Showing 18001 words to 21000 words out of 121208 words
Tsawon lokaci ina cikin mawuyacin halin kafin zuciyar ta lafa numfashina ya daidaita. Ihun yara da bugun da ake yi wa ƙofar ɗakina hakan ya tabbatar mini da yara sun dawo. Daga nan inda nake na yi musu magana cikin ɗaga murya,
"Ku je ku yi shirin sallah!"
Shirun da na ji ya gasgata sun ji abin da na ce. Ko da aka yi kiran sallar magrib ban tashi ba har sai da aka fara tayar da Sallah. Sannan na miƙa cikin rashin kuzari na yi toilet na ɗoro arwala na yi sallah, na daɗe ina jera addu'o'i a kan Ubangiji ya kawo ƙarshen zamana da Mukhtar lafiya. Domin ba na fatar zuciya ta ɗebe ni na aikata abin da zai shafi mutuncin 'ya'yana na janyo wa Ummata da 'yan'uwana gori.
Daren ranar ban fita falo ba, a nan na ƙarasa aikin takardun sai da goman dare ta buga, sannan na gama na fito domin na ga a wani hali yarana suke. Addu'a na tofe su da ita sannan rufo musu ƙofa ina goge ƙwallar tausayinsu da ta gangaro mini.
Kasancewar ba na cikin walwalar zuciya setting ɗin WhatsApp kawai na yi, sai facebook da na ɗan leƙa bayan na buɗe. Ban wani jima ba na ajiye wayar saboda komai ya gundure ni, idan aka cire MD da ke gefen zuciyata motsi kaɗan sai na tuno shi a raina.
Da safe ma sai da na canye cikin shigar doguwar rigar atamfa ɗinkin A.shape. Na yafa mayafina mahaɗin atamfar da takalmin da suka yi shige da kalar atamfar. Na feshe jikina da turaruka ba tare da na damu da huduɓar MD ba. domin burin da nake da shi, a kan wani dalili ya yi tsanin haɗa numfashina da na shi ko da tazara ta ratsa tsakaninmu.
Kamar jiya har na saukar da yara makaranta ba su daina yabon kwalliyata ba. Duk da ban shafa komai a fuskata ba face powder da lips, sai ɗan kwallin da na zirara wanda sai an kula da gaske ake hango shi idona.
Tun a lokacin da na shiga ma'aikatar na fara cin karo da MD ya fito zai nufi motar shi. Ina hankalce da shi kallo ɗaya ya yi mini ya kawar da kai, murmushia a kan fuskata na gaishe shi ƙirjina yana bugawa. Saboda kwarjinin shi ya sa na manta da komai ta yadda ban san lokacin da na saki fuskata ba.
Haka na yi ta gaisawa da mutane fuska a sake, duk da kallon hadarin kajin da na ga wata ma'aikaciya tana yi mini. Ban damu ba kuma ban ji haushi ba, domin ba ta gabana tun asali balle na saka ta cikin abubuwa masu muhimmanci. Saboda tun zuwana wurin na fahimci akwai hassadata a cikin zuciyarta, sai ga shi na ji komai a bakin Amina. Ashe mijinta ne aka karɓe wa matsayi aka ba ni, asali ma aka kore shi gabaɗaya cikin ma'aikatar. Dalilin zanba zamba cikin aminci bayan ruf-da-ciki da sama-da-faɗin da yake yi wa kuɗin wurin. Wanɗanda yake wadaƙa son ran shi daga shi har matar shi wadda take matsayin mataimakiyar shi.
Ni da ban san lokacin da aka yi ba, amma hakan bai wanke ni daga shiga komarsu ba. Duk inda ta gan ni kallon banza ne ke raba mu, tun ina kula ta sama-sama har na tattara ta na watsar domin ba ta gabana. Surutan da take yi a kaina ma ban taɓa bi ta kai ba, domin ina ji a raina ba ta kai wadda zan ɓata lokacina a kanta ba.
Zama na yi a kan kujerar offis ɗina, ina dudduba aikin da na yi ina gyara inda ya dace. Kira ya shigo wayata na yi hanzarin fito da wayar a jaka babu shiri ƙirjina ya buga. Cikin sauri na ɗauka,
"Ki kawo takardun idan kin kammala aikinsu".
Zancen MD kenan bai ƙara da komai ba ya katse, cikin sauri na tattara takardun na yi offis ɗin shi. Da siririyar sallama na tura ƙofar na shiga, kaina a ƙasa na ajiye masa takardun zan juya.
"Shi dai wannan turaren ba za a daina saka shi ba kenan?"
