayi ba, Adama ma ta kira akan ta zo ta tattare wajen da Mug ɗin ya fashe...
Ƙarshe haushi ya sa Farida tashi daga wajen ba tareda ta gama cin abincin ba...
...........................
Tana jiran kiran sa ko text amma shiru. Baƙin ciki ya tokare ma ta maƙoshi, kowa ma haushin sa ta fara ji a gidan. Sabreen kuwa indai su ka haɗu sai ta tsokaneta akan Najeeb.
Ranan da zai dawo ta samu Mom a ɗakin ta da su ka gaisa ta ce "Mom zan je na ɗau wassu kaya a chan gida"
Mom ta yi murmushi dan ta gano Ayshah na son komawa gidan ta ne. Ta ce " 'yata ni inaga horon ya isa haka, Son zai cutu idan ki ka cigaba da zama a nan"
"Amma Mom..."
Mom ta katseta da cewa "ki yi haƙuri ki koma kin ji"
Farida ta yi ajiyar zuciya ta ce "shikenan zan koma saboda ke"
Mom ta ce na gode. Sai da Farida ta fita sannan Mom ta yi murmushin manya...
Farida ta kira Adama ta tayata haɗa kaya, da su ka gama ta kai ma ta su cikin mota. Da ta shirya ta je ta yiwa Mom sallama sannan ta shiga ɗakin Sabreen. Waya su ke da Lukman lokacin da ta shigo, tana kallon ta da jaka ta sa dariya har da hawaye.
"Ni ba na son gulma, Mom ce ta ce na koma" Farida ta faɗa tana haɗa rai.
Sabreen ta ce " to Allah ya kiyaye hanya sai mun zo karɓan tsaraba"...
Saloon ta fara wucewa aka ma ta gyaran gashi da lalle sannan ta wuce gida. Ko'ina na nan tsaf-tsaf saboda Tasallah ba ta wasa da gyaran gidan.
Lokacin da ta shiga ɗaki wanka ta yi ta feshe jikin ta da turaruka.
Ƙarfe biyar na yamma Abdullahi ya faɗa ma ta zai je ya ɗauko Najeeb a airport yanzu kuma ƙarfe huɗu da kwata.
Gyara ɗakinta ta yi kafin ta wuce na shi ɗakin. Yana nan a gyare amma sai da ta cire zanin gado ta sake sa wani sannan ta shiga banɗaki dan ta wanke...
Tun ƙarfe biyar da kwata ta ke tsaye jikin balcony na falon sama tana jiran dawowarshi amma Abdullahi bai shigo gidan ba sai ƙarfe shida saura minti goma. Tana ganin ya fito daga motan ta yi saurin barin wajen. Ɗakin sa ta shiga ta fara gyara arrangement na turaruka da mayukan sa...
Ta ji shigowar sa amma ta dake ba ta kulashi ba ta cigaba da gyaran har da faɗin " duk an bar ɗaki a hargitse. Komai gashi nan ba tsari kaman ba mutum ke kwana a ɗakin ba"
Yana tsaye yana kallon ta bai ce komai ba duk da farin cikin da ya mamaye zuciyar sa.
Ya ajiye jakar sa ya shige banɗaki ba tareda ya ce ƙala ba. Tana binsa da wutsiyar ido har ya shige banɗakin.
Ta ɗan yi ƙaramar tsaki ta ce " koma ya nuna ya gannin nan"
Ta zauna bakin gado tana jiran sa. Ya jima a banɗakin kafin ya fito sanye da bathrobe fari.
"Ni fa kar mutum ya ga na zo ya nemi yi min walaƙanci Mom ce ta ce na zo."
Shiru Najeeb bai ce komai ba. Ta ɗaga ido ta kalleshi yana tsaye gaban mirror yana shafa jikin sa da mai.
