Showing 99001 words to 102000 words out of 124686 words
na alkhairi a rayuwa. da wasu cututtukan ma da ku kan danganta su damu, alamomi ne na rashin lafiyar ruhi, duk da mafi yawa wasu lokutan mu ne muke haddasa rashin lafiya a ruhinku.
Idan ku ka ji alamu na ƙyashi ko hassada, ba ku fiye sakankankancewa ku roƙi Allah ya yaye muku ba, ko ku miƙe ku nemi maraba da hakan ba, ba ku fiye ɗaukarsa komai ba. Sai dai a hankali idan ya tsananta sai hankalinku ya gushe gangar jikinku ta aikata ɓarna. Kamar dai abubuwan da suka faru a masarautar su mijinki. Da abubuwan da aka yi masa. Ƙyashi, baƙin ciki hassada, son kai, da makamantansu duk larurar ruhi ce da ke kashe gangar jiki.
Sai dai a zamana da ke na ƙara fahimtar wani abu, babu abin da ya kai addu'a kusanta mutum da Ubangiji, kuma duk ruhin da yake da kusanci da Allah zaka same shi cikin nutsuwa. Babu wanda ya san inda ruhin ɗan Adam yake sai Allah, amma galibi cututtukan da suke alaƙa da ƙwaƙwalwa da abubuwan da zuciya ka iya rayawa su na da alaƙa da ruhi.
Lokuta da dama sai bawa ya yi ta addu'a, ya ga kamar bata karɓuwa, amma tasirin Addu'a da kusanci da Allah na sanya mutum a cikin nutsuwa, ta yadda zai ga wani da irin kaddararaa koma wadda ba ta kai tasa ba, amma ba shi da nutsuwa da kwanciyar hankali.
Yanzu mu tsaya a nan, ma ci gaba wani lokacin, zan je ɗebo wani magani ne"
Nana ba ta yi magana ba ta ji Muhsin yana kiran sunanta, yana kiran ruwa.
Ba ta motsa ba, ta ji Nene ta tashi ta nemo ruwan ta ba shi.
Abubuwan da suka tattauna da Ƙaisar kaf suka dawo kanta. Ya gaya mata wasu abubuwa da hannalinta bai taɓa kai wa kai ba. Tabbas ɗabi'ar zuciya ce jin ƙyashi ko hassada ko son kai wasu lokutan, hakan na nufin ruhin mutum babu lafiya kenan yana buƙatar attention?.
*****
Babu kowa a gidan, Mama ta ritsa Jamila, cikin matsananciyar damuwa da tashin hankali take tambayarta "Jamila ki gaya mini gaskiya, da gaske ne abubuwan da ki ke faɗa cewar kin shiga ƙungiyar asiri, ko kema aljanun ne suka taɓa ki ki ke wannan soki burutsun?"
Jamila ta sunkuyar da kai. Ta taƙarƙare ta dunƙule hannu ta ɗirka wa Jamila dundu ta ce "Za ki gaya mini ko sai na danne ki da fulo na kashe ki?"
"Ki daina duka na, ba soki burutsu nake yi ba, da gaske nake Hajiya Sa'a ta saka ni a ƙungiyar asiri ba tare da sanina ba. Ta ƙulla alaƙa da ni ne, saboda na kawo mata jinin Nana ta ba wa ƙungiyarsu ta yi arziki, da ban kawo jinin Nana ba ta saka ni a ƙungiya. A can aka fara lalata mini rayuwa, sannan tsautsayi ya sake shiga tsakanina da ɗanta Abba, cikin jikina da ya fita nasa ne. Shi ya sadaukar da kansa saboda kar da na bayar da kowa a ƙungiya, amma haryanzu aljanun ƙungiyar bibiyata suke yi, suna nema su kashe ni nima, wannan ce gaskiyar da ki ke son ji Mama, wannan ce bayan ita babu wata kuma"
Kafin Mama ta yi magana suka ji muryar Baba yana kuka ya ce "Jamila kin cuci kanki, ba ki kyautawa kanki ba, Jamila ƙungiyar asiri, kuma aka nemi jinin Nana"
"Wallahi Baba ban bayar da jinin kowa ba, ba dan son raina na shiga ba, ban san ya aka yi na shiga ba."
