Showing 72001 words to 75000 words out of 81703 words

Chapter 25 - NI NA RAINETA COMPLETE HAUSA NOVEL

FCWA   

20 Dec 2025

33

ranar wannan iskancin da butulcin ba, ban da tarin tashin hankali da wula?anci babu abin da ta ?aru da shi, a hankali ta shiga ware takaddar,zuciyarta ta wani irin harbawa ta kauda kanta hawaye na sauka a kuncinta, can ta saki Wan murmushi ta ce "Allah na ga ishara, na yi nadama,Allah ka sassauta min,ka tsayar min iya haka" sai kuma wasu hawaye ke Wigo mata,ba ta manta lokacin da ta cewa Amma ai Alhaji ya ce Nadiya ba ta shi ba ce,ta kusa sheganta ta,ga shi yau tana girbar abin da ta shuka, cikin jikinta bana Alhaji ba ne,wata sabuwar masifar bayan wadda take ciki. Jugum ta yi ta kasa wani ?wa??waran motsi, ba ta da gata a yanzu sai Allah, ban da ruWin shaiWan me ya aiketa,ta san Amma ita ce duk wata gata da rufin asirinta,tun da aka haifeta babu rana guda da mahaifinta ya siyo tsinke ya bata a matsayinsa na wanda ya yi silar zuwanta duniya ban da asiri, danginsa ma kuwa ba su ?areta da komai ba sai zancen tana gidan arzi?i ba ta tuna wa da su, ga shi yanzu ta yi sanadin taSarSarewar gatan nata ta dawo ba ta da kowa sai ita Waya, ta share hawaye, ta san idan har asirinta ya tonu game da wannan cikin dubunta ta cika, asirinta ya gama tonuwa. ?aki ta rarrafa ta koma,har aka kira isha'i tana safa da marwa kuma ba su dawo ba, tana cikin sallah tunanin maganin zubar da ciki ya zo mata,ba ta ko tsaya addu'a ba ta saka takalmi ta fice, Chemist ta nufa bayan layi ya zo kanta tana shiga ta ce "maganin zubar da ciki nake nema" tana rufe baki ya Wauko ya mi?a mata haWe da faWin kuWin da ?a'idar sha, wani farin ciki ya lulluSeta ta ba shi kuWinsa tare da karba ta wuce, a lokacin sai ta ji kashi sittin na damuwarta ya ragu, tana shiga Waki ta watsa ruwa ta kwanta ta janyo magani ta watsa sa over dossage ta ja bargo ta kwanta,tun tana ?irgen mintina har ta dawo awanni ba ta ji ko watsalniyar abin cikinta ba, sai zuwa can ya Wan motsa ga dukkan alamu gyara kwanciyarsa ya yi har ta ji shigowar su Alhaji kusan goma da rabi na dare,har sha biyu idonta ?uri tana dako,ta ji tsit ta kuma Sallo uku ta watsa amma shiru babu labari, ko da ya wayi safiya ta ganta rass hankalinta ya dugunzuma ya tashi. Burinta bai wuce ta rabu da wannan tsinannen cikin na jikinta ba, ?arfe goma na yi Alhaji na fita ta sa ?afa ta fice,ba ta yi wa ko ina tsinke ba sai sabon gari,wani keSantaccen layi ta shiga, ta taSa raka Siyama a lokacin da take da wani sabon ciki aka zubar da shi. Ta tura ?ofar shagon da ke ta warin asibiti, minti sama da uku tana hello kafin jibgegen Iyamurin ya fito bayansa biye da wata mata bahaushiya tana gyara zama. Ya Wan mata murmushi alamun sanayya ya ce "kai ne!"

"E! Ya aiki" ta ce tana satar kallon matar da ke ta yamutsa fuska. Sai da ya sallami waccan ta fita sannan ya ce "ina jin ka abokin Siyama"

Ta gyara zama hawaye sharr suka zubo mata ta ce "ciki za ka zubar min"

"Wata nawa ne?" Ya tambaya cikin gurSatacciyar Hausarsa.

"Shida da sati uku" ta ce tana goge fuska.

