Showing 51001 words to 54000 words out of 81703 words

Chapter 18 - NI NA RAINETA COMPLETE HAUSA NOVEL

FCWA   

20 Dec 2025

36

kaina gidansa, a ?ofa muka yi gware da Inno ta ja baya tana "ya Rasulullah! Ina zaki haka ne?"

"Gidan mai carbi, Inno yau zan koma da su Bahijja,bari na je na dawo", "zan raka ki" cewar Tasleem da take sanye da hijabi.

Malam Musa Mai Carbi shi ne sunansa,abokin mahaifina ne wanda na ji an ce tare suka yi yawon almajiranci, tsohon dattijo mai tsawon rai da ilimin addini, yana da sani ba kaWan ba, na ji an ce ba mutane kaWai ba har aljannu Allah Ya hore masa, a gulmar ?an garin wasu kan ce ya kan taSa tsafi don in ya yi magani har abada da ?udurar Ubangiji kai da wannan cuta sai ko a lahira in ana yi. Na tura gidan bakina Wauke da sallama, dattijuwar matarsa ta amsa tana mini ?uri can ta ce "ba dai Hadizar Malam ba?" Da fara'arta. Na yi murmushi ina wa kaina masauki bisa tabarma na ce "ita ce fa Inna"

"Lale sannu da zuwa" ta ce tana mi?ewa, ta ajiye mana kwanansha taf da ruwan randa mai sanyi. Muka ?ara gaisawa sannan ta ce "wajen Baban naki kika zo ko?"

"E, Inna, Allah Ya sa yana nan". "Yana ciki bari na miki sallama da shi" ta mi?e, babu jimawa kana ta fito ta ce "ku shiga"

Muna shiga da zama ya ce "sai yanzu kika zo Hadiza?, Na sha mafarki da mahaifinki yana nuna mini ke kina kuka, sai yanzu kika tuna da Uban naki, ko kema kin aminta ina tsubbu ne?" Ya ce.

Kuka na fashe da shi na ce "ko Waya Baba,babu nutsuwar tunani mai kyau ne, a gafarceni", ya yi murmushi ya ce "Hadiza in sha Allahu zan taimaka miki, ba na tsubbu Ni na yarda Al-Qur'ani warakar kowane ciwo ce, me ke tafe da ke?", Na share hawayena na shiga rattabo masa dukkan damuwata. Har na gama bai ce da ni uffan ba, na kai ?arshe sannan ya ce "Hadiza kina sallah,kina tazbihi amma kina sakaci da sadaka,kin ga sadaka maganin musiba ce, a ?alla duk ranar juma'a ki sadakar abinci ga mutum guda in ba hali, mijinki kuma yana sakaci da ibada dole duk ?ulumboton da za a yi ya kamasa,bai kuma tsare azkar ba, ya shagala da kasuwanci me zai sa duk abin jifa ya faWo kansa ba, kin ga azkar tamkar ?ofa yake,in har kana yi ko da an yo maka wata jifar wannan ?ofar za ta tare kafin ya kai ga jikinka, a yau in kin koma gidanki gabaWaya zannuwan gadon mai gidanki ki ?one su haka ki kyautar da duk wani takalminsa a siyi wani daga baya,wannan kina iya bari gobe. Zan ba ki ruwa ya yi alwala da shi,in sha Allahu da ya yi duk wani sihiri da yake jikinsa zai karye, ragowar ki yayyafa a duk wata kusurwa ta gidanki, zuma kuma ki haWa da tazargade da garin habbatussauda ya sha sau bakwai a kwana bakwai in sha Allahu zai samu waraka sosai", ban da hailala da godiya ga Ubangijina babu abin da nake har muka karSi kayan muka nufi gida, tasbihi kawai nake har muka koma gida, kayan Malam me suka samu jinkirin ?arasowa sai wajen huWu tukunna, haka na tasa su Bahijjan muka Wunguma tasha, ?arfe shida cikin gida ta yi mana, da ?warin gwiwata da karsashi na tura gidan, bakina da sallama na tura kofar sashen,idona ya sauka akan Mahaifin Inya na kwararo addu'ar neman tsari na ?ura musu ido ina kallon yadda suka yi WaiWai a parlorna ga ?ullika kala-kala, a firgice duk suka mi?e musamman Inya jikinta ya Wau rawa ta ce "Am..ma" na yi murmushi na taka har inda suke na ce "kun yi tunanin ba zan dawo ba ko?, Kun yi tunanin kun ci riba a kaina, kun yi ?arya ba zan taSa bar muku mijina ku yi yadda kuke so da shi ba, zan tsaya akansa sai ya gagari sharrinku kamar yadda na gagareku alfarmar Annabi da Qur'ani, na rantse da Allah me faci mara tsoron Allah in ba ka kwashe ?ullukan nan ka fitar min daga gida ba sai na ci mutuncinka" na dubi Bahijja na ce "je ki kira min buzu"

