Showing 93001 words to 96000 words out of 121675 words
fita itada Walida data kira.
Suna fita aunty Hannatu tace, "Wlhy Jiddah kin more da abokiyar zama ba irin namuba da kullum fitina bata k'arewa, dan ALLAH kema ki kwantar da hankalinki Ku zauna lafiya, nasan kishi abune mai zafi, amma inka had'a da hak'uri sai ALLAH ya sauk'ak'a maka, ita kanta nasan tanajin zafi, amma take dannewa saboda tasan mutuncin kanta".
Kan Jiddah a k'asa tace, "Insha ALLAHU aunty zan kiyaye, kumani wlhy bana wanijin haushinta, dan tanada kirki".
Dariya sukayi, Aunty Zulai tace, "Zakijine Jiddah, har yanzu akwai saurankine, bakigama tantance abinda akema kishinbane ba, babu macen da zatace bata kishin mijinta ai".
Balu zatayi magana su Maimuna sukayi sallama, hakanne ya sakasu barin maganar, ruwane ta kawo musu sai zo6o data dafa d'azun da safe da Aliyu yace yanaso, saita had'a musu shi yanzu takawo musu, akan shid'in saita data masa wani kafin ya dawo.
Sallamar su Yaruwaiya ce ta karad'e gidan, Maimuna talek'a tana amsawa, suma cikin fara'a take musu sannu da zuwa, suma suna amsawa cikin mutuntawa da sakin fuska.
Sun shigo da tarkacen da aka k'arasa sayama Jiddah dakuma freight d'inta madaidaici ruwan toka.
Sannu sukayiyyi musu sannan sukai gaisuwa da Maimuna tafita domin nema musu d'an abinci mai sauk'i.
Zarah da bakinta baya iya shiru ta kalli Jiddah tana fad'in "yaya Jiddah mi akayi miki? Dan dagani kuka kikayi amma? Idonki duksun kumbura fa".
Rasa amsar da Jiddah zata bata tayi, kafin kuma wani ya bata amsa cikin manyan takuma d'auki kwalin maganin da Jiddah tasha na rage rad'ad'i da ciwon jiki tana dubawa, tad'ago zata kuma jeho wata tambayar Aunty Saudah ta dakatar da ita, "K akku ya isa haka da ALLAH, batajin dad'ine ko dole saikinji mike damun Nata?".
"Yi hak'uri aunty Saudah, nifa kawai dana ganta wani irine, sainake ganin ko wani abu wani yamata, kinsan mai kishiya, gakuma hardasu maganin ciwon jiki, yaya Jiddahr ce tacika sanyi, naga kuma kishiyar nan tata akwai shegen way..."
Kulli Yaruwaiya tayimata a baya, "Zarah ki iya bakinki, banason maganar banza fa, irinkune dangin dake had'a fitina a gidajan y'an uwanku idan sunada abokiyar zama, wlhy koda wasa karna sakejin wannan banzar maganar akan abokiyar zamanta".
Kai Zarah ta d'aga tana tura baki da shafa inda Yaruwaiya ta doketa, su aunty Saudah ma duk fad'a sukai Mata akan hakan da nuna Mata rashin k'yautawa.
Walida tace, "Wlhy matarnan tanama da kirki, wace macece za'aima kishiya a wannan zamanin ta iya dannewa ta kwar6i kishiyar da danginta kamar haka?".
"Wlhy gaskiyarki Walida, aike kinfi Zarah hankali".
"To maganar ta isa hakanan, a canja da wata kuma".
Daga nan suka saki maganar suka koma wata daban, sunayi suna bud'e kayan, wasu na gyagygyarasu inda ya dace. Hakanne yasaka Jiddah d'an sakin jikinta, amma tak'i yarda ta tashi ko nan da can.
Kusan awa d'aya saiga Maimuna da kular abinci babba da zata iya d'aukar abincin dazai wadatar dasu, duk sukai Mata sannu da godiya.
