Showing 9001 words to 12000 words out of 121208 words
fushin da ta hau. Sannan muka yi sallama na kashe wayar bayan na tabbatar mata da zan fito aiki ranar Laraba.
Shiru na yi na ɗan lokaci sannan na furzar da iska a bakina, na ƙara lalubo wayar MD na danna masa kira. Sai dai har ta tsinke ba a ɗaga ba, ban gaji ba na sake danna wani kiran, ringing ɗaya biyu aka ɗauka.
"Assalamu alaikum" ita ce sallamar da na yi cikin karyayyar murya.
"Wace ce ke?" Tambayar da aka jefo mini kenan a fusace cikin ɗaga murya, ƙirjina ya buga babu shiri cikin sauri na katse kiran. Saboda muryar macen da na ji hakan ya tabbatar mini da matar shi ta ɗauki wayar. Jikina ya hau rawa musamman kiran da na ga ya shigo wayata ɗauke da sunan MD. Kamar kada na ɗauka, sai dai na yi jarumtar ɗagawa cikin ɗar-ɗar saboda tsoron abin da za ta faɗa mini.
"Me ya haɗa ki da mijina har kike kiran shi a waya?" Shiru na yi saboda ban san me zan ce da ita ba. "Wannan kiran ya zamo na ƙarshe tsakaninki da shi matuƙar kina da sauran son kanki. Domin a kan mijina wallahi babu abin da ba zan yi wa duk 'yar iskar da ta raɓe shi ba. Idan kuma kina ganin faɗa ce kawai nake yi, to ki sake kula shi ki ga yadda zan sa a nemo mini ke a duk inda kike cikin faɗin duniyar nan.." ƙitt ta datse kiran ta bar ni riƙe da waya a hannu na kasa motsin kirki tamkar wadda aka zare wa laka.
Cikin sanyin jiki da na gaɓɓai, na sauke wayar daga kunnena tare da sauke wata ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya. 'Gaba kura baya siyaƙi' zancen da na faɗa kenan cikin raina. Saran da na ji kaina ya yi ya sa na miƙe da nufin ɓoye wayar na ci abinci. Saboda masifaffiyar yunwar da nake ji, na yunƙura kenan saƙo ya shigo wayata. Da sauri na duba saƙon ƙirjina yana bugawa saboda fargaban kada a ce matar MD ce, sai dai na kasa ɗauke idona daga kan allon wayar saboda saƙon da nake ta maimaicin karatun shi a zuciyata.
'Ki yi haƙuri Zaituna. Na shiga wanka ne ban san kin kira ba. Me ke faruwa ne?'
Ajiye wayar kawai na yi saboda ban san me zan ce da shi ba a lokacin, domin kwanyata babu komai a cikinta kamar an goge mini komai. Fita ɗakin na yi na nufi kitchen, cike da tabbacin ganin abin da zan jefa wa cikina don na san Ummu Salma ta yi mana girki.
Shinkafa da wake na gani, cikin sauri na zuba na dawo falo na zauna ina ci ina tunanin kashedin da matar MD ta yi mini, wanda nake jin sautinta yana amsa-kuwa cikin kunnuwana tamkar a lokacin take magana. Ban san lokacin da na canye abincin ba saboda dogon nazarin da na lula.
A gurguje na gama sallah, saboda kiran da ake ta yi mini wani bayan wani ga wayata da ƙara. Zabura na yi cikin zafin nama na ɗauki wayar a daidai lokacin da wani kiran ya sake shigowa. Da hanzari na danna kore saboda ganin sunan MD ɓaro-ɓaro a jikin wayar, kuma zuciyata ta tabbatar mini da shi ne ba matar shi ba.
"Don Allah ki yi haƙuri, kada ki ga na takura ki. Me ya faru ne na ga kiranki..."
"Daman wayar da na gani ce a cikin ledar da ka ba ni. Shi ne na ce ko ka manta ne ka sako ta a ledar..." katse ni ya yi da faɗin,
"No! Taki ce ba mantuwa na yi ba. Kuma kada ki ɗauki ce wa na ba ki ita ne da wata manufa. Na ba ki ne a matsayin kyauta saboda ci gaban da kika kawo mana a cikin ma'aikatarmu. Muna alfahari da samun zaƙaƙurar ma'aikaciya irinki, fatan za ki karɓa hannu bibbiyu domin ki ji daɗin ƙara jajircewa a kan aikinki".