"Ya yi karfi ma, tashi mu je in gani" ta bi bayansa hawaye na Wigar mata ya ce "cire wando ka hau nan" ya mata nuni da wani gado ta yi yadda ya ce tana rintse idonta ban da hawaye babu abin da take yi, ba ta taSa nadamar zina irin yau ba, ya saka hannu ya wangale mata cinya,ta wani rintse ido tana tauna leSe lokacin da ta ji ya zurmu?a mata yatsu jikinta hawaye sharrr suka gangaro. Ya jima yana jujjuyawa kafin ya zare hannun yana cewa "wannan ciki ta yi ?arfi, yena kwance da kyau"

"Ni dai ka cire min shi don Allah"

"KuWinka dubu talatin na aiki" ya ce. Inya ta zuge jaka ta shiga ?irgawa.

"A'a ba zan yi maka aiki ba, sai ka zo da wani fa" ya ce.

Cikin hawaye ta juya ta ce "Chimo wa zan zo da shi Ni da nake ?araye, ?an uwana duka suna ?araye"

"Ka zo da ?awarka, dokanmu ne,kai da cikinka ya yi karfi in ka mutu a nan, ina zan yi da kai, ka zo da wani sai a yi" duk yadda ta yi da Chimo ya ?i yarda dole ta fito, ba ta san kuma wa za ta nemo ba, wannan ta sanar wa wani ai tamkar ta yi kururuwa ta daSa wa cikinta wu?a ne. Siyama ta faWo mata a rai ta yi saurin cewa "auzubillahi" Siyama da ta tozarta ta so kashe mata aure,yanzu in ta nufeta da wannan zancen ai wasu kuWin za ta nema a wajenta ko ta tona mata asiri. Tamkar wata mahaukaciya ta koma tana tafe tana sa?e-sa?e lokaci-lokaci tana sharar hawaye, a yanzu kuma Waya ne take da wani hope a kai, ta je ?araye ta taho da wata Gwaggonta tun kafin asirinta ya gama tonuwa ta shiga ukunta, da wannan ta nufi gida a gobe za ta tafi ?araye ko Alhaji bai bari ba. Ko da ta isa gida tana tura gate ?irjinta ya wani irin bugawa sakamakon motar Alhaji da ta gani wadda ya fita da ita, har ta tura kai cikin gidan ?irjinta wani irin duka yake. Tana tura ?ofa idonsu ya sar?e a na juna ta wani irin razana ta dafe ?irji, take annurin da ke fuskarsa ya gushe ya haWe girar sama da ta ?asa ya daka mata tsawa ya ce "daga gidan uban wa kike" daga bakin ?ofar ta lafe jikinta na rawa.

"Kai kuwa ba ka ga juna biyu ne a jikinta ba, ka daina katsa mata irin wannan tsawar ai sai ta razana"

"Ba za ki gane ba wannan ba ?aramar muguwa ba ce ba, hawayen da take na makirci ne,ke Ni wallahi na gaji,sau kusan uku ina kamata ta fita ba da izinina ba, wa ya san ina take zuwa" ya dube ni ya haWe rai ya ce "in kika kuma fita ba izinina a bakin aurenki"

Wani wawar zubewa na yi a bakin ?ofa ina kallonsa kukan ma ya ?i zuwa,don tashin hankali da nake ciki ya wuce kuka,zaSi biyu ke gare ni ko tonon asirina ko mutuwar aurena da nake ta lallaSawa kar ya tsinke...


*Wadda ta karanta min ba ta biya ba,akwai ha??ina a kanta,ban yafe ba*


Ayiri yiri =؃?=؃?=؃?=؃?=؃?kuna Ina Mata Mata fa nake nufi bamuna mataba=??=??A& Z COLLECTION takawomuku ingantatun supplement =?G?=?G?=?G?=?G?
Muna da supplement na Infection
Muna da supplement na gyaran jiki Wanda zaisa jikin ki yayi kyau fata tai laushi da sheki >?p?>?p?
Muna dana gyaran breast succiko su tashi tsaf gwanin Sha awa >?p?>?p?
Muna da namatsi dazai matsaki ciki dawaje bawai ki matsi iya farkoba kuma yasaukarmiki da ni ima
Muna da na gyaran gashi Wanda zai fitomiki dagashi
Dawanda zaki haske sosai haske me kyau ba,irin na bleaching ba=??=??

