Showing 129001 words to 132000 words out of 145203 words

Chapter 44 - SAKATARIYA TA COMPLETE

Azizat   

13 Jul 2024

25701

ba sai ga Najeeb ya shigo gidan. Tana zaune a falo tana kallo ya shigo, a zahiri za ka ga kaman kallon ta ke amma ba kallon ta ke ba, hannunta akwai carbi tana jan Ya Hayyu Ya Qayyum.

Ba ta ma sa magana ba haka ya hau sama da gudu kaman zai tashi sama.
Tana ganin ya shiga ta kira Abdullahi akan ya shigo...

Duk yadda ta yi ya zauna a kan kujera ya ƙi. A ƙasa ya zauna su ka gaisa.

"Malam Abdullahi ina fata lafiya?"

" Hajiya dan Allah ki yi haƙuri da abinda zan gaya mi ki"

Farida ta ce ba komai.
Nan ya shiga gaya ma ta abinda ya lura tsakanin Najeeb da Naomi. Ya faɗa ma ta jiya da ya kai su hotel ne Najeeb ya fara ciwo amma da lafiyar sa ƙalau. Ya ƙara da cewa " Hajiya kar ki tsorata amma akwai asiri ajikin Alhaji. Wannan cegiyar arniyar ta yiwa Alhaji asiri"

Duk da gaban ta ya faɗi amma hakan bai sa ta ji tsoro ba, dan tunda Ummi ta ba ta shawarwari ta sa a ranta sai inda ƙarfinta ya ƙare akan yiwa Najeeb addu'a.

Ta yiwa Abdullahi godiya ta sallameshi...

Sai da ta leƙa ɗakin sa ta ga yana bacci kafin ta wuce na ta ɗakin. Ɗazu ta tsiyayi ruwan zamzam a hannunta ta tofa ƙula'uzai a ciki sannan ta yayyafa a gadon sa da duk kujerun sa...

Ƙarfe biyu da rabi ta tashi ta fara gabatar da sallah tana addu'a ba ta kwanta ba har asuba. Ƙarfe shida ta fito ta taya Tasallah haɗa ma sa breakfast duk da ma Tasallah ta ce tea kawai ya ke sha yanzu. Acikin tea ɗin ta tsiyaya ma sa ruwan zamzam kaɗan wanda shima ta tofeshi da addu'o'i...

Da za ta haura sama ta ce da Tasallah ta kai kuɗi gidan da ake musu kunu da ƙosan sadaka lokacin da Najeeb bai da lafiya su ma ta sadaka.
Ita kan ta Tasallah ta san akwai matsala a gidan dan masoyan da kullum su na manne da juna sai ga shi yanzu ko kallon kirki ba sa yiwa junan su.

Saboda bacci da ke idon tana shiga ɗaki bacci ta yi. Ba ta farka ba sai ƙarfe tara. Ta yi wanka ta shirya ta sauko. Kaman yadda Tasallah ta ce tea ɗin kawai ya sha ya fita.
Ta zauna a dining ta ci abinci sosai, ba wai dan daɗi ba sai dan ɗan da ke cikin ta.

Ƙarfe shaɗaya ta wuce gidan su Najeeb. Mom ta riƙa ba ta haƙuri tareda da nuna ma ta Najeeb yana cikin matsala dan jiya sa'insa su ka yi da Daddy akan ya ce zai auri Naomi.

Cikin kuka ta ce " he has never raised his voice to his father, amma jiya..." kuka ya kufce ma ta.

"Mom dan Allah ki dena kuka, addu'a za mu dinga ma sa har Allah ya kawo ma na ƙarshen wannan bala'i"...

Ta jima a gidan dan sai bayan Azahar ta tafi.
Anguwar su ta wuce amma ba ta kai gida ba ta tsaya a gidan su Saminu.
Saminu abokin Yakubu ne, amma tun secondary school ya lalace da shaye-shaye. Yanzu haka ba shi da aikin yi sai maula gidan 'yan siyasa, idan lokacin zaɓe ya zo sune 'yan bangan siyasa.
Duk da halin su da ya banbanta amma ba su dena mutunci da Yakubu ba. Lokaci zuwa lokaci yana zuwa wajen Yakubu ko kuma su haɗu a majalisa.

Da ta je gidan dai cewa aka yi Saminun baya nan amma an bata numbar shi.

Tana fitowa daga gidan ta kira numbar ringing ɗaya kuwa aka ɗauka.

