Showing 51001 words to 54000 words out of 121208 words

Chapter 18 - ABOKIN AIKINA HAUSA NOVEL

24 Nov 2024

6397

_Na jima ina karanta wasiƙar jaki kafin Mukhtar ya shigo da guntuwar sallamar shi, ban iya ɗaga kai na kalle shi ba balle na samu kuzarin amsa masa sallamar da ya yi. Zama ya yi kusa da ni ya miƙe ƙafa tare da janyo mu jikin shi, na yi hanzarin sakar masa Ummu Salma sannan na miƙe tamkar wadda aka tsikari. Jikina yana rawa tamkar mazari muryata tana harɗewa na ce da shi,_
"Ina ka kai mini kayana!? Ka yi gaggawar dabon fito mini da su yanzun nan, kamar yadda suka yi ɓatan dabo a cikin gidanka. Domin na tabbatar da ka san yadda aka yi suka salwanta, shi ya sa kake gwara kan mutane ka dinga zagaye-zagayen ƙarya!"
_Na ƙare maganar muryata a sama numfashina yana hawa da sauka saboda tsananin ɓacin ran da na shiga. Kansa ya duƙar ƙasa ba tare da ya ce da ni komai ba, mintuna a tsakani na fara jin sharɓen kukan shi. Mamaki fal raina na bi saman kan shi da kallo, domin idan ba kunnuwana ne suke ƙoƙarin yaudarata ba, to tabbas na ji sautin kukan shi. Lallaɓawa ya yi a hankali ya ajiye Ummu Salma, idona a kan shi har ya durƙusa a gabana gwiwa biyu, tare da haɗa hannuwansa wuri ɗaya yana sharɓar kukan da ya saka jikina yin sanyi. Kafin ya samu kuzarin yin magana cikin muryar kuka ya ce,_

"Ki yi haƙuri ki yafe mini, saboda na san na yi miki laifin da na cancanci duk wani hukunci daga gare ki. Amma don alfarmar Ubangiji da darajar Manzonmu Annabi Muhammad Sallallahu alaihi Wasallama ki yafe mini. Ta wannan hanya ce kaɗai idan kin yafe mini zan iya ba ki labarin dalilin da ya sa na sayar da kayan nan, wanda ko ke kika ji za ki iya ba ni da kanki ki ce na sayar domin daga ni har ke cigaban namu ne. Don haka don Allah ki yafe mini ba don halina ba, saboda matsin da na shiga wurin nemo mafita ya sa na sayar da kayan nan. Kuma na tabbatar da idan kika ji za ki amince da kanki ki ce na je na sayar domin mu rufa wa kanmu asiri."
_Jikina ya yi sanyi ƙalau! Saboda maganganun shi sun shiga jikina, kuma ratsa zuciyata sosai. Saboda idan akwai abin da ba na iya kaucewa a duniya, shi ne a haɗa ni da Allah a kan abu. Komai hawan da na yi sai na sauko saboda ba na kauce tayin alfarmar da duk aka haɗa ni da roƙon Allah. Sai dai kuma zama da shi ya fice mini a rai, duk da na ƙudurta yafe masa laifin kamar yadda ya roƙa. Tsayuwata na gyara, sannan na sauke hannuna ƙasa daga rungumar da na yi musu a ƙirji, tare da kawar da kaina gefe bayan na riƙe ƙugu na ce da shi,_

"Zan yafe maka kamar yadda ka roƙa, amma sai ka yi mini alƙawarin za ka yi abin da zan nema daga gare ka. Saboda zuciyata ba za ta taɓa yarda da kai a matsayin miji ba, ka sauwaƙe mini kawai cikin ruwan sanyi ba tare da kowa ya sani ba. Ni kuma na yi maka alƙawarin zan yafe maka duk kayan da ka salwanta mini. Don haka ka ba ni takardata yanzun nan gobe idan Allah ya kai mu lafiya na koma inda na fito. Kuma komai za a yi ba zan fasa wannan ƙwan ba balle wani ya ji warinsa, amma fa idan ka sallame ni cikin mutunci ba tare da wani ya ji ko ya sani ba. Domin Wallahi ba zan iya zama da miji irinka ba."
"Don Allah! Don girman Allah ki yafe mini Zaituna! Wallahi ba zan iya sakinki ba ko da za a ɗora mini wuƙa a wuya."
_Ya ƙare maganar tare da riƙo hannuna yana cisgar kuka tamkar zai shiɗe. Ƙwace hannuna na yi sannan na tura shi ya faɗi ta baya, saboda tsabar takaicin da ya ba ni. Amma hakan bai hana shi furta mini cewa,_

"Gara kawai ki yi mini duk abin da kike so a matsayin huce haushin laifin da na yi miki, idan ma dukana za ki yi na shirya karɓar hukuncin kowane irin duka daga gare ki, amma ba zan taɓa yafe wa kaina ba muddin na yi abin da kike so. Na fi so na mutu, ko kuma duniya ta Allah-wadai da ni, a kan abin da na yi miki da a ce na sake ki."