"Me ya yi zafi Hadiza, aure ne Allah Ya haWa ba yadda muka iya, sai dai mu yi ha?uri, Allah Ya baki ha?uri dama hanya ta biyo da ni na ce bari na le?o" ya ce yana mi?ewa

"Kwashe ?ulle-?ullenka ka tafi da su" na ce ina masa nuni. Ya saka hannu ya kwashe ya watsa a aljihu ya fita yana watsa hannu da surutan da ban san me yake cewa ba. Na dubi Inya na ce "ke kuma mu zuba mu gani,shege ka fasa!" Ta ja siririn tsaki ta murguWa baki ta wuce Waki. A matu?ar gajiye nake ga ?ishirwa, Waki na koma na watsa ruwa na yi alwala na zauna kan sallaya ina jiran kiran magariba, bayan magariba ban ko tsaya doguwar addu'a ba na sha ruwa da dabino, na fito, a corridor na tadda Inya tana turaren wuta, na nufi sashen Alhaji na ji sa a kulle,na dube ta na ce "bani makulli", ta yatsina fuska ta ce "ya ce kar a ba wa kowa"

"Ba ni makulli" na ce cikin dakewa, ta yi ?wafa ta nufi Waki ba jimawa ta dawo ta mi?o min, na harareta na buWe Wakin da addu'a,wani ?amshi yake fitarwa amma da sirki marar daWi wanda na rasa na meye, gyaran Wakin na shiga yi,gyara na ?urulla, kafin na gama kuwa na tsinci laya kusan uku har da banWaki, na girgiza kai kawai cike da takaici na yaye kaf zannuwan gadon Wakin har da wanda ke kai na fita da su haraba, Buzu ya taimaka ya watsa min fetur na cinna musu ashana, sai da suka yi ?urmus tukunna na hauro sama, na yi kiciSus da Inya a ?afar bene ta na kai da komowa hankalinta a bala'in tashe sai hura hanci take yi, na sakar mata murmushi na wuce Wakina, na Wau sabon zanin gado da garwashi da turaren wuta da habbatussauda na nufi Wakin, na shimfiWa zanin gadon na watsa habbatussauda da turaren wuta, nan da nan Wakin ya Wau haya?i. Na fitar da shi bayan na tabbatar ko ina ya samu rabonsa kana na tattara takalman Alhaji na fito,Inya da ke tsaye tana kai da komowa ta kalleni tana duban hannuna ta ce "ina kuma za ki kai masa takalma?"

"Gidan ubanki zan kai" na mata da?uwa na wuce, wallahi ni kaina wani fess nake jin raina,kamar ana wanken damuwata. Buzu na ba wa takalmin na ce ya rabar. Sai da na gama sannan na samu shiga kitchen na Wora jellop Win taliya mai daddawa wadda ta sha wadataccen busasshen kifi, a parlor muka zauna da yara muna kallo har ta gama, ina kitchen ina kwashewa na ji dirar motar Muntari, har na kwaso na dawo bai shigo ba, zuwa can ya shigo bakinsa Wauke da sallama, na yi tunanin zan iya manta komai, amma sam na kasa ina ganin Muntari na ji raina ya soma Saci, na shiga tariyo irin dukan da ya wa Tasleem kamar ba gudan jininsa ba. "Hadiza!" Na ji ya kira ni muryarsa da sanyi ?alau,ban kallesa ba na daure na ce "na'am"