Murmushi kawai tayi, dan hankalinta yakwanta dasu, yanda suke girmamata, dukda yawanci duk san girmeta, Zarah ce kawai takula kamar bata sakin jiki da ita sosai, amma hakan bai dametaba dan k'aramar yarinya take kallonta, kuma baizama dole dama kowa ace kamasaba.
Bayan fitarta sukayi haramar sallah, yayinda akabar wasu a kicin suna k'arasa gyarawa.
Aunty Saudah ta kalli Jiddah tana fad'in "Wane d'aki kuke kwana Jiddah?"..
Da hannu ta nuna mata kamar zata nutse dan kunya.
"A to bara muyi amfani da wannan mu kenan, wancan yazama Na k'aninmu ai". 'cewar Aunty Nafisa'.
Dariya sukayi irinta shak'iyanci suka shige. Jiddah k'in tashi tayi saida taga sun shige, su Zarah kuma hankalinsu na a kicin sannan ta lalla6a d'ayan d'akin domin yin salla.
Bayan an idar da sallah Aliyu ya shigo gidan, saida yafara shiga sashen Maimunatu sannan, itace take sanar masa zuwan y'an uwan jiddahr.
Hakanne yasashi zuwa dansu gaisa, amma saiya iske falon shiru, sai maganganunsu da yake jiyowa a kicin da d'ayan d'akin, kamar zai koma da baya saikuma ya nufi d'ayan d'akin da Jiddah take, a nufinsa saiya kirata a waya dan zatonsa tana kicin ko d'ayan d'akin da yakejin firarsu.
Jiddah dake canja kaya duk zatonta Zarah ce ko walida, batareda ta juyoba tace, "Zarah zoki jamin zip d'inan sama".
Murmushi Aliyu dake tsaye yana kallonta yayi, yatako a hankali zuwa gareta................???
_Naga kuna Neman shiga rud'ani akan buk d'in da kuka gani jiya, wancan sunansa *WUTSIYAR RAK'UMI...* Na kud'ine da zamuyi Na k'ungiya, so dukmai buk'ata zai sayane, guda biyarne muka fitar, pages na jiya kuma d'and'anone??, ciwon Kai ya hanani yimuku typing jiya?????¡â_.
*ga mai buqatar littafan zafafa biyar dukansu ko wasu daga ciki sai ya biya 500 ga dukka litattafan,ko 200 ga littafi daya,ko 300 ga littafi biyu,ko 350 ga liitafi uku,ko 450 ga littafi hudu*
*za'a tura kudin ta wannan accnt number din*
Hafsat kabir umar
0225878823
GT bank
Saika tura shaidar biya ga wannan number
08030811300
Ga masu turo da katin waya kuma zaku tura katin MTN ta wannan number din
07067124863
Da zarar kin biya kai tsaye zaki tsinci kanki cikin gidan da zaki samu littafin da kika biya.
*Karki bari ayi babu ke*????????????
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu_*??????
[12/25/2019, 1:59 PM] ??Noorunnisa??: *_Typing??_*
*_??HASKE WRITER'S ASSO...._*
*_??MUTUM DA DUNIYARSA....!!??_*
_(ya dace ya gyara kansa)_
*_Bilyn Abdull ce????_*
*_[51?52]_*
............Duk yanda yaso daurewa karta fahimci shine yakasa, maimakon ya zuge mata zip ?in tamkar yanda ta bu?ata saiya ?ige da tura hannayensa cikin rigar ya zagayo dasu saman cikinta.
Ba?aramar firgita Jiddah tayiba, tanemi juyowa a razane yay azamar ?ora kansa saman kafa?arta yana fa?in, "Afuwa hajjaju nine ba Zarah ba".
Kasa motsin kirki Jiddah tayi, sai jikintane ke mazarin tsumar tsoro, muryarta na rawa tace, "Sannu da dawowa".
"Yauwa amarsun Aliy, yaya jikin dai?".
Shiru tai ta kasa amsawa, gaba ?aya tagama takura, gefen zuciyarta kam addu'a take ALLAH yasa kar cikinsu Walida wani ya shigo, ita abindama bata fayimtaba inasu Aunty Nafisa suke? Harya shigo nan....... Firgita tayi tana Saurin dafe hannunsa dake neman canja salon yawo a rigarta, cikin sar?ewar murya da matu?ar in ina tace,
"Su..su..s..u aunty Sau..dah sun.. zo fa".