A&Z COLLECTION dealer ce kayanmu suna da sauki sosai price dinmu price din sari ne zaki samu kayanmu cikin sauki alhmdulillah=؃?=؃?=؃?=؃?=؃?
Ga kadan daga ciki

1 Royal jelly karami 2500 me 60 pcs babba 16k me 365pcs
2 surga wanita 2500
3 vitamin e 2000
4 Amirna pills 7500
5 gluta white 2000
6 collogen + glutathione 2000
7 whiting gummies 2200
8 khusus 3500
9 juliet Eve 8500
10 vitamin c 2200,2500

Waddannan sune kadan daga cikin price din kayanmu nasan kodaga nan zaku gane A&Z COLLECTION gidan sauki ne =؃?=؃?=؃?=؃?=؃?=؃?

Muna garin Kano Dan neman Karin bayani Kira
ko whaspp 09037870422

Karku manta muna tura Kaya duk garin dakike inkinyi siyayyama dayawa muyi Miki free delivery =؃?=؃?yan garin Kano kayanku har kofar gida >??

*My book is 500 only via 1401611541,Fatima Lawal Sa'id,Access bank, DM 08167888934*

RAHUSA DATA AVAILABLE (MTN)

1GB-280
2GB-560
3GB-840
4GB-1120
5GB-1400
10GB-2800
(1401611541, Fatima Lawal Sa'id, Access bank. Call 08167888934) All network available.

3?? 3??

Wani wawar zubewa ta yi a bakin ?ofa tana kallonsa kukan ma ya ?i zuwa,don tashin hankali da take ciki ya wuce kuka,zaSi biyu ke gare ta ko tonon asirinta ko mutuwar aurenta da take ta lallaSawa kar ya tsinke.

Tana kallon Amma tsam ta mi?e ta bar wajen ba tare da ta ce komai ba. Alhaji ma ya mi?e ya wuce ta gabanta yana doka tsaki,ta san ya tsaneta don ba ya ko iya Soyewa yadda idanunsa kan nuna kamar duk duniya babu wacce ya tsana sama da ita, ta sha karanta hakan a idonsa. Ba ta da wani ?arfi ko kuzari haka ta lallaSa ta shiga Waki ta kwanta bisa gado tana sha?ar iskar da take jin ta gidanma dukka ta mata kaWan bare Wakin.

Har ?arfe uku idonta biyu,duk yadda take son ta kare igiyar aurenta ba ta da halin hakan don ko bata tafi ba,cikin jikinta sai ya fallasa ta an mata korar da kare ma ba zai ci ba,zaSin da yafi kwanta mata shi ne ta tattare komai nata ta yi gaba tun kafin komai ya ?ara jagule mata. Da wannan tunanin bacci Sarawo ya samu nasarar kwasheta.


Washegari misalin sha biyu ta gama tattara komai nata, hawaye na ta bin kuncinta, doguwar hijab ta saka har ?asa,tana ji a jikinta lokaci ya yi da za ta nemi yafiyar Amma, yafiya ta gaske ba ?an kwanonin da take yi ba, kafin ta fice ta bar mata gidanta,tana da tabbacin da wuya ala?arsu ta koma ta da, amma za ta so ko yaya ne Amma ta Wan sassauto a kanta, ta yi nadamar ba?anta mata irin haka, duk halin da ta jefata ga shi ita ma tana WanWanan mafiyinshi. Bakinta Wauke da sallama ta tura ?ofar. Zaune ta tadda Amma kan gado tana yankan ?umba,ta Wago idanunta ta sauke a kanta.