Maganar da ya jefo mini kenan cikin ƙasan maƙoshi, shiru kawai na yi masa ina wasa da yatsun hannuna. "A matsayinki na matar aure, bai dace kina bari wani yana shaƙar ƙamshinki ba, wanda na san kin sani ko wadda babu aure kanta ba a halasta mata shafa turare dan za ta fita ba..."
"Sai bayan na saka na tuna, amma in Sha Allah zan kiyaye daga wannan".
Na ƙare zancen cikin sanyin murya da ƙara mata zaƙi. Bai ce da ni komai ba har na kai ƙofa zan fita na tuno saƙon shi na jiya da ban ga me ya rubuta ba. Juyowa na yi riƙe da handle ɗin ƙofar cikin ɗakiya na ce,
"Jiya ban ga saƙon ka ba wayar ta fashe. Ina ƙara godiya Allah ya ƙara buɗi".
"Amin" Ita kaɗai ya faɗa ya ci gaba da aikin da yake yi, na fito zuciyata fes saboda kulawar ta shi gare ni. Hakan ya tabbatar mini da fatsata ta fara kamo mini kifi.
Ranar ban yi aiki da yawa ba, ina tsaka da chatting Amina ta shigo, muka gaisa fuskarta babu yabo babu fallasa domin na kasa tantance yanayinta.
Zama ta yi tana sauke ajiyar zuciya ta ce "Jiya da tunaninki na kwana, ta yadda na matsu safiya ta waye na zo domin na ji tarihinki..."
"Ina Mama fatan tana lafiya?"
Tambayar da na yi mata kenan domin na ji yadda suka ƙare da rikicin kwanan. "Ina kwana ce kawai ta haɗa mu yau. Ita ma ba ta amsa ni ba, na ƙara yi mata duk da na san ta ji ni a farko. A masifance ta katsa mini tsawa tana faɗin na bar mata ɗakinta ba ta son gani na. Da na ƙi tashi ta yi kaina da duka na fice, a bisa tsautsayi ta rufo ƙofar ɗakinta cikin fushi ta dantse mini yatsun hannu na. Na jima ina jinyarsu kafin su rage mini zugi na samu ƙarfin fitowa".
""Hmmmmm! Batun kwanan fa a can ya kwana ko a wurinki?"
Shiru ta yi tana goge hawaye tsawon mintuna sannan ta ce, "A can ya kwana".
"Ki yi haƙuri komai yana da farko kuma yana da ƙarshe. In Sha Allah komai zai zamo tarihi watarana".
Daga ni har ita muka yi shiru, na shiga dogon tunanin cutarwar da mata suke fuskanta a gidajen aurensu. Tare da tambayar kaina 'Yaushe ne mata za su daina fuskantar ƙalubalen aure?'
'Babu rana' amsar da wata zuciyar ta ba ni kenan cike da tabbacin matuƙar ba a ɗinke ɓarakar ba, to ba za a taɓa daidaituwa tsakanin ma'aurata ba.
'Ta wace hanya?'
Tambayar da na sake yi wa kaina a zuciyata kenan, kafin Amina ta katse mini zancen zucin da nake yi, "Ina so ki sanar da ni abubuwan da kika fara faɗa mini jiya, wanda asali dalilin hakan ya sa na fito aiki yau. Domin ba na so na ƙi zuwa na yi missing wannan babban Flight'".
'Yar dariya na yi saboda ƙarshen zancenta, shiru na yi ina nazarin ta inda zan fara ba ta labarin kaina.