Dariyar dake nemen kufce masa ya danne da ?yar, dama yayi mata hakane dan tayi magana. Fuskarsa ?auke da shinfi?a??en murmushi ya cire hannunsa yana juyo da ita. Kasa kallonsa tayi, hannunsa yasaka ya ?ago ha?arta yana fa?in, "Tun randa na fara ganin wannan fuskar na fahimci matsoraciya ce ke kam".
Murmushin da bata shirya yibane ya kufce mata, tasaka hannayenta ta rufe fuskarta. Yanzun kam saida ya dara, ya jawota jikinsa yasaka mata zip ?in.
Komawa yay ya zauna a bakin gadon yana kallonta tana ta wani sinne kai, aransa kam dariyar yanda taketa kare ?irjinta yakeyi da fa?in mata kenan, hakafa Maimunatu taita masa, amma kwanaki naja tana kuma sakin jikinta dashi, yasan itama Jiddahn zata koma dai-dai ne, duk macen kirki dolene asameta da wannan kunyar, danshi baiga birgewaba ga ?ammatan yanzun da idanunsu ke a soye, watama ?an kukannan idan za'a kaita gidan miji batayi, ?agarama take atafi, suna ?aukar hakan wayewane basusan zubar da kimarsu suke ta ?iya maceba, koshi mijin sai dai ya?i fa?a maki amma saiyaji baki birgeshiba kwata-kwata, duk son wayayyar mace da wasu mazan keyi sunason koyaya ta?an ringa kunyarnan a gabansu, domin kunya ita kanta jan ajine ga ?iya mata, kuma alamune na kin kwankwa?i tarbiyyane a gidanku, danshi abinda yake kallon mace mara kunya *BALLAGAZACE* kawai mara isashshiyar tarbiyya. Numfashi ya?an sauke yana kallon jiddah dake tattare kayan data cire, amma koda wasa ta?i duban sashen da yake. "Juddatulkhair muje na gaida su auntyn namu naje na?an kwanta na huta kafin lokacin sallah ko".
Kanta ta jinjina masa tana ajiye kayan hannunta, cikin sanyinta tace, "To".
Harta kama hanyar fita yace, "Zonan na tambayekima".
Dawowa tayi da baya, zata dur?usa ?asa ya kamo hannunta yana fa?in, "Zauna anan". Ya nuna mata bakin gado kusa dashi.
Bata musaba ta zauna, kanta a ?asa tana wasa da yatsun hannunta.
"Kinsan mizan tambayeki?".
"A'a".
Murmushi yayi mai sauti yana kuma maida hankalinsa gareta, "Wai kinsan sunanama kuwa?".
A mugun bazata tambayar tasa tazo mata, dan haka ta ?ago kai tana kallonsa cikin waro idanu.
Babu shiri shima dariya ta kufce masa, mi?ewa yay tsaye yana cewa, "Dama sonake naga idonki kuma nagani, tashi muje ki rakani".
Jitai tamkar zata nutse dan kunya, wlhy rayuwar bawan ALLAHn nan tana matu?ar burgeta, tarigada ta taso Abbansu banda jaraba babu abinda ya iyayima Umma, idan sunga fira tsakanin mata da miji cikin aminci to sai dai idan gidan Uncle yahya sukaje, amma a gidansu dai a'a, itafa zatama iya lissafa dariyar Abba data gani a rayuwarta, wannan yasaka duk abinda Aliyu yay mata sai take ganinshi tamkar wani mijin novels ko film??.
Fita tafarayi falon ta barsa a ?akin, su aunty Hannatu na zaune sunacin abinci, yayinda su Balu ke ?aki suna salla sukuma.
Yanda taketa wani nu?u-nu?u da sissinkuyar dakai ne yasakasu zuba mata idanu.
