Showing 39001 words to 42000 words out of 121208 words

Chapter 14 - ABOKIN AIKINA HAUSA NOVEL

24 Nov 2024

6399

Tsawon minti goma tana zaune har na kammala aikin na ture files ɗin gefena. Tagumi na yi da hannuna biyu muna kallon juna muna murmushi, sannan na cire farin gilashin da nake sanye da shi ina faɗin,
"Sannu cika-aiki. Wannan sammako haka ba kya bari a kira ki?"
"Gara dai na zo don zuwa da kai ya fi aike."

Dariya muka saka a tare sannan na jingina bayana jikin kujera ina ɗan juyawa a hankali. Murmushi ɗauke a kan fuskata na ce da ita, "A ina muka tsaya da labarin? Don na san kin fi ni sanin inda za mu tashi."
Zama ta gyara sannan ta ce, "Abu mai sauƙi cire wando ta kai, mun tsaya ne a daidai inda cikinki ya kai wata tara haihuwa yau ko gobe. A lokacin da Abban su Ummu ya yi miki laifin da ya so katse igiyoyin aurenku."
"Madallah da ke, don ni haddar kaina ta daɗe da gogewa."
Shiru na yi ina nazarin abubuwan da suka faru a lokacin, sannan na yi murmushin da iyakacin shi leɓe tare da sauke ajiyar zuciya na ɗora daga inda na tsaya.

_EDD na yana cika na ce da shi ya bari na koma wurin Ummata, saboda koyaushe zan iya haihuwa amma ya nuna ba zan je ba har sai na haifu. Domin ita kanta Ummar ta so a mayar da ni wurinta na haifu gabanta, amma babu kunya ya nuna ya fi so sai na haifu gidansa. Ba ta ja da tsauri ba ta bar maganar saboda ya fito ƙarara ya nuna ba ya so._
_Duk da girmama al'ada irin ta Sakkwatawa haka ta haƙura, domin abu ne wanda kowa ya sani haihuwar farko a gida yarinya take yi. Wani lokaci ma da wuri ake komawa a yi ta dakon zuwan haihuwar._