"Kai ɗan dambulan 'wa ina ka shiga, na je shagon ka ban sameka ba" abinda Saminu ya fara faɗi kenan.

"Haba Saminu a bi a hankali mana"

Jin muryan mace ya sa Saminu ya fara washe baki yana faɗin sorry Hajiya.

"Suna na Farida ƙanwar Yakubu ɗan gidan Alhaji Musa Wase"

"Kai kai ashe Hajiya Farida ce. Ki gafarceni dan Allah na ɗauka wani banzan yaro ne"

Farida ta ce ba komai

"Ina son ka min wani aiki ne ka ɗan samu wani abokin ka sai ku zo. Za ku samu 'yan chanji na siyan kati"

Saminu ya sa ihu yana faɗin koma minene za su yi...


Farida ta yi murmushi ta ce "Naomi miji na ki ke so ko?. Fine, za ki same shi da kyau"...

...............................


Tana zaune tana duba kayyayakin da su ka siyo ɗazu ta ji wayarta na ringing. Da sauri ta ɗauka dan tunanin ta Najeeb ne ganin sunan Madam Farida ya sa ta yi tsaki. Ko me ta ke nema a wajena oho.
Kamar ba za ta ɗauka ba sai kuma ta ɗauka.

"Naomi Naomi, Naomi Masoyi. Naomi matar Najeeb ko?. Fatan kina lafiya? Ina son ganin ki ya za ayi ne?"

Naomi ta ja tsaki ta ce " ba za ki ganni ba. Na san plan ɗin ki bai wuce ki dake ni ba"

Farida ta yi dariya ta ce "Allah ko? To barin zo sai mu ga ko dukan na ki da gaske zan yi"...

Naomi ta kashe wayan tana tsaki. Baifi minti goma ba sai ga shi Mrs Comfort na kiran ta akan ta zo ta buɗe ƙofa ana ƙwanƙwasa ƙofa.
"Mama ina Abel, ya je ya buɗe mu su"

Mrs Comfort ta ɗaga murya tana faɗin " wai ba za ki fito ba. Abel baya nan fa"

Naomi ta yi tsaki sannan ta fito.

Mrs Comfort na zaune a kan keken guragu tana karanta bible Naomi ta zo ta buɗe ƙofa. Naomi ta zaro ido lokacin da ta ga Farida tsaye, bayanta kuma wassu samari biyu ne wanda da ka gan su ka san a buge su ke.
Ta ja da baya da sauri tana faɗin Mama.

Suna shigowa Farida ta ce "Saminu rufe min ƙofa dan Allah"

Naomi gefen Mrs Comfort ta tsaya jikin ta na rawa.

Farida ta kalli Falon na su da kyau sannan ta ce " Mrs Comfort ban san ko da sa hannun ki Naomi ta asirce min miji ba, har ta ke son auren shi"

Mrs Comfort ta zaro ido, Ita da ta tsani musulmai shi ne za ta bari 'yarta ta yi tarayya da musulmi. Ta dai lura da yawan kayyakin da Naomin ke zuwa da su kwana biyun nan, kuma ta yiwa Naomin magana amma ta ce saurayin ta ne ke siya ma ta.


"Ni ban san komai ba. Naomi wai mijinta ki ke so?"


"Madam Farida ki fita a gidan mu ko na kira police"

Farida ta kwashe da dariya ta ce " ina da numban comissioner of police zan baki sai ki gaya mi shi ƙorafin ki amma kafin nan..."

Ta kalli Saminu ta ma sa ishara da ido. Shi da ɗayan da su ka zo da ake cewa Maska su ka yi kan Naomi. Naomi ta yi hanyar ɗaki tana ihu amma ko takun kirki ba ta yi ba, Maska ya cafko ta.

Kujeran da ke wajen ɗan ƙaramin dining ɗin su Saminu ya ɗauko. Aka zaunar da Naomi ana ɗaureta bayan sun fara rufe bakin ta saboda kuka da ihu da ta ke yi.

"Tsirara za ku ma ta" Farida ta faɗa da ƙarfi.

Maska ya yaga vest ɗin da ke jikinta, mini skirt ɗin ma ya yage ta ya saura daga ita sai pant.

"Shi ma ku cire" Farida ta faɗa ba alamar wasa a fiskarta.