"Ashe ?araye kika je, ba jimawa aka ce min an ganki a can"

"E" kawai na ce ina daure zuciyata. Har ya shige kuma sai ya dawo ya ce "akwai ragowar abincin ne, ina sha'awar daddawar",kamar na ce babu sai na ga rashin kyautuwar hakan, na mi?e na ce "bari a kawo", na zuba masa daidai cikinsa kana na dawo, Sai da na dawo Win ne na kula da shi,ya bala'in ramewa, ya yi ba?i, Muntari Wan ?walisa ya susuce har da barin suma. Na ajiye masa ina kallon yadda yake jan su Nadiya da hira amma sun yi tsuru-tsuru tsoronsa ma suke ji, ya Wauki plate Win ya dube ni ya ce "Hadiza ba na jin daWi, ki taya ni da addu'a" ya wuce. Hawaye suka Wigo min,wallahi kamar ba Muntari ba, duk ya lalace ya fita hayyacinsa,mutum mai fara'a da wasa da barkwanci,Wan gaye na ?arshe amma duk ya yi wani ga shi nan dai, da ka gansa ka san a zabure yake. Abincin ma kasa wani mai cin kirki na yi na nufi Waki, bayan yara sun kwanta na kunna Qur'ani ina sallah a Waki, Muntari ya turo ?ofar, bayan na idar sai na ga ya kwanta kan gadona ya rufe fuska da hannunsa kamar mai bacci, idan na ce tausayinsa bai tsirga min ba na yi ?arya,sai da hawaye suka kwaranyo min sannan na share na ce "bacci kake?"

Ya buWe idanunsa ya mi?e zaune ya ?ura min ido,har sai da na kauda kaina, ya ja ajiyar zuciya ya ce "Hadiza ina Tasleem?"

Na watsa mai mugun kallo na ce "wadda ka so halakawa?"

"Wallahi ban san me yake damuna ba, abu ?an?ani sai ya hassala Ni, sai da ga baya na ga wauta ta, don kuWi ai ba na kassara ?ata ba"

"Bare ma ba ta Waukar ma kuWi ba ko"

Bai ce komai ba,ya yi shiru ya jingina a gadon, na ce "matarka sabon injin na jiranka fa, Ni ma bacci nake ji zan kwanta", ya runtse ido tare da cije leSe ya ce "wai me ya sa ba ki da ha?uri da mantuwa ne?"

"Hmmm! Kai kuma da ?in gaskiya ba" na ce ina kauda kaina.

"Yaushe za ki karSi girkinki?" Ya jefo min tambaya.

"Ai ta yafe, ka manta ta ce ta yafe, Wazun nan ka gama ce min zumarta ya ?are, ka ce min ba mace ba ce shi ne yanzu za ka ke tambayarta ranar da za ta amshi girki!" Inya ta banko min Waki a zafafe. Raina in ya yi dubu ya bala'in Saci na mi?e daga zaunen da nake na ce "wa ya baki izinin shigo min Waki"

"Malama ba wajenki na zo ba" ta ce cike da fitsarar da ba ta taSa min irinta ba, yadda na kula ranta a bala'in Sace yake, na san kuma hakan na da nasaba da lalata aikinta da na yi.

Na yi murmushi na ce "to fitar min a Waki"

"Ba zan fita ba, ta so mu je", yarinyar raininta ya yi yawa hakan ya sa ni kuma na nufe ta na ce "fitar min a Waki,shi kuma a nan zai kwana"

"Wallahi ba ki isa ba!" Ta ce tana ri?e ?ugu. Na saka hannu da niyyar hankaWata ta ri?e tana cewa "wallahi yadda kika je kika yo surkullenki ba zai kwana a Wakin nan ba" ta fashe da kuka.

"Fitar min Waga Waki kafin na miki mugun duka" na ce.