_Ranar da zan haifu, tun cikin dare na fara naƙuda, amma ban da bacci babu abin da yake yi. Sai idan na ji azaba ta yi mini yawa na ƙwala masa kira ya tashi yana jera mini sannu. Da ƙyar na ga asuba, zuwa lokacin na galabaita sosai ta yadda ko magana ba na iya yi. Ko da 'yan gidansu suka zo ban san lokacin da suka kai ni asibiti ba, saboda jinin da ya fara zubar mini ya sa na cire rai da duniya balle ganin abin da zan haifa._
_A gurguje aka karɓe ni cikin sauri aka yi labor room da ni, a saman gadon ɗaukar marasa lafiya jini yana ta bin jikina. Cikin ikon Allah har an fara zancen yi minti aiki sai ga yarinya ta kunno kai. Nan take na haifo 'yata ba tare da cikina ya sha askar likitoci ba._
_Bayan na samu kaina na ga an kimtsa ni tare da abin da na haifa. Ummata na fara gani sannan Inna Kulu da sauran 'yan gidansu Mukhtar, har da ƙawata Hafsa waton ɗiyar maƙocin Kawu Sale da muke kai ɗaya a nan Bafarawa Estate. Murmushi na bi kowa da shi cike da jin daɗin ganin kyautar da Allah ya ba ni. Mamaki fal raina tare da bin Mukhtar da kallo saboda ganin wasar bakin da yake yi, wanda alamu ya nuna fili ya yi farincikin da samun Bbyn. A raina na ce 'Ashe dai ana so ake kai wa kasuwa.'_
_Kwanana ɗaya Asibitin ana ƙara mini jini, saboda jinina ya yi zubar da dole sai an ƙara mini da wani. Da dare aka sallame ni muka yi tsinke sai gidan Kawu Sale, a nan ma mutane suka fara tururuwar zuwa gani na tsakanin 'yan'uwa da abokan arziƙi._
_Kwana huɗu da haihuwa 'yan gidansu Mukhtar suka kawo mana kayan fitar suna, kayan da suka janyo mana ce-ce-ku-cen mutane. Domin kala uku ce da kayan jarirai biyar sai wasu tarkacen da rashin su ya fi kawo su rana. saboda ba a kawo sauran kayan da Sakkwatawa suka mayar tamkar ibada ba. Domin babu kayan yajin da suka daɗe da camfi kansu, a kan duk maijegon da ba a ba ta su ba, ko lahira sai an biya ta su a gaban Allah. Surutun mutane ya sa Umma ta je kasuwa da kanta ta siyo tare da wasu kayan da ya dace a ce Mukhtar ne ya kawo su._
_Ana gobe suna mutanen Kebbi suka zo, farinciki fal raina saboda ganin babbar ƙawata Asma'u. Wadda muka yi karatu tare tun daga matakin primary har zuwa Sakandire, ko a Jami'a mun yi makaranta ɗaya sai dai kowa da ɓangaren da ya karanta. Akwai shaƙuwa sosai a tsakanina da ita, irin wadda kowa ya san ta zai san ni, haka ma wanda duk ya san ni ya san ta a baki ko a zahiri, saboda ƙarfin abotarmu._
_Ranar suna aka raɗa wa yarinya Ummu Salma, an sha hidima sosai komai a wadace ma Sha Allah, saboda ƙoƙarin Ummata da Baba Sale har ma da Baba Ali. Domin sun yi namijin ƙoƙari wurin fitar da ni kunyar 'yan biki, saboda ɓangaren abinci da abin sha Alhmdulillah har rara aka yi da dare. Domin girka abincin ake yi wani kan wani, sai da sawun mutane ya ɗauke aka dawo jinyar jiki._
_Da safe aka fara rabon tsokar abin sunan kusufa-kusufa lungu da saƙo. Saboda babu laifi Mukhtar ya yi abin kai gida, domin dabba biyu ya yanka amma sai da Umma ta dawo siyen ƙaramar tunkiya saboda mutanen kunyar da ba su samu ba._
_Yan Kebbi kuma suna gama sallar zuhur suka fara sallama da mutanen gida. Don daman can sun haɗa kayan tafiya tun da sake aka dakatar da su domin a ba su nasu kaso. Sai da suka soye namansu sannan suka yi haramar tafiya, har raina ban so tafiyar Asma'u ba. Na so a ce ta zauna amma ta nuna mini wannan tafiyar da da ƙyar aka bar ta, saboda Babansu mutum ne mai tsattsauran ra'ayi da masifar faɗa tamkar ya ci babu. Amma ni duk da faɗan shi Allah ya haɗa jinina da shi sosai yake mutunta abotarmu._

_Sai da suka isa gida sannan hankalina ya kwanta, domin lokaci bayan lokaci ina kiran su na ji sun isa ko suna kan hanya._

_Na ci gaba da zaman jego a gidan Kawu Sale har yi arba'in, sannan na tafi Kebbi cike da jin daɗin ganin Baba Ali da sauran 'yan'uwa da abokan arziƙin da aka yi zaman mutunci. Satina biyu a can na dawo saboda matsin lambar Umma da Kawu Sale suke yi mini, a kan na dawo haka nan na koma gidan mijina. Sai dai su abin ba su sani ba, koyaushe muna waya da shi, amma bai damu da sai na dawon ba. Bayan wata tambayar da ya yi mini wadda ta sa na kasa tantance ina zancen shi ya dosa. Domin a lokacin da muka gama waya da Umma a kan dawowar sai ga kiran shi, na dauka cike da tunanin shi ma zancen da zai yi mini kenan. Sai ga shi na ji sabanin abin da zuciyata ta zata._
"Telar nan taki da firij. Kina so a sayar miki da su kafin ki dawo?"
"Kada a sayar domin idan na dawo zan fara koyon ɗinki, kuma zan dinga yin zoɓo da ƙanƙarar zaƙi na san yaran unguwar za su saya."
"To" _Kawai ya ce sannan ya katse kiran, bayan mintina kaɗan ya sake kira yana yi mini gargaɗi a fakaice._
"Yawwa! Ki bar zancen nan a tsakaninmu ba sai kin faɗa wa kowa ba."
_Murmushi kawai na yi masa sannan na ce,_ "Wannan maganar ai ba ta kai na yi yamaɗiɗi da ita ba."
_Daga haka muka yi sallama tare da sanar da shi gobe zan koma Sokoto, sai dai ban ji ya yi murna ba balle ya yi zumuɗin dawowar ta yadda zan gane._

_Tun da safe na yi sallama da waɗanda ya zama dole, sannan Baba Ali ya sa aka kai ni tasha tare da kayan alherin da na samu niƙi-niƙi. Saboda mutanen Sokoto da Kebbi akwai ƙara kuma akwai girmama baƙunta._