"Lafiya kuwa Jiddodo?" 'Aunty Zulai tai maganar'.
Kuma ?asa tayi da kanta kafin tace, "Aunty wai dama shine zaku gaisa".
Harsun fara dariya saikuma kowacce ta rufe bakinta da hannu saboda harar da Aunty Saudah ta zuba musu dukda itama danne tata dariyar take, yanda Jiddah tayi maganarne dole tabaka dariya.
"Wlhy Jiddah yanda kikasan ?ar da haka kike, bakisan sunansa baneba?".
Murmushi tayi kanta a ?asa, "toni aunty bansan yanda zance muku ku ganeba".
Cikin tsokana Aunty Nafisa tace, "Sai kice auntys Hubbiy zaizo ku gaisa".
Ido jiddah ta zaro saikuma ta narke fuska, "kai Aunty Nafi wlhy nidai babu ruwana".
Yanzukam kasa daurewa sukayi, saida suka?an dara ka?an.
Yaruwaiya tace, "To ?an nawa yana ina?".
Da hannu jiddah ta nuna ?akin data fito.
"K jiddah wai kina nufin yana ciki?".
Kai ta ?agama aunty hannatu mai maganar.
Hannu sukasa suna dafe bakuna, Aunty Sauda tace, "Wai kina nufin dama tun ?azun yana nan?".
Cikin son tsokanarsu Jiddah tace, "eh mana".
Babu wanda bai rikiceba dukansu, Maman Sadiq ta zubama Jiddah da??uwa tana fa?in, "Jiddah kinci gidanku, shine dan iya shege kika barmu muketa zuba da sakin magana".
Dariya jiddah keyi, saikuma tarufe bakinta da hannu tace, "Wasafa nakeyi, wlhy yanzu yashigo kuna ?aki kuna sallah, su Zarah kuma suna kicin".
Babu wanda bai sauke ajiyar zuciyaba a cikinsu, yayinda aunty Nafisa ke fa?in, "ALLAH kafin nabar gidanan saikinci gidanku jiddah".
Nanma dariyar Jiddah tayi tanama aunty Nafisa gwalo.
Shiekh Aliyu dake ?aki duk yana jiyosu, murmushi yay yana mamakin dama tana magana haka, da sai yaga kamar tafishi shiru-shiru, amma yaukam dayaji bakinta saiya kuma tabbatar da kunyace kawai da rashin sabo dasu.
?akin ta shigo da sallama, ya ?ago idanu yana kallonta da amsa mata.
"Na fa?a musu zakaje ku gaisa".
"Wakikace musu zaizo?".
"Kai mana".
"Niwa?".
Shiru tayi dan an ?ureta kuma.
"Shiyyasa nace bakisan sunanaba ai madam, muje kirakani to".
Kafinma yakai ?arshen maganar harta kai ?ofa, dan batason yazo yacim mata.
Tunkan su fito dama sun kimtsa, Aliyu ya zauna saman kujerar farko idan kafito daga bedroom ?insu, fuskarsa shimfi?e da murmushi yana musu sannu da zuwa.
Duk suka amsa masa cikeda girmamawa, yau gasu ga babban malamin da sukeji a redio da tv a gabansu, matsayin mijin ?ar uwarsu.
Sun gaisa cikin mutunta juna, sunata kuma mamakin sau?in kai irinna Aliyu, har yana tsokanar yaron Aunty Hannatu wanda dashi ka?ai akazo dan ?aramine sosai.
Suma su Zarah sun fito suka gaisa dashi, yace, "Walida kece ?ar zaman ?aki ko?".
Dariya tayi tana fa?in "A'a malam, ai Umma bazata yardaba".
"Aini sainaje na ro?eta tabamu ke auta. Idan kuma auta batason nesa da Umma sai a bamu Zarah".
Dariys sukayi, Zarah na fa?in, "Ai sai arasa gane matar gidan da ?ar zaman ?akin".
Mi?ewa yay yana murmushin maganar Zarahn, ya?an saci kallon jiddah dake gefe kanta a ?asa ya fita abinsa.