"Kashe ni Hadiza sai ki kwana da Muntari, amma na rantse da Allah ba za ki kwana da shi ba a daren yau, sai dai mu kwana Waki Waya" ta ce tana shigowa Wakina ta zauna a ?asa. Yadda na ga ta kafe na san wani mummunan tashin hankalin ne,Ni kuma na ?uduri a raina ba zan bar Muntari ya kwana da ita ba a yau. (Tasleem ta ce : kin san Allah Fatima haka suka kwana a Wakin nan su uku, Amma ta kafe, Inya ta kafe har asuba idon kowaccensu biyu)


*Wadda ta karanta ba ta biya ba ban yafe ba, masu ?aryar sun biya suna turawa ba sa paid grp Wina ban yafe ba*




_Ina mata y'an kwalisa ma'abuta gyaran jiki macce Mai gyara daban take ga zuciya mijinta muna da kayan mata da supplement na gyaran jiki kala muna hadin amare da uwargida Dana masu jego muna da set Mai hade da kaza Mai kwai 3 da cicicibe da kifi da galam 3 na tsime da Burkett din gumba 2 da garuruka da zuma wanna set na maccen da ta isa ne muna hadin shi 20k akwai karami set na 15k akwai na 10k akwai na 5k_

_Muna da zuma Bata gindin kishiya ga wadda kishiya ke muzguna mata wanna Zuma In kinyi anfani da ita miji salab zaiji Daya shiyasa indai ba macce cikin matsala take ba bamu Bata ita_


_Muna da magunguna masu jawo hankali maigida da kara martaba dasa alhere ga maruwacin namiji_


_Akwai Zuma kiba da hip sati Daya Kinga result_

_Muna hadin kiba duk ramar ki duk bushewa ki kinka sha shi sai ke ciciko_


_Fanin supplement ma ba'a bar mmn mujaheed abaya ba tana da nagyaran fata da kara haske akwai na gyaran brst na gyaran hip na kiba
Kamar su Lady capsule 4500
Sugar wanita 3500
Glutathione 3500
Vitamin e 3k
Gluta white 3500
Royal jelly 3500
Apetamin 3k_
_Frozen collagen 3500
Da sauran su insha Allah duk Wani supplement Zaki same su ga mmn mujaheed y'ar mutan skwatawa
Ina wadda sanyi ke Hana ta jindadin gidan miji_
_Y'ar uwa kiyi bayani abaki dai2 da type dinki indai sanyi ki Hana Miki jindadin aure ku budewa GABA ku rashin niima to kedai yima mmn mujaheed bayani zata baki dai2 Dake mun tanade set din maganin sanyi 4500 Wanda zai fatataki sanyi Kuna kashe ne_

_Mmn mujaheed y'ar mutan skwatawa muna zaune garin kebbi state
08066726866_

_Kayan mu iya kudinka iya shagalin kane_

*My book is 500 only via 1401611541,Fatima Lawal Sa'id,Access bank, DM 08167888934*

RAHUSA DATA AVAILABLE (MTN)

1GB-280
2GB-560
3GB-840
4GB-1120
5GB-1400
10GB-2800
(1401611541, Fatima Lawal Sa'id, Access bank. Call 08167888934) All network available.
2?? 6??

Duk yadda na yi da Inya ta fitar min Waki ta ?i, sai hawayen da ban san dalilinsu take ba, alwala na Wauro na zauna kar sallaya ina karatun Qur'ani Murya buWe,yayin da Muntari ya gyara kwanciyarsa ya bamu baya akan gadon, Inya ta zauna bisa kujera, a haka dai muka wayi gari, cikinmu Alhaji ne kawai ya rintsa, da asuba na tashesa na zuba mai ruwa a buta na wannan maganin,lokacin Inya ta fita da ta ji kiran sallah, yana yin alwala ya fito dafe da kansa, ya dube ni ya ce "Hadiza bari in yi sallah a gida,kaina sarawa yake yi"