_Sai dai abin da su Umma ta tarbe ni da shi ya kaɗar mini da 'yan hanjina, duk da ban bari na fito da firgicin a fili suka gani ba. Amma na shiga rashin natsuwar da ta janyo mini kiran Mukhtar babu shiri, saboda Inna Kulu ta sanar da ni,_
"Mun yi ta zuwa a gyara miki ɗakinki ba a iske Mukhtar gida. Kuma an sanar da Mahaifiyar shi ta karɓi makulli a hannun shi idan muka zo mu karɓa, nan ma duk muka je haka muke dawowa babu makullin. A ƙarshe ma cewa ta yi da mu ya yi tafiya, kuma bai bar musu makullin ba. Amma ya ba da haƙuri a kan ki koma gidansa shi ma zai dawo garin a ranar da kika dawo."

_Ajiyar zuciya na sauke sannan na ce ta bari na kira shi na ji yaushe zai dawo. Ni ma hakurin ya ba ni a lokacin da na kira shin, tare da saka mini ranar da zan koma domin shi ma a ranar zai dawo._
_Kasancewar rana ba ta ƙarya sai dai uwar ɗiya ta ji kunya, hakan ya sa na tattara kayana na koma gidansu Mukhtar. Tare da rakiyar su Inna Kulu da Hafsa, sai wata ƙawar Umma da wasu mata biyu daga cikin dangin su Ummata da ke Dunguza._
_Sai dai har tara na dare ta wuce goma ta doso Mukhtar bai dawo ba, dole suka tafi ba tare da sun kai ni ɗakina ba. Ni ma a nan ɗakin Mahaifiyar shi bacci ya kwashe ni, kasancewar Ummu Salma tana hannun matar Baban shi._
_Cikin bacci na ji muryar shi na yi firgigit na tashi, ya iso inda nake cike da mayalwacin farinciki a kan fuskar shi. Ni ma sosai na ji daɗin ganin shi har raina, ya saɓa Ummu Salma a kafaɗar shi muka yi ɓangarena. Makulli ya ba ni sannan ya miƙo mini ita ya ce; bari ya je ya kwaso mini kayana da muka baro ɗakin Mahaifiyar shi. Ban kawo komai a raina ba, kawai na buɗe na shiga da guntuwar sallamata, sai dai babu shiri na zaro ido tare da kwarma ihu iya ƙarfina ina faɗin,_
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun!"





Shin me ke faruwa ne😨 na yi nan ni ma🏃🏻‍♀️


Idan ban ga ruwan comments ba zan je hutun sati ɗaya😒



D. AUTA CE✍🏼


*ABOKIN AIKINA*


*@HADIZA D. AUTA*


*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*


*LAMBA SHA TARA.*

"Subhanallah! Me ya faru a lokacin? Me kika gani bayan kin shiga ɗakin?" Tamboyoyin da Amina ta jefo mini kenan a ruɗe, tare da firgici kwance a kan fuskarta. Murmushi na yi saboda ganin yadda hankalinta ya tashi, cikin sauri ta ce da ni,
"Don Allah ki sanar da ni me ya faru a lokacin? Na mats...

"Me dai yake shirin faruwa a yanzu!"

Maganar da muka ji kenan daga ni har Amina a bakin ƙofar ofis ɗina, cike da mamaki muka bi mata biyun da ke shigowa da kallon mamaki, waɗanda ke ƙoƙarin isowa inda muke cikin gadara. Kallon sama da ƙasa ɗaya ta fara yi mana sannan ta tsayar da kallonta a kaina, nuna ni ta yi da key ɗin da ke hannunta ta ce,
"Da alamu ke ce Munafukar da nake nema!"
"Ta ya za ki neme ni bayan ni ban san ki ba!" Maganar da na faɗa mata kenan cike da jin haushin rainin hankalin da take ƙoƙarin yi mini, har cikin ofishina. Bayan dakan luguden da zuciyata ta hau yi saboda tsabar kaɗuwar da na shiga"
Kallon uku kwabo ta yi mini sannan ta miƙa hannu ta baya wadda suka zo tare ta saka mata wani wallet a hannunta, sai da ta buɗe shi sannan ta wurgo mini a fusace saman ya daki ƙirjin ya yi ƙasa. Daga shi har kayan da ke cikin shi suka yi ɗaiɗaya, na yi hanzarin kai kallona a kayan da suka zuba daga wallet ɗin, cike da mamakin yadda aka yi ta yi ta same su. Kafin na duƙa na ɗauko Amina ta riga ni haɗa kansu ta ɗago, cike da zallar mamaki a kan fuskarta ta fara jujjuya kayan cikin wallet ɗin a hannunta tana faɗin,
"Wai ku bayin Allah me ya kawo ku ofinshin nan da rana tsaka haka? Sannan ina kuka haɗu da Id card ɗin ta, da passport har da ATM?"
"Za ki samu duka amsoshin tambayoyinki dalla-dalla, kuma zan yi miki gwari-gwari yanzu ba sai na ja zaren da tsawo ba. Amma kafin nan ke ki yi mata bayanin inda kika je kwatankwaci kika baro wallet ɗinki."