Hawaye suka Wigo mata ta share sannan ta ce "Amma ina kwana, an tashi lafiya"

"Lafiya" ta amsa mata yadda ta yi tsammani. Hawaye suka zubo mata sharrr cikin dauriya ta ?arasa kusa da Amma ta ce "Amma zan tafi na zo miki sallama ne da ba ki ha?uri" sai a lokacin ta Wago ta kalleta. Ta kuma share hawaye ta ce "nadama ita ce ?an?anuwar abin da zan ce nake yi a halin yanzu, wallahi ban san me ya ja ni aikata haka ba, duk da na Wau zigar Siyama wadda ta zame mini annoba da nawa laifin da na makance wajen mallakar abin da yake kusan haramun a wajena, Amma duk duniya ban da kamarki,babu wanda ya soni sama da ke har da mahaifina kuwa,ina ji a jikina idan na tafi da ha??inki ba zan taSa albarka ba,rayuwata za ta lalace sama da haka domin ke uwa ce a wajena, na rantse da Allah ji nake da ina da ikon tariyo baya da na goge zuwa na computer school domin shi ne ya ja min haWuwa da wadda ta tarwatsa rayuwata, Amma duk duniyata ban da kamarki amma silarta na makance na yi duk abubuwan da na miki, ba zan ce ki yafe min domin laifina mai girma ne a wajenki, amma ina ro?onki kar ki tsaneni domin na ga ishara daki-daki a duk abin da na yi miki, wallahi Amma ban san me ya shige ni na dinga abubuwa irin haka ba"ta dakata tare da fashewa da wani irin kuka. Amma ba ta ce mata komai ba sai kallonta take yi da alamun rauni a idonta.

Ta runtse ido tana tabbatar wa da kanta ta Sarar da duk damarta, me ya kaita, me ya aiketa take ta nanatawa a zuciyarta, Amma da ke gatanta ta rasa inda za ta juye shararta sai akan wadda ta yi mata sitira ta kuma fashewa da wani kukan cikin haki take cewa "Amma na zaSi saki akan zama da Abba, ina fatan hakan zai sassauto da zuciyarki, don Allah ki yi ha?uri, Tasleem ta tsaneni ba ma za ta saurareni ba amma itama don Allah ta yafe min, zan yi nesa da ku, ina fatan hakan zai dawo da walwalarku" ta ce tana ?o?arin mi?ewa.

"Asma'u!" Amma ta kira ta cikin wani irin yanayi marar daWi da rashin karsashi. Jiki babu ?wari ta waiwayo tana sharar hawaye.

"Kar ki kashe aurenki!" Ta ce a ta?aice. Wani irin sanyi ta ji har cikin ranta kafin wani kuka ya taho mata, umarni kawai zuciyarta ke bata ta sanar da Amma halin da take ciki, ta sani ko ba ta magance mata ba, ba za ta taSa tona asirinta ba, Amma mutum ce da ba dai ka ji zancen wani a bakinta ba. Wani irin kuka ta fashe da shi tare da zube wa kan gwiwoyinta ta shiga rerawa kafin daga bisani ta Wago ta dubi Amma ta ce "Amma ciki ne da ni, ciki ne da ni, ya zan yi Amma, na sha magani ya ?i ya zube, ina tsoron ka da na je a zubar na mutu bayan ban ajiye komai wa lahirata ba, Amma ya zan yi?" Ta fashe da wani irin gigitaccen kuka. Hannun Amma ta ji a bayanta ta dafa kafaWarta,har ranta wani irin nutsuwa da sanyi ta ji suna saukar mata wanda uwa ce kawai ke iya kawo shi, Amma tabbas uwa ce a wajenta, ita ce dai ba ta cika ?a ta halak ba.

"Ba cikin Alhaji ba ne?" Amma ta tambaya

"Amma ba cikinsa ba ne, yanzu cikin yana wata shidda da sati uku, auren ai wata biyar ne" ta ce cikin kuka.

"Ba tun kafin ku yi aure ba kuka same shi" wannan koran da Wan Waci a harshenta.

"Bai sanni ba sai da muka yi aure, ba nashi ba ne" ta ?are tana haki.

Cikin wani irin yanayi Amma ta koma gado ta zauna, kallon Inya kawai take yi, zuwa can wasu siraran hawaye suka zubo mata ta ce "me ya sa kika yi haka Asma'u? Da me na rage ki da kika gurSata tarbiyyar da na baki mai tsafta"

Cikin haki da kuka Inya ta shiga girgiza kai tana cewa "Amma ban sani ba, duk ban sani ba, bani da amsa, amsa Waya gare ni ita ce *Kawa* Amma ban san ya zan yi, na je a zubar da cikin an ce sai na zo da wani, Amma na rasa ya zan yi, komai ba daWi, na yi danasani,na gaji!" Ta ?are tana kifawa kan kafet Win cikin matsanancin kuka.