"Da dai ka daure,ana idar wa sai ka juyo". Bai ce min komai ba ya fita, ina idar da asuba ya turo ?ofar Wakina,idonsa ya bala'in yin ja kamar ya sa kuka, gadona ya kwanta bai ce min komai ba,zuwa can na fara jiyo saukar numfashinsa haWe da huci,rage gudun Ac na yi sannan na fita kitchen, su Bahijja za su makaranta hakan ya sa na Wora doya don ba wuya ta yi, har na gama aikina da gyaran gida bai tashi ba, ina ?o?arin shiga Waki na ji uban ?amshin turaren wuta mai hawa kai ya turni?e gidan, kaina ya sara na ce "auzubillahi minna shaitaani rajim" na ce, na nufi hanyar Wakinta, idona ya sauka akan kaskon da ke gabanta da ?ullin turaren wuta a leda, na ?arasa na Wauki kaskon da ?ullin, da runannun idanunta alamun ta ci kuka ta gode Allah ta kalleni,na yi mata murmushi na ce "asiri lokaci garesa, na yi mamakin inda kika watsar da tarbiyyar da na baki" ba ta ce mini komai ba ta Wauke kanta har na fice. Alhaji sai wajen sha biyu ya tashi da salati, kallo guda zaka masa ka tabbata ya samu sassauci ba kaWan ba, ya yi min Wan murmushi ya ce "Hajiya Hadiza na kai haka ina bacci ba ki tashe Ni ba?"

"Ai na ga ba ka jin daWi ne, ga magani" na mi?a masa zumar da na haWa da duk abin da aka ce,ya karSa ya sha, ya yatsina fuska,ban ce komai ba har ya gama na wuce na mai da cokalin,parlor na zauna ina break fast ya fito,gefena ya zauna yana "ina nawa?"

Da mamaki na kallesa na Wauke kai na ce "dama Ni nake maka girki ne?"

Ya Sata fuska ya saka hannu a kwano na, muna cin abincin Inya ta fito ta ri?e ?ugu tana kallonmu da ganinta ta ?ulu iya ?uluwa,sai cika take tana batsewa. Na ja tsaki a raina na Wauke dubana, Alhaji ma kallo guda ya mata ya maida hankali kan abincinsa,sai da muka gama sannan na ce "ka ga ka cinye min abinci ban ?oshi ba" don Inya kawai na ce,na san Muntari in dai na da ne sai ya faWi wadda za ta Sata mata,ya kuwa ce "ranki ya daWe ai sai na shiga kitchen Win na miki wani,in bai yi ba ma na sake" na mi?e ina sakin Wan murmushi na ce na wuce ban ce komai ba, ya biyo bayana. Muntari sai ya zame min kamar jela, duk inda na jefa ?afata a ranar yana biye da Ni,kasuwar ma na yi juyin duniya ya ce ba zai je ba, ba daWin shishige min Win da yake nake ji ba,hasalima daure zuciyata kawai nake don haushinsa Win dai nake ji ban daina ba, ina daurewa ne don gani nake da ya koma gun Inya za ta kuma juya kansa,burina yanzu ya samu lafiya gabaWaya na tabbatar ya wuce tsafinsu sai na Wau matakin da na ?udurcewa yi a zuciyata. Sai bayan la'asar Muntari ya fita bayan mun yi azkar Win maraice tare, fitarsa da wuya na samu ba?uncin Hajiya Kubra, da murna na tarbeta a parlor, muka shiga gaisawa ta tambayi Tasleem, na ce "wallahi can na barota ?araye,na ga duk bala'in kanta yake ?arewa in an yo,gara ta zauna can kafin komi ya daidaita"

"Hakan yafi,Allah Ya kyauta, ga kayayyaki kuwa na jido muku har ita"

"Kayan me?" Na tambaya

"HaWaWdun kaya masu inganci na Maman Mujahid ?ar usulin garin sakkwatawa, na gwada na yaba,ke har na ci ribarsa ?awata,shi ya sa na ce ba za a bar ki a baya ba, Tasleem kuwa magungunan sanyi ne masu fatattakarsa kamar me, kin san yanzu gyaran mace shi ne martabarta,to tunda har muna ganin mun samu tsayayye tun yanzu ya kamata mu fara maganin sanyi, kar daga baya lokaci ya ?ure mana, kin ga ai an yi mai wuyar, kuma ba a haWa gudu da susar Wuwawu ba,muna na ni'ima muna na sanyi,gara mu fara da na sanyin tun wuri, kin ga kayan maman Mujahid su ake kira da maida tsohuwa yarinya,sosai suke dawo da martabar mace, da ta min dahuwar kaza in gaya miki sai da aka maimaita daren amarci" Kubra ta ce cikin dariya, na yi dariyar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login