"Plz Madam Farida, i beg you. Naomi za ta bar mi ki mijin ki, plz dont kill her" Mrs Comfort ta faɗa tana kuka.

"Ni ba kisa zan yi ba, zan dai ɗanɗana ma ta kaɗan daga azabar da za ta ji duk ranan da ta sake neman mijina ne"

Ta kalli Saminu ta ce "bar ma ta pant ɗin, zai ma sa cirnakun su ci gindinta sosai"

Handglove ta cire ta miƙawa Saminu. Saminu ya ce " Hajiya barshi zan sa hannu kawai"

"A'a ka dai saka ɗin"

Ya karɓa handglove ɗin yana sawa. Daya gama Maska ya fito da wata leda wanda kwalbar Bama mayonnaise ne aciki cike da cirnaku baƙaƙe da jajaye.

Saminu ya ɗebo cirnakun nan ya sa hannu cikin pant ɗin ta ya zuba su. Har da cuccusawa cikin abun ta.
Da ya gama ya zuba sauran a cinyayyen gashinta, dama ta riga ta cire wig ɗin da ke kan ta. Sauran ya sa a bayanta....



*SAKATARIYA TA*
.......(My Secretary).......


*Azizat......✍*
*Wattpad @000Azee*


*BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM*


0️⃣5️⃣4️⃣





Naomi sai zazzare ido ta ke yi tana kici-kici akan kujera, idonta yai ja ga gumi da ke ta tsatstsafowa a jikinta. An ɗaure hannu da ƙafa ga bakin ma an kulle ba halin kuka.

Mrs Comfort ta turo kekenta zuwa wajen Farida da ke tsaye tana kallon Naomi.

"Plz Madam Farida, i beg you in the name of the Almighty God stop this. Naomi za ta bar mijin ki i promised you that"

Jin yadda Mrs Comfort ke roƙo tana hawaye ya sa ta ɗan ji tausayin ta.

Ta ciro Shentos insecticide a jaka ta miƙawa Saminu.
"Fesa ma ta su mutu, tunda uwarta ta roƙi alfarma"

Saminu ya ƙarɓa ya fara fesa wa Naomi a kanta da bayanta. Yana shirin feshe wajen abun ta, Farida ta ce "tsaya-tsaya Saminu. Cire ma ta pant ɗin za su faɗo"

"Hajiya ki bari na fesa a wajen za su fi mutuwa da wuri"

Farida ta girgiza kai. Saminu ya cirewa Naomi pant ɗin wanda ke cike da cirnaku wasu sun mutu wasu kuma suna ta mutsu-mutsu a jiki. Cikin minti ɗaya kusan duk cirnakun sun mutu saboda ƙarfin maganin. Wanda su ka tsira ma to sun nakasa sosai.

Farida ta kalli Mrs Comfort ta ce "ki jawa 'yar ki kunne, duk abinda ta yiwa mijina ta warware idan ba haka ba. Nan gaba ba'a cirnaku kaɗai zan tsaya ba, sai ta ƙwammace ba ta zo duniya ba"

Ta cilla ma ta wani tube na magani ta ce " idan ta wanke jikinta da kyau ta shafa wannan. Zai taimaka wajen rage raɗaɗi"
Ta kalli su Saminu ta ce su kunce ta. Ana kunce bakin Naomi ta ɓarke da kuka, ihu ta ke kamar wadda aka aikota saboda azaba. Ana gama kunceta ta fita da gudu sai banɗaki, tana zuwa taga ba ruwa a ciki ta fito ta wuce kitchen da gudu tana sosa gabanta da bayanta zuwa kanta duk lokaci guda. Suna ji ta buɗe randan ruwa ta fara kwararawa kan ta tana yi tana kuka...

Farida ta kalli Mrs Comfort ta ce "ki jawa 'yar ki kunne ko kuma jikinta ya gaya ma ta" daga haka su ka fice a gidan.

Gaba ɗaya ruwan randar ta ƙarar a jikinta still ba ta ji sauƙin komai ba. Sai ihu ta ke yi, Mrs comfort ta ɗau waya ta kira Abel ƙanin Naomi akan maza-maza ya zo gida.
Naomi ta zama tamkar mahaukaciya a cikin gidan, ta shiga nan ta fita chan, ta kasa zama ta kasa kwanciya sai kuka da soshe-soshe...