Uhumm! Maza mutanenmu😊




D. AUTA CE✍🏼

*ABOKIN AIKINA*


*@HADIZA D. AUTA*


*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*


*ASHIRIN DA UKU.*

_Kallon takaici nake aika masa ta gefen idona, hawaye yana zarya a kan dandamalin fuskata. Duk da maganganun shi sun saka zuciyata rauni, sannan kukan da yake sha tamkar wani ƙaramin yaro, ya saka ni jin lalle akwai babban dalilin da ya sa shi sayar mini da kaya dole. Tsayuwata na gyara tare da zuƙe majinar kuka na ce,_
"Me ka yi da kuɗin kayan? Sannan wace lalura ce ta janyo ka salwantar mini da kaya ba tare da sani na ko na Iyayena ba?"
_Miƙewa ya yi daga durƙushen da ya yi, ya iso inda nake ya riƙo hannuna. Ya zaunar da ni bakin gefen ƙwalluwar katifar da ta yi saura a cikin ɗakin, shi ma ya zauna tare da rungume ni jikin shi yana share mini hawayen da suka kasa tsayawa a kwarmin idona. Sannan ya goge na shi da gefen hannunsa, tare da kama hannuwana duka biyu ya riƙe gam-gam! Kamar wanda yake gudun na tsere masa._

"Na san ban kyauta ba saboda ban yi shawara da ke ba kafin na zartar da hukunci. Amma ki sani wallahi Allah ya sani ban da wata mafita ne shi ya sa na yi hakan."
_Ajiyar zuciya ya sauke mai ƙarfi sannan ya sake cewa,_ "Kamar yadda kika sani, wurin da nake aiki ba wani albashin kirki ake ba ni ba. Saboda matsayin ajiya nake yi a wurin har zuwa lokacin da zan ƙara karatu, domin a ba ni gurbi mai kyau da karatun da zan ƙaro idan na gama. Shugaban wurin namu ya uzzura mini a kan ko na ƙaro karatuna, ko kuma su canza ni da wani mai manyan takardu.
Dalilin da ya sa na shiga neman kuɗin registration kenan ido rufe, lungu da saƙo kusufa-kusufa a cikin faɗin garin nan ban samu ko dubu biyar ba. Har na gaji da gantalin neman bashi ga shi taimako ya yi ƙaranci ga mutane yanzu. Ga kuma karatun yana buƙatar kuɗi masu ɗan kaurin da zai wadata, kuma ana saura ƙiris a rufe sayar da foam ɗin a lokacin. Wannan dalilin ya sa na shiga damuwa tare da neman ta wace hanya zan samu kuɗin nan, saboda tsoron na rasa aikin kuma na zo mu rasa ya za mu yi ni da ke a cikin gidan nan. Tunanin sayar da firij da telarki ya zo mini, shi ne ya sa har na kira ki a lokacin na yi miki zancen. Duk da kin nuna kada na taɓa dole ta sa na sayar da su, sai dai abin haushin kuɗin ba su kai ko rabin na registration ɗin ba. Tunanin na haɗa da kayan gadonki ya faɗo mini, da nufin duk lokacin da na samu sarari na saya miki wasu idan buƙata ta biya.
Dalilin da ya sa na saka su kasuwa kenan domin mu samu abin da za mu rufa wa kanmu asiri. Shi ne na sayar da kayan na yi kuɗin registration, amma ki kwantar da hankalinki in sha Allah cikin kwanan nan zan saya miki wasu. Saboda ba zaune nake ba akwai buge-bugen da nake yi, idan Allah ya saka mana hannu komai zai wadata gare mu da yardar Allah."