"Rufe mini baki, ni ta wani fannin na gode Allah da na yi wa Nanan aure ma, ta bar muku gidan. Kuma ki tattara yaranki ku bar mini gida Rabi, ko ƙaunar ganinki bana son yi. Ku je ku da Allah" Yayi maganar yana kuka. Mama ta rasa bakin magana, tabbas ita da din ga ƙara tunkuɗa Jamila jikin Hajiya Sa'a, ba tare da tunanin abin da ka iya faruwa ba.
Daga cikin ɗaki Jamila na kuka take faɗin "Dan Allah Baba kar ka yi mini baki, ka yi haƙuri ka yafe mini dan Allah, ko iya haka na sha wahala, ina kan sha ma na san ba tsawon rai zan yi ba, ba za su bar ni haka ba nima kashe ni za su yi"
"Gara su kashe ki, sai ya fi mini kwanciyar hankali" Ya goge hawayensa ya fice.
Yana fita ya ci karo da Ummi, ta kalle shi ta ce "Baba fita zaka yi, ina ta sauri saboda na cim maka, ina ta kiran wayarka amma ba ta shiga"
Ya ce "Eh, fita zan yi Allah ya sa dai lafiya?"
"Lafiya ƙalau, mu shiga daga ciki"
Ya girgiza kai ya ce "Ba na son sake shiga cikin gidan nan"
Ummi ta ce "Amma Baba meyasa, magana ce mai muhimmanci"
Ya ce "Ki yi ta a nan kawai"
Jiki a sanyaye ta ce "Ranar da 'yan uwan mijin Nana suka zo gurinka sun je gidana" Sai Baba ya gyara tsayuwarsa, ya ce "Yaya aka yi suka san gidanki?"
Ta ce "Nima ban sani ba, amma har magana na yi da mijin Nana, ka san lokacin da suka samu matsalar nan, da ba shi da lafiya sun zauna a unguwarmu"
"Haka ne, amma nifa ban yarda da abin da suka gaya mini ba"
Baba ya nuna wa Ummi guri suka zauna, ya ce "Ummi da gaske ke kin yadda?"
Ummi ta ce "Baba ga zahiri nan kana gani, tun daga Nijar suka taho fa. Sun gaya mini ma an so gyara maka gidan nan ka ce ba ka so"
Ya ce "Bar ni Ummi, ni yanzu na shiga hankalina da al'amuran rayuwa, babu abin da ya kai kwanciyar hankali da nutsuwa daɗi" Nan ya bata labarin halin da suke ciki da Jamila.
Jikin Ummi ya yi sanyi sosai da sosai, ta ce "Baba idan ka kori Jamila ina za ta je yanzu? Ƙaddara ce Allah ya aiko dole a yi haƙuri da ita. Yanzu dai sirukanka za su ranar Lahadi idan Allah ya kaimu, sun kira ni a waya, an ce ba a samun lambarka. Mijin Nana ya sai duk wani abu da za a tarbi 'yan uwansa da za su zo. Kawowa kawai za a yi kafin su iso. Dan Allah ka kwantar da hankalinka ka bar batun Jamila mutanen nan su zo lafiya su tafi lafiya.
*****
Asal na kwance a gadon Asibiti, Hasna na gefenta ta riƙe hannunta, sai uban kuka take yi.
"Hasna wallahi ina son Hammad, ji nake mutuwa zan yi idan ya sake ni, ga shi haryanzu ban san a wani bugiren ya ajiye ni ba, bai sake ni ba, bai ce mini komai ba. Babanmu ne duk ya janyo mini da zigar Imam Omar."
"Asal ki yi haƙuri mana, kar ki illata kanki a kan sa, shi fa yanzu ya samu wata ne da yake rawar ƙafa a kanta, ke sai ki kashe kanki fisabilillahi"
"Hasna ba ki san me nake ji ba, wai ni ce nake da kishiya, wadda na ɗauka ƙasƙantacciya mara galihu na shiga uku"
Hasna ta rungume ta, ta din ga rarrashinta tana yi mata nasiha.
Kwanan Yusuf huɗu da mutuwa, tsufan Alhaji Zailani ya sake fitowa, duk ya fita hayyacinsa ya yi wani iri. Alhaji Zailani ya zo duba shi, yana ta rarrashinsa yana ba shi haƙuri. Mutane jefi-jefi na shigowa su na yin gaisuwa.
Wani mutum ne ya yi sallama, suka amsa masa ya shiga, duk suka bi shi da kallo, dan babu wanda ya san shi a cikinsu.