Sosai suka shiga yaba masa dajin ?arin ?aunarsa a ransu, tareda kuma taya ?ar uwarsu murna.
Sai la'asar lis suka bar gidan, bayan sun kammala kimtsa komai, kayan gara kuwa sashen Maimunatu suka kaisu tareda kayan cin-cin daduk suka ?iba mata, itama Jiddah aka ajiye mata nata.
Har gate suka rakosu Jiddah na hawaye, duk sai tausayinta yakama Maimunatu, dan da gaske duk amarya saitaji wannan damuwar a farkon aurenta, kaitajin tamkar ka koma gidanku.
Itace taita lallashinta bayan tafiyarsu, harma jiddahn ta?an saki jikinta.
???????????
Abba baibi takan hajia hindu ba yagama shirinsa ya fice, yau koma yaran bai sauraraba, danshifa haushinma kowa yakeji, shika?ai yasan tanajin kalar rashin mutuncin daya shirya zuwa ya saukema Uncle yahya da Umma.
Koda ya fito gidan Alhaji garba ya nufa. Da ?yar Amarya tabarsa ya fito, shima danya mata bayanin cewar ku?i ?ila Abba ya kawo masa, har tsakar gida tamasa rakkiya, saima tasamu wajen zama tana jiran su gama taja abinta su koma. Hajia deluwa batasan hidimar da akeba, tanacan zaune jigum a falonta abin duniya yagama addabarta.
Fitowa abba yayi daga cikin mota yabama Alhaji garba hannu suka gaisa, koka?an fuskar Alhaji garba babu fara'a, sai wani ciccijewa yakeyi, shidai Abba ya danne tashi zuciyar dan masalaha yake nema yau.
"Alhaji idan ban takurakaba dan ALLAH magana nakeson muyi dakai".
"Magana kuma Alhaji Zakari, to aini babu sauran wata magana a tsakaninmu yanzu saita ku?ina".
"dukda haka dai ka daure ka saurareni, nasan zakayi farin ciki da hakan".
Umarni Alhaji Garba yabama direba yakawo musu kujeru, hakan da hajia amarya taganine yasata komawa sashenta takawo musu lemo, Abba dai sai kallonta yake da mamaki, dan yasha ganinta tazo shagon Alhaji garba, har mutane kansha dangantata da karuwarsa ce, to yanzu kuma mitakeyi a gidansa?. Bashida mai bashi amsa dan haka ya maida hankalinsa kan Alhaji garban.
Sabuwar gaisuwa suka sake kafin Abba ya ?ora dayima Alhaji garba bayanin abinda ya faru akan auren Jiddah, Alhaji garba dai baice uffanba. Ganin haka sai Abba yakuma gyara zamansa yana fa?in, "To ni yanzun nayanke wata shawarar danasan zatai maka da?i insha ALLAHU, tunda dai hakan ta kasance mizai hana nabaka ?anwar ita Jiddah ?in Zarah, itama yarinyace mai hankali, kuma tana kama da Jiddahn ma sosai wlhy".
Wani banzan kallo Alhaji garba ya zubama Abba, "Alhaji Zakari nakula dai kama maidani wani sha katafi kawai, to bara namaka gwari-gwari dai kawai, bana bu?atar auren kowace yarinya ma ni yanzun, dan na auro wadda take tsaremin komai dake sakani aure-aure, yanzu hakama dai zancen danake maka gobenan zakaga sammaci, dan nariga na shigar dakai kotu akan ku?ina. Naji tausayin ha?aka da Ashir ne kawai wlhy, dan ka?an daga aikinsa yasaka fitsari a tsaye, nabarka lafiya, saimun ha?u a kotu".
Gaba ?aya abba yagama ru?ewa, duk maganar da yakema Alhaji garba ya?i saurarensa, saima yun?urin shigewa sashen amaryarsa da yakeyi. Akuma dai-dai wanann lokacinne hajia deluwa ta fito saboda jin ?ar hayaniyar maganar da abba kema Alhaji garba.
Ai tanayin ido hu?u da Alhaji garba itama saitayi kansa da gudu.