Girmansa da mutuncin shi ya sa na ce da shi na gode "Na gode sosai Sir. Allah ya ƙara rufa asiri" Muka yi sallama a mutumce, amma a raina na so ya karɓi wayar shi. Ko ba komai zan yi nesa da rashin mutuncin matar shi, duk da ba na zaton ta san da wayar balle zancenta...
"Da wa kike waya?" Ita ce tambayar da Mukhtar ya jefo mini ba tare da na ji motsin shigowar shi ba. Fuska na haɗe alamun babu sassauci ga duk abin da zan furta cikin bakina a lokacin.
"Ina ruwanka da wanda nake waya da shi. Ko kana da ikon duk wani motsin da zan yi sai ka san da zaman shi?" A fusace na yi maganar cikin ɗaga murya. Bai kula ni ba ya nufi wurin wayar da ke kan gado har lokacin, ya fiddo ta a leda yana jujjuya kwalin yana girgiza kai. Ban hana shi ba har ya gama tsugudidin shi ya ajiye tare da rugume a hannu a ƙirji ya ce,
"Wai me kike son mayar da kanki ne? A tunaninki Allah ba zai kama ki a kan cin amanar auren da kike yi ba...?"
"Kafin ya kama ni kai ne mutum na farko da haƙƙi zai rataye maka wuya ka mutu a wulaƙance. Yanzu kai har kana da bakin faɗar ana cin amanar aure? Kai nawa ka yi kafin ni na fara? Ko ka manta bala'in da kake yi na tuna maka yanzun nan? Ka san darajar aure kake shiga hurumin wasu matan auren? To bari ka ji abin da ba ka sani ba, a yau duk abin da na zama wallahi kai ne ka ɗora ni a kan hanyar na miƙe ɗoɗar. Saboda matan auren da ka yi rayuwa da su haƙƙinsu ne ke ƙoƙarin fita a saman kaina..."
Jikina yana rawa nake faɗar maganar saboda tsananin ɓacin ran da maganar shi ta saka ni. Kafin shi ma ya katse ni da faɗar,
"Babu inda aka ce wai don wani ya yi abu kai ma sai ka yi. Ki bar ni da haƙƙinki da kika ce na ɗauka, ke kuma ki sauke wanda yake kanki ki huta. Amma wayar nan ko ki mayar wa ɗan iskan da ya ba ki ita. Ko kuma na sanar wa Umma tun da ni kin raina ni ba kya jin maganata..."
A harzuƙe na ce "Duk inda za ka je ka faɗa ka je ka faɗa, amma wallahi ba zan mayar da wayar nan ba. Idan ka isa kai namiji ne ɗan halak, ka haɗa ni da takardar sakina uku yanzun nan ba sai anjima ba..."
"Allah ya ba ki haƙuri. Tun da ke ba ki da wani zance a rayuwarki sai na saki".
"Aurenka auren tsiya miye amfanin shi? Wallahi da irin wannan auren naka gara zawarcin mace dubu. Don kai ba mijin aure ba ne kuma ba ka kai namiji ba har yanzu..."
"Ya isa! Kada ki nemi faɗa mini babu daɗi. Waya dai ce ki je ga ki ga ta nan. Idan wadda ta isa da ke ta zo ai sai ku yi maganar tun da ni kin mayar da wani shashasha".
Daga haka ya fice fuu tamkar ya tashi sama, kallon banza na bi shi da shi sannan na yi tsaki. Wayar na mayar a leda sannan na ɓoye ta, don na san tsaf zai iya dawowa ya ɗauke ta ba tare da na sani ba. Zuciyata cike da alwashin ko Ummata ta ce na mayar da ita ba zan mayar ba balle shi.
Ku ci gaba da bi sannu a hankali za mu je inda warwarar ƙullin da ya wargaza zaman lafiyar auren Zaituna da Mukhtar 😅
D. AUTA CE ✍🏼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*LAMBA TA BAKWAI.*
Raina a ɓace na fito falo saboda sautin maganar shi da nake ji a sama, yana bayanin rikicin da muka yi da shi. Wanda nake da tabbacin waya ce yake yi kuma Ummata ce yake faɗa wa. Bakin ƙofar shi na nufa saboda baƙincikin makircin da na ji yana yi a cikin wayar, don bayan abin da ya haɗa mu har da ƙarin gishiri da mai, yana ta ƙoƙarin dole sai ya ɗora mini laifukan da ya saba ya wanke kan shi. Saboda komai na yi a wurin shi laifi ne shi kaɗai ne mai yin daidai.
"Wallahi Umma har yanzu suna tare, a kan shi yau babu abin da ba ta faɗa mini ba. Babban baƙincikina mutane har sun fara yamaɗiɗi da ita a cikin unguwar nan saboda tarayyar da take yi da shi..."