_Shiru ya ratsa tsakani bayan dire maganganun shi, na shiga nazarin dalilin da ya janyo kayana suka salwanta. Sai dai ni a nawa hangen da ya yi shawara da ni, da ban ji rabin zafin da na ji yanzu ba. Saboda ni kaina ina buƙatar cigabansa, kuma ina fatar ya samu rufin asirin da zai riƙa ni ni da jinjirar 'yata Ummu Salma. Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi sannan na ce da shi,_
"Tabbas! Ranar biyan buƙata rai ba a bakin komai yake ba. Amma da ka yi shawara da ni tun farko ba za a rasa yadda za a yi ba, domin ina da tabbacin zan samo nama kuɗin registration ɗin ba tare da an taɓa kayana ba. Saboda ni yanzu ban san da wane baki zan yi wa su Umma bayanin yadda kayan suka yi b..."
"Ni ma ba na son ki yi musu bayani, don Allah ki bar zancen nan a tsakanina da ke ba tare da kowa ya sani ba. In da hali ma ki nuna kawai ni da ke ba mu san yadda suka yi ba, idan ta kama ma za mu ce ɓarayi ne suka sace a lokacin da ba na garin. Don Allah ki yi mini alƙawarin ba za ki tona cikin wannan magana ga kowa ba, har da Umma don Allah kada ki bari ta san gaskiyar maganar nan!."

_Gabaɗaya ya ɗaure ni da jijiyoyin jikina, na shiga tunanin maganganun shi tare da yadda zan fuskanci lamarin a tsanake. Domin na kare shi ba tare da an gano shi ne ya yi sanadin rasa mini kayan ba, amma na san duk abin da zan faɗa ba zan fita daga wannan laifin ba. Matuƙar ba gaskiyar zancen na tona ba domin na wanke kaina. Haƙiƙa zuciyata ta yi amanna da tsayuwa kai-da-fata, domin na yi masa garkuwar da za a kasa hango laifinsa, balle a jefe shi da wata maganar da ransa zai ɓaci."_
_Da wannan tunanin na kwana cikin raina, shi ko lallaɓa ni kawai yake yi tamkar wata sabon ƙwai har baccin ya ɗauke ni. Tun da safe ya fice gidan ko kayan cefane aiko mini ya yi a lokacin da rana ta take, domin na fahimci ko ido ba ya son mu haɗa kafin ya fita. Hakan ya sa jikina ya yi sanyi na tabbatar da cewa dole ce ta sa shi ya yi mini hakan, duba da yadda yake jin nauyina kuma yake jin kunya ta a kan abin da ya aikata mini._
_Ban san ya aka yi ba, mahaifiyar shi ta shigo ɗakin fuskarta a haɗe, tare da yin tagumi tana ƙare wa ɗakin kallo. Kafin ta yi magana cikin sanyin murya tamkar ta yi kuka._

"Don Allah ki yi haƙuri Zaituna, wallahi ban san wainar da yake shukawa ba sai yanzu da ya shiga yana yi mini bayani. Saboda a lokacin da na ji ana ɗibar kayan ana sakawa mota, sai da na kira shi na tambaye ina za a kai miki kaya. Kai-tsaye ya ce da ni daga gidanku aka aiko ɗauka, za a canza miki sababbi kafin ki dawo. Da wannan maganar ya rufe mini baki kuma ya toshe ƙofar zargin da ya shiga kaina. Don Allah ki yi haƙuri Zaituna, kuma in Sha Allah yau-yau ɗin nan duk inda zai nemo miki wasu kayan sai ya yi ko na tsine masa albar..."
"Haba-haba! Ai abin duka bai kai can ba Innar Hanafi. Ya yi mini bayanin komai tun jiya kuma na gamsu, don haka kada ki damar da kanki a kan hakan. In sha Allah babu abin da zai faru domin ba zan bari kowa ya san yadda gaskiyar abin yake ba. Kuma ya ce zai san yadda za a yi kafin hankalin mutane ya kawo kan kayan."