Yadda Inya ke wannan kukan wani iri take ji, duk haushi da Sacin ran da yarinyar ta jefata ji take kamar ta rungumeta a ?irjinta, haushi wani abu ne da za ka iya hucewa, amma ?auna takan rayu ne har gaban abada,?auna irin ta Wa take wa Inya,duk da kashi mai yawa ya zagwanye ba za ta taSa mutuwa murus ba,SarSashinta take ji yana Wan kamawa riririii cikin zuciyarta, ta toshe kunnuwanta don kukan ya tuna mata a lokacin da ta Wauke ta ranar farko cikin fellen zani,tik ba ko riga ta rungumeta a ?irjinta ta ce "ba za ki taSa kukan rashin uwa ba, ni nan zan zame miki uwa, zan miki gata, zan so ki sama da yadda zan so kaina" wasu hawaye masu Wumi suka sauka kan kundukukinta cikin wani irin mugun rauni ta dubi Inya da ke kuka kamar ranta zai fita ta ce "me ya sa?, Don me za ki min haka, na soki sama da yadda na so wadda ta fito daga jikina, don me za ki min tukwicin gatan da na miki da wargaza tarbiyyar da na jima kusan shekara ashirin ina miki? Don me?!" Ta daka gigitacciyar tsawar da ta ?are da kufcewar hawaye. Cikin wani sabon kuka Inya ta rarrafo ta Wora kanta saman ?afafun Amma ta ce "in kika tsine min na tsinu,Ni da duniya mun shaida ke uwa ce a wajena, Ni ce dai da nake da ba?ar zuciya da hassada na ruWe akan ke uwata ce, ga shi na yi gini kan tubalin toka ya ruguje,Waya bayan Waya nake girbe dukkan abin da na shuka da hannuna, don Allah ki yafe min Amma ko na samu sassauci na san ha??inki ne ke ta bibiyata" ta ?are tana dafe saitin zuciyarta.

Amma ta saka hannu ta Wago ta ta ce "ya isa haka. Ki bar kukan na ce hakanan"

Inya ta mi?e da ?yar tana cewa "Amma bari na wuce ban so yamma ta yi min"

"Kar ki je ko ina" Amma ta ce

" Na gama auren nan, ki yi ha?uri zan kuma saSa umarninki karo na biyu"

"Ina zaki?" Amma ta tambaya.

"?araye!" Ta bata amsa.

"Duk duniya baki da in da za ki suturta wannan sirrin sama da nan,kar ki zubar da cikin nan, ya yi tsufan da in kika ce za ki zubar za ki iya halaka rayuwarki, bayan haramcin da Allah Ya yi akan hakan"

"Shege ne fa, ban san uban cikin ba, ban sani ba wallahi"

Amma ta runtse ido jin kalmar take kamar Wigar dalma a zuciyarta wai Inya ce da zina har ta rasa waye uban cikin duk tarbiyyar da ta bata. Ta haWiyi wani abu ta ce "kar ki zubar da shi, ki koma Wakinki ki zauna amma kar ki zubar da shi" ta ce tana kauda kanta daga duban Inya.

Jikinta a matu?ar sanyaye ta nufi Wakinta, daSas ta zauna kan gado hawaye na Wigar mata ta rafka uban tagumi.


HADIZA

Wani irin kuka nake yi cike da Wacin zuciya, tausayin Inya na ratsa ni,ta bala'in lalacewa duk ta rame, shekarunta ba su wuce ashirin da Waya zuwa da biyu ba amma in ka ganta sai ka rantse ta yi talatin saboda tashin hankali, ban taSa sanin abin da Inya ke aikatawa ba sai da na ganta da Alhaji, hankalina ya bala'in tashi wai a ce gabana duk ta watsar da tarbiyyar da na bata har da zina duk ban ankare ba, na yi tunanin Alhaji shi ya lalata ta ashe da gaske bai san ta mace ba yadda ya rin?a jadadda min, haba abin da bala'in Waure kai, na san Muntari mutum ne mai takatsantsan da gujewa abin da za a ce ya yi mara kyau, mutum ne mai tsananin dattako, amma Inya fa,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login