"Hakiƙa duk mai irin halinka a rayuwa ba ƙaramar asara ya yi ba wallahi. Ina takaicin zama wuri ɗaya da kai, ina da-na-sanin auren da na yi maka tsawon shekaru. Haka ma ina tausaya wa yarana da na yi zaɓen tumun dare wurin zaɓar musu uba kamar ka..." Abin da na faɗa kenan a bakin ƙofar ɗakin shi, cikin ɗaga murya bakina yana kumfa, domin ya tabbatar da na ji abin da yake faɗa.
"Ai kin saba faɗa ba tun yau ba, don haka yanzu ko kin maimaita ba abin mamaki ba ne..." Na katse shi cikin hanzari ina faɗin,
"Tir! Da rayuwarka Mukhtar! Ka ji haushi iya haushi a kan rayuwar azuzancin da kake yi. Idan burinka haɗa ni da mahaifiyata ne, to ka je ka ci gaba ga gani idan Allah zai bar ka..."
Ƙarar da wayata take yi cikin sautin kiɗan da na saka mai daɗi, hakan ya tabbatar mini da Umma ce take kira na. Ban bi ta kan wayar ba na ci gaba da aika masa baƙaƙen maganganu yana mayar mini da raddi cikin rainin hankali, domin duk na faɗa sai ya mayar mini ɗaga can cikin ɗakin shi.
Shigowar yara aguje bai sa na daina abin da nake yi ba, saboda na riga da na zo wuya. Kamar yadda har lokacin wayata take ta ɓurarin neman agaji. Kallo kawai yaran suka bi ni da shi bayan kowanensu ya sha jinin jikin shi, domin in da sabo sun saba gani amma sun kasa cire damuwar hakan a ransu. Saboda su na koma kan kujerar falo na zauna ina sauke numfashi, Haidar ya zo ya zauna kusa da ni yana riƙe mini hannu cikin nuna kulawa. Ummu Salma ta yi ɗaki da sauri ta ɗauko wayar ta kawo mini, Iman ta rakuɓe tana kallona tana sharar ƙwalla.
"Mukhtar ƙarya yake yi Umma, kuma ƙazafin da ya saba ne ya sake yi mini..." Na faɗa raina a ɓace ba tare da na jira cewarta ba.
"To me ya haɗa ki da mutumin har ya ba ki waya?"
Ajiyar zuciya na sauke sannan na ce "Waya ce aka rarraba a ma'aikatar kowa aka ba shi ba ni kaɗai aka bai wa ba. Shi ne fa daga ganin ta ya fara jifa ta da ƙazafin da ya saba, tun da ni babu ranar da zan yi abin kirki kullum sai ya kawo ƙara ta. Saboda ganin yake yi ya fi ni iya faɗar zance, da daɗin bakin ƙarya domin kawai ya sa ki ga laifina.."
Na katse maganar saboda kukan da ya zo mini. Umma ta yi shiru na ɗan lokaci sannan ta ce, "Daina kuka ba na son jin kukan nan raina ƙara ɓaci yake yi. Ki yi haƙuri zan fahimtar da shi domin ya daina tunanin da yake yi a ran shi..."
"Na gaji da zama da Mukhtar Umma, na kai matuƙar ƙololuwa a kan zaman nan da nake yi.." Ƙit! Ta kashe wayar, saboda abin da ta tsana kenan a ranta ta ji ire-iren waɗannan maganganun suna fita daga bakina.
Kuka na ci gaba da yi Haidar yana goge mini hawaye cikin fuskar tausayi. Ummu Salma da Iman suka shiga sharɓar kukan su ma, kafin Ummu Salma ta miƙe cikin ɓacin rai ta shige ɗakinsu.
Na kai kallona ga Iman cikin muryar kuka na ce "Tashi ki cire kayan Makarantarki. In dai wannan ƙaddararren uban naku ne, kuna da aiki idan kuka ce za ku dinga kuka a kan mugun halin shi. Kai ma ta shi ka je ku cire kayan ka fito ka yi shirin zuwa masallaci".
Suka miƙe tare da jan jakar islamiyarsu suka yi ɗakinsu. Na daɗe zaune a wurin ina karanta wasiƙar jakin da na saba, a kan wace hanya zan rabu da wannan baƙin zaman da nake yi. Sai dai duk hanyar da na zura kai cikinta sai na hango tarnaƙin da ke gabana idan na ce ita zan kama.