_"Kamar yadda kika sani sunana Zaituna Aliyu, amma Aliyu Yayan mahaifina ne ba shi ne asalin wanda ya haife ni ba. Sunan mahaifina Alhaji Sani. Na samo asalin sunan tun a ranar da Baba Ali ya saka ni makaranta tare da 'ya'yan shi. "_
_"Haifaffiyar Jahar Kebbi kuma 'yar asalin garin Fulani, waton ƙauyen Ɗakin Gari. Na taso a garin Kebbi tare da mahaifina kafin Allah ya yi masa rasuwa. Na ci gaba da zama a garin Kebbi hannun Baba Ali cikin unguwar Aleru Quarters har na kammala karatuna a matakin digiri. Inda na yi Federal staff school nursery, primary and secondary. Sannan na ci gaba da karatun jami'a a Federal University Birnin Kebbi "_
_"Mahaifiyata 'yar asalin jahar Sokoto ce. A ƙaramar hukumar wamakko lokal government. Jefi-jefi ina kai mata ziyara a duk lokacin da na samu sarari, sai dai ba na daɗewa idan ba babban hutu aka samu a makaranta ba."_
_"A irin wannan ziyarar da nake kai wa Ummata a garin Sokoto na haɗu da Mukhtar har Allah ya ƙaddara aure tsakanina da shi. Sai dai kafin auren ya tabbata sai da aka yi ɗan ƙaramin gumurzu."_
Ni ma dai a matse nake da na ji tarihin aurenki da Mukhtar da wannan gumurzun😅
D. AUTA CE✍🏼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
_*Ban yarda ba, ban amince a juya mini littafi, ko a yi amfani da shi ta kowace fuska ba tare da izinina ba. Saɓanin haka zan ɗauki matakin gaggawa wanda babu sani balle sabo😼*_
*LAMBA SHA ƊAYA.*
_A ranar da na fara haɗuwa da shi, ina kan hanyar zuwa Bafarawa estate na fito Line G. Inda na kai wa wata ƙawar mahaifiyata ziyara a bisa umurnin ta. Domin ɓeran masallaci ce ni babu inda nake zuwa kullum ina gida, wannan fitar ma ta matsa ne sai na je na gayar da danginta da ke Dunguza, saboda babu tazara tsakanin su da Line G . Kullum suna ƙorafin ba ta bari na yi zumunci, idan na zo har na koma ba su sani ba. Su yi ta mita bayan sun juye laifin da nufin ita ce ba ta so na yi zumunci da su._
_Kasancewar ba wata tazara ce mai yawa ba, na zaɓi komawa ƙasa domin na miƙa ƙafafuwana. Na fito Line G. Kenan daidai polo na ji magana a bayana, cikin sauri na waiga na yi tolazi da fuskar shi ɗauke da murmushi. Amma tun daga kallo ɗayan da na yi masa ban sake bi ta kan shi ba, tafiya nake yi yana bi na a baya yana faɗin,"_
"Don Allah ki tsaya ki saurare ni, unguwarku kawai nake so ki sanar da ni sai lambar wayarki".
_Na ci gaba da tafiyata ban tsaya ba balle na tanka shi kamar yadda yake so. Tun yana yi mini magiya ina jin haushin takurar da ya yi mini har ta kai ya fara ba ni tausayi. Saboda muryar kukan da na ji ya koma yi cikin marairaitar da ya yi nasarar saka ni tsayawa na ce da shi,_
_"Ka yi haƙuri ba na magana a kan hanya..."_
"Lambar wayarki kawai nake so ki ba ni. Sannan ki sanar da ni a ina zan same ki?"
_Tafiya na ci gaba da yi ya biyo ni yana ci gaba da roƙon lambata amma ban sake bi ta kan shi ba, har na isa gidansu Ummata da ke Bafarawa estate._
_Kwana biyu tsakani ina tsaka da aiki aka aiko wani yaro ana kira na, ina gunguni haɗi da tsaki na fito. Saboda takurar da Umma ta yi mini a kan dole sai na je na ga wanda ke nema na. Da mamaki na bi shi da kallo saboda tunanin wa ya sanar da shi unguwar balle gidan da nake. Murmushi ya bi ni da shi hannun shi a aljihu ya ce,_
"Kin yi mamakin gani na ko? To Hausawa sun ce mai son ɗan tsuntsu shi yake bin shi da jifa, shi ya sa na biyo sawunki sau da ƙafa har na ga gidan. Saboda na gani kuma na yaba da kalar tarbiyyarki. Hakan da kika ya ƙara miki matsayi a zuciyata da ƙima a cikin idanuwana. Don haka ga Muhammadu Mukhtar da fatar ya yi miki a matsayin mijin auren ki!".
_Shiru kawai na yi domin har zucina natsuwar shi ta burge ni, sai dai a lokacin ba aure ne a gabana ba domin farkon shiga ta Jami'a kenan. Kuma ina da burin karatun shi ya sa ba na kula samari ko a Kebbi duk da takurar da suke yi mini. Don asali ma akwai wani da muke soyayya da shi sai dai Baba Ali bai yi na'am da shi ba. Hakan ya sa duk nacin da yake yi a kan ya turo Iyayen shi a tsayar da magana bai amince da hakan ba. Dalilin da ya sa na fuskanci karatun da kyau domin na samu abin da na je nema._
_Ajiyar zuciya na sauke sannan na ce,_ "Ka yi haƙuri da abin da na yi, saboda ba na tsayawa magana a titi. Musamman irin Polo club da ta zamo mahaɗar kasuwanci da dandazon mutane..."