"Allah na gani sai na tafi tunda ba a son ganina, dama ba wai da son rai na na zo ba"
Najeeb ya ajiye man da ke hannun sa ya je ya buɗe ƙofar ɗakin ya ce " a gaida Mom da su Sabreen. Allah ya kiyaye hanya"
"Kuturun Uban chan. Au'uzubillahi har ka sa ina zagi"
Ta tashi fuuuu ta ce " zan tafi ɗin koma ba za ka sake ganina ba"
Sai da ta zo shigewa ta ƙofan ya riƙe hannun ta.
"Ni ka sake ni in tafi, ka sake ni na ce"
Ya jawota jikin sa yana kallon ƙwayar idon ta. Itama ɗin kallon sa ta ke ƙirjin ta na bugawa da sauri-sauri ba abinda jikinta ke muradi irin tajita kwance kan faffaɗan ƙirjin sa.
"My stubborn Mrs Jibo. Na san duk maganan nan cika baki ne kawai, you miss me, i see it in your eyes"
"Ba wani. Ni dama taimakon ka zan yi tunda Mom Allah Annabi ta roƙeni akan na dawo"
"Oh really?" Ya faɗa tareda sunkuyo da kan sa, ganin yana matso da bakin sa kusa da nata bakin ya sa ta lumshe ido tana jiran haɗuwar bakin su.
Maimakon kiss a baki sai ya kissing kumatun ta. Ta buɗe ido a hankali gaba ɗaya ta yi laushi saboda wani mugun sha'awar sa da ke taso ma ta.
Murmushi ya ma ta ya sake matsowa da bakin sa wannan karan kam tuni ta yi saurin matsawa da nata bakin, bakin su ya haɗe waje guda...
Sun jima suna aikawa junan su hot kiss kafin ya jawota zuwa kan gadon. . Wata ɗaya da 'yan kwanaki rabonta da shi, ba ƙaramin missing ɗin sa ta yi ba. Yadda ya ke sarrafata haka itama ke mayar ma sa da martani, sun jima su na gogar junan su saboda an jima ba a gamu ba...
Bayan komai ya kankama da su ka yi wanka Najeeb ya ce " ki shirya na maida ki wajen Mom na haƙura ki huta a chan"
Duka ta kai ma sa ya goce yana dariya...
..........................
Rayuwan masoyan gwanin sha'awa, kullum su na manne da juna. Duk dare sai sun tashi sun gudanar da sallah sun roƙawa junan su addu'an samun zaman lafiya da kuma samun 'ya'ya ma su albarka. Duk Jumu'ah Farida ba ta fasa yin sadaka ba...
Ranan Asabat aka ɗaura auren Sabreen da Lukman. Daddy ne ya zama alwalin Sabreen 'yan uwanta sun zo ba laifi, wannan karan har mahaifiyarta sai da ta zo. Anyi walima kuma anyi family dinner a gida. Washe gari Sunday kuma aka wuce da Sabreen Abuja. Farida ta so zuwa amma Najeeb ya hana saboda yanzu ta yi nauyi.
Duk cikin 'yan uwanta babu wanda ya nuna damuwar sa da asalin Lukman, su daɗin su ne ma Allah ya shirya mu su Sabreen har kuma ta yi aure hankali kwance...
.......................
Wanda su ka kawo Sabreen mutum huɗu ne Mom ce da Najdah sai Aunt Mouna da wata cousin ɗin Sabreen ɗin Nihaya. Ba su fi awa biyu a gidan ba suka koma bayan sun yiwa Sabreen 'yan nasihohi.
Ƙarfe biyar Lukman ya shigo gidan na su. Cike da farin ciki, finally shima ya zama ango...
Ƙarfe takwas saura su ka gabatar da sallan Isha tareda sallar godiya sannan Lukman ya gabatar ma ta da kazarta. Tare su ka ci kazar su ka ƙoshi sannan Lukman ya tattare wajen...
Kunyar Lukman ta ke ji, ta sani ita ba irin matar da ta dace da Lukman ba ne. Ya fi ta daraja da kima duk da kuwa ta fishi asali.