'Ni shi kenan a haka zan ƙare rayuwata da mijin da ba zai share mini hanyar shiga aljanna ba?'
Tambayar da na jefi kaina da ita kenan wadda ban da cikakkiyar amsarta, kiran sallar magrib ya sa na miƙe na yi ɗaki. Ina kan sallaya har aka yi isha, sannan na miƙe na fito falo na zauna, ɗauke da wayata ina chat su Ummu Salma suna kallo. Jiki na saki a cikinsu muka ci abinci tare na sha magani kamar ba ni da damuwar komai, domin Allah ya saka ni cikin mutanen da damuwa ba ta zauna mini a zuciya duk girmanta. Daga na yi masifata na gama shi kenan nake jin komai ya wuce a wurina, amma duk lokacin da ban samu damar furzar da abin da ke bakina ba, abin ya fi tsaya mini a zuciya har ya haifar mini da damuwa.
Mun ja lokaci a falon har suka yi bacci. Sai da na tayar da su suka shiga ɗakinsu, sannan na tofe su addu'o'i na rufe musu ƙofa na nufi ɗakina.
MD na hango online bayan na kwanta na sake buɗe datata, saboda Gb WhatsApp ne gare ni duk wanda ke online sai ya nuno mini yana nan. Haka kawai na tsinci murmushi a kan fuskata, domin har cikin raina na ji daɗin ganin shi ko da ba za mu yi magana ba. Na shiga duba status ɗin mutane idan na fita wannan na faɗa wancan har na isa ga na MD. Shiru na yi ina nazarin maganganun da na ga ya rubuta a status ɗin shi, domin kai-tsaye na alaƙanta rubutun da ni.
'Mu yi haƙuri da yanayinmu na yau idan bai yi daɗi ba. Domin komai wucewa yake yi kamar ba a yi ba. Babu abin da yake tabbatacce idan ba wanda Allah ya tsara ba! Ubangiji ya kawo mana farincikinmu a kusa da mu'.
Ajiyar zuciya na sauke, tare da goge ruwan hawayen da ya ziraro mini a gefen fuska. Saboda ina ji a raina kamar ya shiga zuciyata ya hango abin ke cikinta. Ina ji kamar ya haska wani madubin da ke hango masa hoton abin da ke damuna.
"Tabbas!"
Comment ɗin da na yi masa kenan a jikin status ɗin. Babu jimawa ya buɗe saƙon tare da fara typing a lokaci ɗaya. Kasaƙe na yi ina jiran ganin me zai ce, saboda sanyin da jikina ya yi a lokacin ɗaya bayan na fito daga akwatin sirrin shi.
'Barka da dare!'
"Barka dai sir!"
Maganar shi da amsata kenan bayan na ɗan ja lokaci kafin na buɗe saƙon, gudun ya gano zumuɗin da nake yi da ganin maganar shi.
"Ba ki yi bacci ba ashe?"
"I, yanzu dai zan shige"
Na ba shi amsa daidai da tambayar shi, kafin ya sake jefo mini wata tambayar na amsa masa.
"Ya jikinki?"
"Alhmadullilah! Na ji sauƙi sosai."
"Allah ya ƙara lafiya"
"Amin Ya Rahman!"
Shiru ya ratsa tsakanin maganganun. Har na bar akwatin sirrin shi na koma status ina kallo sai ga wani saƙon ya jefo mini, wanda na hango abin da ya ce tun a saman sanarwar da ake yi mini ta shigowar saƙon.
"Yaushe za ki koma aiki?"
Ɗan jim na yi kafin na ba shi amsa da cewa, "Laraba in Sha Allah!"
"Allah ya kai mu". Ita ce amsar da ya ba ni kafin ya sauka. A gaban idona ya sauka online ba tare da ya jira mun yi sallama ba, haka kawai na tsinci zuciyata da ɓacin rai, saboda rashin jin daɗin hakan a raina. Shiru kawai na yi ina tunanin me ya sa bai jira mun yi sallama ba, a ƙarshe ni ma kashe wayar na yi na gyara kwanciya. Da tunanin shi na kwana a raina, tare da guntayen mafarkan da na yi da shi a cikin baccina. Waɗanda ba zan iya kawo ya ya na yi su ba, amma dai tabbas na gan shi a cikin mafarkina kuma a yanayi mai daɗi.
Abu kamar wasa wunin ranar zungur MD yana maƙale a zuciyata, domin ko na so kawar da tunanin shi sai ya dawo mini sabo. Ta kai minti ɗaya biyu sai na buɗe data domin kawai na yi