_Hawaye ta shiga sharewa da gefen mayafinta sannan ta fice gidan tamkar ta kife saboda sauri, domin fuskarta a haɗe take babu alamun wasa. Hakan ya tona asirin takaicin ta a kan abin da Mukhtar ya aikata mini ba tare da sanin ta ba._
_Bayan fitar ta da mintuna kaɗan ta aiko na rufo ɗakin na zo tana nema na, na yi wa Ummu Salma wanka na shirya ta tsaf tana zuba ƙamshi muka yi gidan. Haƙuri ta ƙara ba ni sannan ta roƙe ni da Allah kada na bari wani ya san da maganar, a cikin 'yan'uwana ko nasu. Saboda abin kunya ne da gori kawai hakan zai janyowa tare da faruwar abin da ba a yi tsammani ba. Don ta nuna mini muddin gidanmu aka sani rikici zai iya ɓallewa sanadin hakan, a ƙarshe ma abin ya shafi aurenmu._
_Har raina ba na fatar rabuwa da Mukhtar a lokacin, ko sakin da na nema ƙarfin hali ne kawai na yi domin na rage ƙunar da zuciyata ke yi._
_Daren ranar a gidansu Mukhtar na wuni, duk wanda ya zo a nan yake iske ni mu gaisa. Domin ko cefanen da ya aiko a nan na yi girkin ƙannen shi da Sajida ɗiyar Yayar shi suka taya ni. Domin Innar Hanafi tun da muka gama magana ta fice gidan, ba ta dawo ba har sai da duhun marece ya fara kawo jiki. Sannan ta zauna tana sauke numfashi, ina lura da fuskarta har da 'yar rama ta yi. Cike da mamakin me ya jigatar da ita take ta sauke numfashi alamun gajiya a tattare da ita._
_Abinci na kawo mata ta ci tana saka mini albarka, bayan ta gama ci ta ja ni ƙuryar ɗakinta ta ce na zauna. Cikin sanyin jiki na zauna zuciyata cike da tunanin abin da take ƙoƙarin sanar da ni, wanda ba ta so kowa ya ji daga ni sai ita sai Allah._
"Zaituna! Ina ƙara ba ki haƙuri a kan laifin da Mukhtar ya aikata miki. Kuma don Allah ki yafe masa don ko kaɗan bai yi miki adalci ba. Sannan abu na biyu da nake son sanar da ke, ki yi haƙuri a kan abin da za ki gani a ɗakinki. Na je na ƙulla da ƙyar na samo miki gado da kujeru, domin ba na farinciki mutane su taras da ke a yadda na gan ki babu komai sai faƙon ɗaki. Kuma don Allah kada ki bari hakan ya janyo muku tashin hankali ko ki ce za ki yi zuciya watarana ki sanar da Ummarki. Saboda muddin ta ji wannan magana ba za ta sake ganin girmansa idonta ba, kuma in Sha Allah sai ya biya ki kuɗin kayanki ko da arziƙi ko da tsiya-tsiya."

_Har ga Allah tausayinta ya kama ni, duba da yadda ta ɗaga hankalinta sosai a kan lamarin. Kuma kayan da ta faɗa na yi haƙuri da su, hakan ya nuna mini ita ce ta yi fafutukar nemo mini su, domin ta wanke kaso biyar a cikin goman laifin da Mukhtar ya aikata mini._
_Cike da ladabi na nuna mata babu komai kada ta damu, domin na ƙudurta komai za a yi mini a gida ba zan faɗi abin da zai sa a gano laifin Mukhtar ne ba._
_Sai da na yi sallar Isha sannan ƙannen shi suka raka ni ɗauke da Ummu Salma Sajida da kular abincin shi a hannu. Wanda na dawo takanas na ɗauki kula sabuwa na zuba masa, don Allah ya tsare bai taɓa mini kayan kitchen ba, sannan kuma na dawo da wasu sababbin da Umma ta saya mini na ƙara da waɗanda nake da su._

_Ƙwalla na shiga gogewa bayan ƙannensa sun tafi Sajida ma ta bi su sun fice. Na shiga dudduba kujerun da na gani a falona, sannan na nufi ƙuryar ɗaki na ga sabon gado da wadrobe har da madubi. Duk da ba su kai darajar nawa ba, amma har zuciyata na ji daɗin ganin su kuma na yi farinciki._
_Wanka na shiga sharp-sharp na kammala, sannan na feshe jikina da turaruka masu sanyi, na mulke jikina da wata shu'umar humra mai taken 'Yar Sakkwato. Saboda kayan matan da aka ɗirka mini da kazar ƙarin ni'imar da na ci, sun sa na ji ina kewar Mukhtar tare da zumuɗin ya kasance ni a raina. Kuma na yi alƙawarin zan faranta masa a daren ranar ko don Innar Hanafi, saboda ba ƙaramin daɗi na ji a kan kulawar da ta ba ni ba. Saɓanin baya da ba ta sake mini fuska tun bayan rikicin abincin da suka ce ina ba su kaɗan._

_Ban san na yi bacci ba sai da na ji ana shafa jikina, firgigit na farka tare da motsawa amma na kasa. Saboda Mukhtar da na ji ni gabaɗaya ya matse ni, sai aikin shinshina ta yake yi tamkar wani ƙaramin bunsuru. Don ko bai faɗa ba na sani turarukan da na saka a jikina ne suka zautar da shi. Idanuwana a rufe ina karɓar saƙon da yake ƙoƙarin aika mini na ce da shi; abincin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login