"Ka yi haƙuri ba nida abin da kowane ango ke farin cikin samu a rana irin ta yau. Na yi rayuwa marar daɗi a baya, na zubda mutuncina a idon duniya, na ɗauka rayuwa mai kyau na ke yi, rayuwa ta 'yan ci da jin daɗi amma a gaskiya rayuwar ƙunci na yi a baya. Ka yi haƙuri dan Allah. Ina godiya da Allah ya bani kai. Ba ka dubi yawan shekaruna ba, ba ka dubi rayuwar bariki da na yi a baya ba amma ka amince da ni ka amince na zamo sashen rayuwar ka. Thank you Lukman"
"Shhhhhh" ya faɗi tareda haɗe bakin su...
Sabreen ta sha gyara sosai, duk da ta saba amma Lukman ya bata mamaki saboda yadda ya birkitata da salon sa, sai takejin ba ta taɓa tarayya da wani da yai kusan sa a iya sarrafa mace ba....
Skt 58
*ina roƙon duk wanda ya karanta wannan shafin yai wa Mijin Maman Durratu addu'a, Allah ya jiƙan sa da rahama, ya haskaka ƙabarin sa, ya gafarta ma sa ya kuma bawa iyalen sa haƙuri da juriyan rashin sa, Amin. Wanda su ka rigamu gidan gaskiya Allah ya jiƙan su da rahama, muma idan tamu ta zo Allah ya sa mu cika da imani amin*
Yau tun safe ta ke jin ta ba dai-dai ba. Ta dai daure ta cigaba da ayyukan da ta saba. Yana fitowa daga wanka ta riga ta cire ma sa kayan da zai sa. Ita ta shafa ma sa mai sannan ta taimaka ma sa ya shirya. Tana gyara mi shi tie ɗin ya ce "my Queen lafiya? You look dull this morning"
"Just ƙafafuwa na ke ciwo" ta faɗa dan kawai kar ta tada ma sa hankali
"Ko za mu je ki ga likita?"
"No, zai yi sauƙi zuwa anjima"
Ta ɗan bugi ƙirjin sa kaɗan ta ce " mijina ka ga yadda ka yi kyau. Dan Allah ban da dogon hira da mata, banda lumshe mu su ido, ban da yi mu su murmushi, ka ji nawan"
Ya ɗan ja kumatunta ya ce "na ji your highness zan kiyaye duk abinda ki ka ce" light kiss ya manna ma ta a baki kafin ya ja hannunta su ka bar ɗakin...
Tafiyar Najeeb office da awa uku Farida ta fara naƙuda. Ɗanliti sabon dreban ta ya wuce da su asibiti. Tun a hanya Tasallah ta kira Mom ta gaya ma ta. Su na zuwa asibitin ko minti arba'in ba ta cika ba ta haihu.
Abin ya zo ma ta da sauƙi gaskiya, kuma Alhamdulillah ba wata matsala...
Tana kwance an kaita ɗakin hutu Mom na gefe tana kallon jaririn mai kama da uban sa. Cikin zuciyarta ta ke godiya wa Ubangiji da ya sa ta ga ɗan Najeeb.
Mom ta miƙawa Farida jaririn tana faɗin "he look just like his father"
Farida tana kallon jaririn tana godiya bisa wannan ni'ima da Allah ya ma ta...
Bayan minti talatin da haihuwar kafin Najeeb ya iso asibitin. He cant believe it sai da ya ga jaririn, Mom ce ta kirashi ta ma sa albishir da haihuwan. Bai kawo haihuwa ba tunda ya bar Farida lafiya gashi kuma EDD ɗin ta saura kwana shida. Sai dai al'amari na Allah yafi gaban kowa.
Ya ɗau yaron yana murmushi tareda kissing goshin yaron. Alhamdulillah ya ke ta maimaitawa a fili, bakin sa ya ƙi rufuwa saboda farin ciki.
Ƙarfe huɗu da rabi aka sallame su daga asibitin su ka dawo gida. Kafin dare gidan na su ya cika da Jama'a. Kowa na zuwa ganin babyn Farida.
................................