"Kwartanci kuma!?"

Maganar da muka haɗa baki kenan wurin faɗa ni da Amina cikin tashin hankali, babu zato na ji 'Karaf' sauti da dirar marin matar a kan fuskata. Kafin na yi wani yunƙurin ramawa ta ci kwalata a masifance tana faɗin,
"Sai na illata ki, ta yadda gobe ko da kuɗi aka ce ki sake zuwa gidana kwartanci ba za ki iya taka ƙafarki ki je ba."
Duka ta fara kai mini Amina tana riƙe hannunta cikin zafin nama, yayin da ni kuma na shiga ƙwatar kaina ta ƙarfi duk da fargaba ya hana ni kataɓus. Ƙawarta ta fara janye Amina tana faɗin,
"Ke dalla malama matsa daga gefe ba wurinki muka zo ba. Ci ubanta Fatima gobe ko kallon MD aka ce ta yi ba za ta sake ba, balle ta kai ƙafarta gidanku a matsayin ƙatuwar kwartuwar da ba ta ramin kanta sai na wasu."
Sunan MD da na ji ƙawarta ta faɗa na ji ƙirjina ya buga dam-dam! Amma a hakan bai hana ni jarumtar ƙwace riƙon da ta yi mini. Amina ta yi hanzarin shiga tsakaninmu tana tura ta baya, ita kuma sai ƙoƙarin kai mini bugu take yi ta gefen Amina.
Cikin ƙololuwar ɓacin rai na fara nuna ta da hannu ina huci na ce,
"Zan nuna miki na fi ki tashanci matuƙar kika sake taɓa ni da sunan du..."
Kafin na rufe bakina ta shammaci Amina ta kawo mini wani sabon duka, kukan kura na yi tare da ture Amina gefe. Cikin rufewar ido da na zuciya na yi cikinta da duka iya ƙarfina. Kokawa muka fara yi ni da ita Amina tana ƙoƙarin raba mu, ƙawarta kuma tana ƙara zuga ta da ihun faɗin ta ci ubana kada ta ƙyale ni.
Ta dake ni na dake ta muke yi a tsakiyar ofishin ba tare da ta yi nasarar kayar da ni ƙasa ba. Cikin sa'a na saka mata ƙafa ta faɗi na hau kanta ina ta jibga, ƙawarta ma tana kai mini duka tare da ƙoƙarin ture ni daga saman ruwan cikinta.
Ban san ya aka yi ba na tsinkayo muryar MD yana salati, amma hakan bai hana ni ci gaba da jibgar ta ba inda ta yi mini daɗi. Domin ko a shekaru zan iya girmar ta kaɗan ko mu zo tsara, duk da ta fi ni zama duma-duma amma hakan bai sa ta yi nasara kaina ba.
Amina ta janye ni daga samanta ina huci tare da ƙoƙarin ƙwacewa na koma, da nufin sake kai mata wani dukan domin na cire rainin da ke tsakaninmu. Saboda raina ya yi ƙololuwar ɓaci a kan abin da ta yi mini, haka idona ya rufe ba na ganin komai face na yagalgala ta iya son raina.

"Yanzu miye fa'idar wannan abin da kuka aikata? Tukunna ma ke me ya kawo ki wurin nan har cikin ofishinta?"
MD ya yi magana cikin sanyin murya mai ɗauke da tsananin ɓacin rai, na ƙwace daga riƙon da Amina ta yi mini na koma kujerata ina gyara zaman mayafina, wanda ya saɓule a jikina yayin damben ba tare da na sani ba.

"Ai dole ka ga laifina yanzu, bayan ka gama kai ta har gidana a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login