AREWABOOKS
Sai da suka Shukura ta biyo bayan mutumin, sannan suka rikice gaba ɗaya suka miƙe, banda Alhaji Zailani. Hajiya Amina ta nufi Shukura da gudu har tana neman faɗuwa, ta rungume ta cikin tsananin tashin hankali da manakin ganinta ta ce "Shukura, ke ce? Ina ki ka shiga aka din ga neman ki, ina cikin jikin naki?" Wani irin tausayin Hajiya Amina ya shiga ran Shukura, ta rungume Hajiya Amina tana kuka.
Alhaji Fatuhu ma cikin matsanancin mamaki yake faɗin "Ikon Allah, Allah da girma da iko yake. Sannu Shukura" Alhaji Zailani dai yana zaune yana kallon su, bai ko motsa ba.
Idanun Shukura suka sauka a cikin nasa, ta ji tamkar ta yi tsalle ta shaƙe shi, saboda wani abu mai ɗaci da ya tsirga mata.
Mutanen da ya sabauta rayuwarsu, duk ga su a tare da shi a zaune.
Ta ce "Mummy wai na ga rumfa a harabar gidan nan, me yake faruwa ne?"
Hajiya Amina ta ce "Ba wani abu bane ba, Shukura ina ki ka tafi?" Kan ta ba wa Hajiya Amina amsa ta durƙusa ta gaida Alhaji Zailani ya amsa mata cikin damuwa ya ce "Shukura kin sanya mu a tashin hankali, meyafaru wannan bawan Allah kuma waye?"
Shukura ta numfasa ta ce "Garkuwa aka yi da ni, wannan mutumin Likita ne, shi ne wanda ya taimake ni, a gidansa na ƙarasa jinya"
Suka gaisa da mutumin, Alhaji Fatuhu ya din ga yi masa godiya. Hajiya Amina ta ce "Daddy, ba ka ga Shukura ba, Shukura ce fa ta dawo" Ya sauke numfashi ya ce "Na ganta"
Alhaji Fatuhu ya ce "Haba Zailani, amma atleast yakamata ka yi farincikin dawowarta ko, yarinyar da ake ta nema ba a gani ba, ta dawo kuma ka yi fuska"
Alhaji Zailani ya ce "Ni yanzu ta mutuwar ɗana nake yi, dan Allah ku ƙyale ni" A burkice Shukura ta ce "Wane ɗan nasa?"
Tsit suka yi aka rasa mai yi mata bayani, Alhaji Zailani da kansa ya gaya mata Yusuf ne ya mutu. Shukura ta gigice cikin matsanancin tashin hankali ta hau kuka, tana faɗin "Shi ma ka kashe shi ko? Da ni ba a kashe ni ba sai ka kashe mini ɗan uwa, wallahi ba zan yadda ba sai na tona maka asiri Duniya kowa ya san abin da ka ke yi" Likitan da ya rako ta, ya tashi tsam ya yi musu sallama, ya ce zai dawo.
Duk yadda suka so Shukura ta nutsu amma ta ƙi, ta din ga surutan da ba su gane kansu ba, kuma Alhaji Zailani ya yi mursisi ya yi shiru.
*****
Nana jikinta har wani sheƙi yake yi, ta yi kyau sosai da sosai, sai dai ganin Hammad ya yi mata wahala, saboda yana ta kai kawon shirin bikinsu. Yadda ta lura lamarin ba da wasa suka ɗauke shi ba, sai gayyatar mutane suke yi. Bangaren Sultan yana ta shan suka, da ƙorafe-ƙorafe, a kan ya ci mutuncin Al'adar da aka gada daga iyaye da kakanni. Bai tsaya a iya nan ba, ya ayyana rushe majalisar Imam da ake da ita. Ya sauke Tafawa, ya sauke Sardaunanda wasu daga cikin muƙarrabansa, tare da cewar za a ayyana waɗanda za su maye guraben su, a lokacin shagalin bikin Hammad da matarsa ta ɓoye da zai bayyana wa Duniya yanzu.
Nana a ranta take ƙara jinjina ikon Allah, sai dai tana ganin lamarin bikin nasu, kamar a ƙasar turawa, sun yi aure sun haihu har da ɗa, sannan za a yi shagalin bikinsu.