Ƙarfe shida na yamma Naomi na kwance tsiraran ta tana hawaye tana nishi sama-sama, gefenta ƙawarta Maureen ne ke ma ta fifita a gabanta. Maganin da Farida ta bayar aka shafa ma ta, ya ɗan taimaka wajen samun sauƙin raɗaɗin da ta ke ji. Ilahirin jikinta duk ya cika da tabon cizo.

"Na God go Punish that woman" Maureen ta faɗa tana tsaki

Mrs Comfort da ke gefe tana ganin 'yartata ta ce "ba laifin Madam Farida ba ne. Laifin Naomi ne, mi ya kaita soyayya da musulmi hakan ma married man"

"Mama ki dena faɗin haka. Ko ma mi Naomi ta yi ba ta chanchanci wannan punishment ɗin ba. This is pure cruelty"

Mrs Comfort ta girgiza kai tana tunanin idan Naomi ba ta ji sauƙi ba za su wuce asibiti kawai...


.............................

Hankali kwance Farida ta koma gida, zuciyarta saƙayau, ko ba komai Naomi za ta yi jinyar kwana biyu.
Ƙarfe shida saura sai ga Anas da Najdah sun zo ma ta.
Anas dai haƙuri ya ba ta kan wannan magana tareda nuna ma ta suna tareda ita ɗari bisa ɗari.
"Akwai wani Malami da na yiwa magana ya ce zai tayamu da addu'a. Insha Allah za mu ga ƙarshen wannan al'amari"

Farida ta ce " Ya Anas na gode sosai Allah ya saka da alkhairi"

Najdah ta cire girman kai ta ce " Anty Farida, Big B yana son ki sosai, ba zai taɓa walaƙanta ki cikin hankalin sa ba, Please kar ki yi fushi da shi"

" Na gode Najdah, ku dai cigaba da tayamu da addu'a"

Najdah ta ce Insha Allah.


Sun ɗan jima kafin su ka tafi. Su na ma tunanin Najeeb zai dawo ya same su amma har su ka tafi bai dawo ba...

A ɓangaren Najeeb kuwa zuciyarsa tafarfasa ya ke lokacin da ya isa gidan su Naomi ya isketa kwance. Maureen ce ta kira shi ta sanar da shi komai.

Lokacin da Mrs Comfort ta ga Najeeb ya shigo gidan su hankalin sa a tashe ta fara tunanin kaman maganar Farida gaskiya ne. Idan ba haka ba Sir Najeeb ɗin da ta sani ɗan ƙwalisa mai ji da kan sa ba zai taɓa kallon Naomi ba balle ya damu da ita ko kuma ya so ta.

Tana gani ya ɗauki Naomi a hannun sa su ka fita tareda Maureen. Tana faɗin su tsaya amma ba wanda ya kulata cikin su...



Da su ka je asibiti gado aka ce ta kwanta sannan Likita ya duba ta daga sama har ƙasa. Da ya gama examining na ta ya nemi bahasin abinda ya faru har cirnaku su ka cize ta haka musamman a ta wajen abun ta. Maureen ta fara koro bayani akan ai wata Ogar Naomin ce ta sa ma ta cirnaku a jiki.

"Saboda me? Wannan ya kamata akai case ɗin nan gaban 'yan sanda" Likitan ya faɗa cikin faɗa.
Maureen ta ce yanzu ma daga asibitin police station za su wuce.

Magani ya rubuta mu su na sha da na shafawa sannan aka sallamesu bayan ya rubuta mu su report da za su kai police station.

Daga asibiti Najeeb ya ce Abdullahi ya kai su police station. Abdullahi dai mamaki ya cika shi dan bai gane wannan al'amari ba daga asibiti sai police station. Ya dai cika umurni ya wuce da su...

Ganin report ɗin da su ka kawo da kuma testimony da Naomi da Maureen su ka bayar ya sa aka haɗa su da police biyu dan su je su arresting wannan muguwar mata da aka kira da Madam Farida.
Cikin su Naomi ba wanda ya ambata cewa Madam Farida matar Najeeb ne. Shi kuma Najeeb yana zaune kaman wawa duk abinda Naomi ta faɗa to daidai ne...

Motar su na gaba motar police na baya har su ka isa gida. Abdullahi dai bai san mi ya ke faruwa ba.

Maureen sai kumfar baki ta ke tana faɗin "today she go know say our madness pass her own"
Naomi kam maƙalewa ta yi jikin Najeeb wanda ke ta ce ma ta sorry...