"Hakan ma ya tabbatar mini na yi zaɓen matar aure a inda ya dace. Amsar ki kawai nake buƙata yanzu domin ita ce abu ma fi muhimmanci a wurina".
_Shiru muka yi daga ni har shi ina wasa da gefen hijabina amma jikina a mace saboda daburcewar da na yi na rasa me zan ce. Ga kuma jikina ya ba ni idon shi duka a kaina suke, na yi jarumtar ɗagowa domin na saci kallon shi. Caraf muka haɗa idanuwa na yi saurin janye nawa ina masa kallon gefen ido, amma shi kafe ni ya yi da kallo ko ƙyaftawa ba ya yi. Na kawar da kaina gefe tare da rungume hannu a ƙirji na ce,_
"Ka ba ni lokaci zan sanar da kai idan na gama shawara".
Shiru ya yi na ɗan lokaci sannan cikin sanyin murya ya ce, "Kamar zuwa yaushe za ki gama shawarar?"
"Sati ɗaya"
Na ba shi amsa ina ɗan murmushi, ya maraice murya yana faɗin "Kafin lokacin na zama gawa ai".
_Dariya ta suɓuce minu saboda sosai zancen shi ya ba ni dariya, domin yanayin da ya yi maganar yana karye wuya tamkar yaron da aka ƙwace wa alawa yana tsaka da jin zaƙinta._
"Kwana uku ai ya yi ko?"
"Kwana ɗaya tak zan iya juriya, ko shi zan kasance cikin wasiwasi da ƙididdigar lokaci. Don haka ki taimake ni ki sanar da ni yanzun nan ko don na fita fargabar da nake ciki..."
"Ka kwantar da hankalinka in Sha Allah alheri ne".
_Daga haka ya ci gaba da ja na da hira har duhun magrib ya kawo jiki. Sallama muka yi da shi bayan na ba shi lambar wayata, domin ya kira ya ji amsar shi gare ni._
***
_Abu kamar wasa soyayya mai ƙarfi ta shiga tsakanina da Mukhtar. Saboda ƙarfin da Umma take ƙara wa abin a ƙoƙarinta na son na yi aure Sokoto ko don na dawo kusa da ita. Amma Baba Ali bai karɓi abin kamar yadda Umma ta ɗauke shi da muhimmanci ba.
Familyn su Mukhtar sananne a cikin garin Sokoto, shi ya sa ba a sha wuya ba yayin binciken asalin shi, wane ne shi a idon mutane._
_An ɗauki lokaci muna soyayya da Mukhtar, kuma Baba Ali bai hana shi zuwa wurina ba kamar yadda ya yi mini iyaka da Jafar. Saboda ya nuna ƙarara ba zai ba shi ni ba, saboda asalin tushen shi Rundawa ne su. Kuma a cewar shi abin kunya ne da Allah-wadai ga Bafulatanin da ya haɗa zuri'ar shi da masu Fawa. Duk da wasu daga cikin 'yan'uwanmu sun tunatar da shi Allah bai haramta ba, amma ko kaɗan bai yi amanna da hakan ba. A ƙarshe ma fitowa ya yi a fili ya sanar shi ya yi mini miji ya yi haƙuri._
_Sosai na ji tausayin Jafar saboda na san kalar son da yake yi mini marar algus. Duk da a lokacin ni kaina zuciyata ta fi karkata da son Mukhtar fiye da shi. Dalilin hakan na tattara shi gabaɗaya na ajiye gefe, na bai wa Mukhtar matsayi mai girma a raina. Bayan lokacina da na sadaukar masa, amma ban bari ƙaunar da nake yi masa ta shafi karatuna ba. Kasancewar doka ce ta musamman Baba Ali ya gindaya mini, duba da yadda na yi nisan kiwon da ba na jin kira a kan soyayyar Mukhtar._
***
_Zancen aure na da Mukhtar ya kankama har an kawo sadakina. Domin ƙa'ida ce a wurin Baba Ali ba ya bari a yi wa 'ya'yan shi lefe, duk da yake ɗan boko kayan fitar biki kawai yake ɗora wa wanda zai auri 'yar shi. Saboda ba a kaina aka fara ba shi ya sa ban wani damu ba. Amma Ummata ta ji haushin hakan kasancewar ni kaɗai ce gare ta har lokacin. Duk da ta yi aure biyu bayan mutuwar Babana amma babu inda ta haifu._
_Mukhtar ya nuna mini jin haushin shi sosai dangane da soke lefen da Baba Ali ya yi. Domin ya sanar da ni har ya gama haɗa komai lokacin kawo mini kawai