Gefe guda sannu a hankali take ƙara yi wa kanta fashin baƙin, bayanan da Ƙaisar ya yi mata a game da rashin lafiya da ya ce ruhin ɗan Adam yana yi. Kuma ga yadda ta fuskanta, babu wani magani tattare da hakan face ka yadda kana da ciwon, sannan ka tsananta addu'a Allah ya raba ka da shi.
Tabbas ko a kankin kanta ta ga misali, ta ƙara samun nutsuwa da yarda da komai lokaci ne, lokacin da take addu'a Allah ya kawo mata ɗauki a kan matsalolinta, gani take kamar ba za su wuce ba, kamar waraka ba za ta zo ba. Ashe wannan addu'a da take yi, ke ƙara samar mata da nutsuwa da kwanciyar hankali, tabbas banda haka, da irin azabar da ta ci da tuni ta amince da al'amarin bori, ko ma haukace saboda wahala da yadda ratuwarta ke tafiya kamar ba ta mutane ba.
Ta kalli yadda a yanzu ba ta aikin fari bata na baƙi, sai dai kawai a kawo mata ta ci, ta yi ibada ta kwanta. Sai dai ta dage da roƙon Allah, kar Ni'ima ta sanya ta shagala da neman kusancinta da shi.
****
Gidansu Nana, Mama ta yi mamaki, ganin Uwani ta zo ranar Asabar, wai zata kwana, da azahar ma sai ga Ummi da uban kayan cefane, har ma da Yaya Atine.
Mama ta ce "Wai lafiya duk na ganku, meke faruwa ne?"
Uwani ta ce "Kamar yaya meke faruwa? Karɓar kayan auren Nana muka zo ayi da mu mana"
Ta yi saroro ta ce "Nana kuma, wace Nanan?"
"Nana wacce da wacce ku ke da ita a gidan nan? Ba dangin mijinta ne za su zo daga Agadez ba?"
Mama ta ce "Ban fa gane ba, yaushe aka ganta"
Uwani ta ce "Ke Ummi, ba ku gaya mata ba ne?"
Ummi ta ce "Ina ga Baba bai gaya mata ba, Nana tana Agadez can hannun dangin mijinta, gobe in Allah ya kaimu za su zo kawo kayan aurenta"
"Shi ne kuma dan munafunci ba a gaya mini ba? Kuma wane irin kayan aure kuma bayan wanda aka yi"
Ummi ta ce "Wallahi nima ban sani ba, sai dai sun zo za mu ji"
Mamaki ya cika Mama, domin babu wanda ya tsaya ya yi mata cikakken bayani, kamar ma ba a son ta ji abin da yake faruwa.
Washegari tun ƙarfe sha ɗaya na safe, gidan abincin da aka sai Abinci a hannunsu, suka kawo abinci mai rai da lafiya cikin kuloli na alfarma. Baba ya din ga shiga yana fita, shi fatansa kawai ya ga Nana ba wai abin da za a kawo na auren ba.
Da azahar motoci biyu suka iso, ɗaya guda ɗaya ta alfarma ɗaya kuma ta matafiya.
Ƙaton carfet dama aka shimfiɗa a tsakar gidan, aka shirya wannan uban kayan Abincin.
Manyan mutane ne, farare sol Turaki da Matawallen Agadez, sai kum Tafida, sai kuma Imam Zahradeen, Mahmoudu Sulei, sai kuma Imrana.
Kai tsaye Imarana ya nufi Baba, aikuwa Baban ya rungume shi yana fashewa da kuka. Yadda ya ga Imarana a nutse cikin kamala kawai ya sanya shi mantawa da tarin baƙin cikin da yake ciki, kuma sai a lokacin ya gazgata mutanen nan da gaske suke.
Imrana ya ce "Baba kar ka yi magana, ka ga mu na tare da baƙi" Baba dai kai kawai ya iya jinjinawa yana sake riƙe shi, kamar zai sake guduwa.
Ta taga Mama take ɗan leƙowa, ta saki baki tana kallon ikon Allah, suturar jikin buzayen kawai ya fallasa cewar a cikin rufin asiri suke, ba ƙananan mutane ba ne.