Bayan tafiyar su Anas, wanka Farida ta yi ta gabatar da sallar Isha. Tana ma kan sallayar tana addu'a Tasallah ta shigo ɗakin da gudu tana haki.

"Baaba Tasallah lafiya?" Farida ta faɗa ganin yadda ta tsorata.

"Folisawa a falo, Folisawa suna neman ki Hajiya"

"Police kuma"

Tasallah ta gyaɗa kai.

"To ki je ina zuwa"

Tasallah ta fita, still tana tsoro dan ganin Najeeb ne ya zo da su ya sa ta ƙara tsorata da lamarin.

Farida ta cire hijabin sallar ta ta je ta ɗauko ƙarami ta saka dama gown ɗin material ne a jikin ta.

Najeeb da su Naomi na zaune a falon su kuma police ɗin su na tsaye.
Ganin Naomi ya sa ta gane dalilin zuwan police.

"Suna na Sergeant Iliya. Mu na tambaya ko ke ce Madam Farida Salihu?"

Farida ta kalli Najeeb wanda ko wajen da ta ke tsaye bai kalla ba sannan ta kalli sergeant ɗin ta ce "eh ni ce"

"Madam you are under arrest"

Farida ta yi murmushi ta ce "mu je ko"

Tasallah da ke chan wajen dining ta fashe da kuka tana faɗin "Alhaji ka yi wani abu dan Allah. Za su tafi da ita"
Ko gizau Najeeb bai yi ba balle ya sa baki.

Maureen na faɗin "evil woman. You'll rot in jail for this"

Haka Farida ta bi bayan su suka fita. Tasallah na ihun matar gidan ne fa, mi ta yi?.
Ganin ba wannan ba ne zai fishsheta ya sa ta nufi ɗaki ta ɗau wayarta ta kira Mom...

Ganin gidan Najeeb ya ƙara haukata Naomi. Duk ciwon da ta ke ji sai ya zamana ta watsar da shi gefe, babban burinta shi ne yadda za ta mallaki wannan gida ita kaɗai...


...........................


Tun kan su isa police station ɗin Daddy ya fara kiraye-kirayen waya. Su na zuwa ma ba wani dogon bayani kawai sake Farida aka yi. Domin Comissioner of police ne ya kira ya ce a saketa.
Abinda ya ƙara sa Daddy ya tsorata da lamarin shine jin cewa Najeeb ne ya zo ya bada report sannan ya ce a arresting Farida. Gaskiya Najeeb yana buƙatar addu'a.
Farida kam har su ka iso gida ba ta ce ƙala ba. Mom ce ma ke ta aikin ba ta haƙuri.
Daddy ya ce wa Mom gobe Tasallah ta kwasowa Farida kayanta. Daga yanzu a nan za ta dinga kwana tunda abin ya kai ga haka kar su wayi gari Najeeb ya kashe Farida.

Farida sai da ta shiga tsohon ɗakin su sannan ta fashe da kuka. Tun ɗazu ma tanajin kukan, kawai ta daure ne saboda su Mom. Wai ita ce yau Najeeb da kan shi ya ke kawo ma ta police har gida.
Najeeb ɗin da lokacin da Sabreen ta sa aka kamata haka hankalin sa ya tashi ya zo police station yana masifa kaman zararre. Ta tuna first kiss ɗin su a ranan. Shi ne yau Najeeb ke gani ana tafiya da ita amma ko ajikin sa, kai duniya!...


..........................


Washegari kamar yadda Daddy ya ce haka Tasallah ta ɗebo wa Farida wa su daga cikin kayan ta. Daddy ya ce ta fita hanyar Najeeb kar ya illata ta tun da abin ya kai ga haka.

Addu'a aka ci gaba da yiwa Najeeb dan addu'ar ce kaɗai garesu. Tasallah ba ta fasa sawa Najeeb ruwan zamzam a abinci ba kaman yadda Farida ta buƙata...

A ɓangaren Naomi duk faɗa da wani masifa da Mrs Comfort ke yi ba wanda ya shigeta. Tun da su ka shiga ɗaki ita da Maureen su ka fara shirya yadda za su kawo ƙarshen Farida saboda ma kar a samu matsala a gaba...

Bayan kwana biyu


Maureen da Naomi su ka sake duƙufa gaban Boka Ifagbemi.
Lokacin da Naomi ta gama kwararo buƙatunta Boka ya kece da mahaukaciyar dariya. Sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login