Gidajen biyu sun kasance cikin farinciki bisa wannan ƙaruwa da aka samu. Da farko Mom ta so Farida ta dawo wajenta amma gogan sam bai ba da dama ba.
Mom za ta je gidan su tun safe sai dare ta tafi. Ita ke yiwa Farida wanka. Ummi ma kullum sai ta zo duba Farida da jikar ta.
Kafin ranan suna gidan an cika shi da tarkacen yara. Wassu abin ma jaririn kafin ya iya amfani da su sai ya shekara uku amma an siye su tun yanzu.
Ranan suna yaro ya ci sunan *Muhammad Yaman*
(Finally Farida an zama Umm Muhammad🤓)
Mutane ba kaɗan ba su ka halarci waliman wannan suna, tun daga mutanen Gombe zuwa na Wase da Jos kowa ya karkaɗe jiki ya zo. Sabreen da Lukman ma saura kwana ɗaya suna su ka dira a Kano. Yaro ya samu kyaututtuka ba adadi.
Sorveniers sa aka raba ba za su irgu ba. Saboda gudun evil eye, sunan yaro kawai aka sa babu hoto. Washe gari aka yi abincin sadaka aka kai Iskalin Almajirai sunfi ishirin...
Rayuwa ta cigaba da tafiya hakanan soyayyar Najeeb da Farida tana tafiya gwanin sha'awa. Baby Yaman ba ƙaramin gata ya ke gani a wajen iyayen sa ba, ga uwa uba kakannin sa. Kowa son ɗaukan sa ya ke idan aka fita da shi, amma miskilin yaro ba kowa ya ke yarda ya ɗauke shi ba. Ko Tasallah da ƙyar ya ɗan saba da ita ya dena kuka idan ta ɗauke shi...
Kamfanin Najeeb sai daɗa bunƙasa ta ke yi, yanata samun buɗi ta ko'ina...
Wannan zuwan Farida gida lokacin Yaman yana ɗan wata huɗu ta lura da cikin Ummi. Ko ya akayi ma ba ta lura da shi ba sai yanzu oho dan aƙalla cikin zai kai wata shida.
"Ummi dan Allah ki haifo mace na samu ƙanwa nima"
Ummi ta ma ta daƙuwa, Farida ta sa dariya, dan ta gane Ummi kunyar cikin ta ke ji...
....................
Aneesa da Maijiddah sun saita kan su, sun dena kishin hauka. Aneesa ta yadda duk makaman yaƙinta, sosai ta ke kula da miji da yaranta tunda yanzu ba inda ta ke zuwa. Ciki ma ta ke da shi amma ta kasa sanar da Abdulwahab dan kar yai zaton ƙarya ta ma sa irin wancan karan.
Daren wata Monday AbdulWahab yana ɗakinta ya ke ma ta maganar wani abokinsa da ya buɗe sabon kamfani, yana yi ma sa tayi akan ya bar Aneesa ta jagoranci ɓangaren sales and marketing saboda experience da ta ke da shi.
"Mi ki ka gani?"
"Duk abinda ka ce Sweetheart" ta faɗa tana kai hannunsa daidai cikinta. Jin ɗan tauri-tauri da cikin yai ya sa shi duban Aneesan da kyau yana neman ƙarin bayani. Ta ɗaga ma sa yatsu huɗu tana murmushi.
"Da gaske?"
Ta gyaɗa ma sa kai. Ya jawota jikin sa sosai yana hamdala...
Bisa amincewar AbdulWahab ta fara aiki wanda 8am-2pm za ta dinga yi duk rintsi zuwa uku da rabi ta dawo gida randa ba ta samu traffic sosai ba ma kafin ƙarfe uku ta iso gida. Cikin be zo ma ta da wani laulayi ba shiyasa ta ke gudanar da lamuranta cikin sauƙi. Ita kuwa Maijiddah sosai Al'amin ɗinta yai wayo, kowa na son yaron a gidan ba ma kamar yayunsa Baby da Alizah, indai su na gida sun dinga faɗa akan sa kenan kowa na