Bayan Baba ya ɗan nutsu, duk sun nemi guri sun zauna, suka gaggaisa. Imam Zahradeen ya ce "To Baba mun sake dawowa, mun zo mu cika alƙawari da muka ɗauka, waɗanan 'yan uwan mahaifinmu ne, ga shi muka zo tare da su"
Suka sake gaisawa Matawalle ya ce "Ɗan uwa, Sultan ne ya aiko mu wakilci mussaman, mu zo mu yi godiya, mu jinjina wa namijin ƙoƙarin da ka yi, na aura wa ɗanmu 'yarka ba tare da sanin waye shi ba. Haƙiƙa mu yarinyarka alkhairi ga ahalinmu da ƙasar Agadez baki ɗaya ma. A madadin Sultan Jalaludeen ya ce "Mu ce maka mun gode, mun sake gode wa. Mu na tafe da dukiyar aurenta, kamar yadda ake yi wa kowace 'ya da ake yi wa kabilar buzaye. Sannan ya ce ita wannan 'ya yanzu ta zama tasa, yana kuma gayyatarka da duk wani wanda yake sha'awar zuwa, gagarumin shagalin bikin yaran nasa. Hammad da kuma Gimbiya Asma'u."
Baba ya numfasa yana ganin abin kamar a mafarki, ya ce "To ai tun da dai da aure a tsakaninsu, a ganina da an haƙura da bikin shagalin nan"
Turaki ya ce "To ai ɗan gidan mulki ne, abu ne aka yi shi da babu wanda ya sani, kuma ya saɓa wa al'adarmu, wands a dalilinta an soke al'adar ma gaba ɗaya, dan haka dole a yi shagalin bikin domin nuna wa Duniya ita. Saboda gudun abin da ka iya biyo baya, saboda mutum ne mai mulki mai faɗa a ji a garin Agadez. Dan haka nan da mako guda za a yi bikin, duk adadin waɗanda za su je, za a ɗauki nauyinsu tun daga ƙasa Nigeria har can, domin yin wannan shagali" Daga cikin ɗakin Uwani ta rafsa wata irin guɗa mai ɗan karen sauti tana faɗin "Alhamdillah" har sai da hankalinsu ya koma kan inda sautin guɗar ya fito. Gaddafi dai daga baya ya shigo, suka yi ido huɗu da Imrana. Imarana ya tashi ya nufe shi, rungume juna suka yi. Gaddafi ya ce "Imrana, wannan karon nisan kiwon naka har ya kai tsawon wannan lokacin?"
Imrana ya ce "Wani nisan kiwo, kame ni a kayi, a ka kai ni makarantar dole, abubuwa ne da yawa suka faru" Ai tuni suka manta da wani batun ba sa jituwa, saboda girman alaƙar jini, suka din ga murnar ganin junansu.
Daga nan aka shiga shigo da kayan auren Nana, sai da Baba ya saki baki, a ransa ya fara tunanin anya mutanen nan su na da hankali kuwa. Saboda shi yanzu al'amuran abin duniya tsoro suke ba shi.
Domin karrama abin da su Baba suke da shi, su Turaki suka ci abincin da aka kawo musu.
Aka gabatar musu da 'yan uwan Nana, Yaya Atine sai rawar kai take, tana nanata musu ita yayar Baban Nana ce uwa ɗaya uba ɗaya, ita ta saki Nono ya kama.
Haushi sai da ya kama Imran, Gaddafi ma ya tsuke fuska ya ce "Matar nan duk abin da aka haɗa da ita sai ta yi hauka"
Imrana ya ce "Har da wani ita ta saki nono ya kama, kamar nonon akuya, ko kunya ba ta ji ba, kamar ba da ita aka dinga muzguna wa Nana ba"
Ta din ga rawar ƙafa tana jan su da hira, sai da ta ba wa kowa haushi.
Da suka tashi tafiya kuwa, Haka Ummi ta shiga maƙwabta ta karɓo kayan da aka shirya, na tukuci da za su tafi da shi, dan kar ma wani ya sanya zalama. Kaji, da kayan snacks masu yawan gaske, da dabino kusan kwano biyar da tasoshin turare.
Turaki ya ce karramawar da aka yi musu ta isa, ba za su karɓi komai ba, ai Nana 'yar Sultan ce.
Gaddafi ya ce idan ba su karɓa ba, ba za su ji daɗi ba.
Baba ya ga za su tafi ya yi musu godiya sannan ya ce "To ba za a kawo mini Nanan ba, ita yaushe zan ganta?"
Imam Zahradeen ya ce "Zaka ganta Baba, sai kun zo