Showing 81001 words to 84000 words out of 121208 words

Chapter 28 - ABOKIN AIKINA HAUSA NOVEL

24 Nov 2024

6412

Mere na yi musu daga shi har ita, sannan na ci gaba da bai wa su Ummu Salma umurnin su yi sauri su gama su tafi.
"Wai fa abincinka ne ta ɗauko ta zube wa yaran, bayan kuma sun ci abincin tun lokacin da na gama girkin."

Kallo na kawai ya dinga yi fuskarsa a haɗe sannan ya ce,
"Wai ke don Allah har abada ba za ki bari a zauna lafiya ba? Yanzu wannan abin da kika yi miye ribar shi?"

"Daga kai har ita ban da lokacinku! Don haka idan ta gama shirya maka zance ka haye, to ka zuba mini fetur ka ƙone mu duka mu kama da wuta daga ni har yaran."

Wata zabura ya yi tare ƙoƙarin kai mini duka, ta yi hanzarin riƙe shi tana faɗin,
"Don Allah Romiyo ka ƙyale ta a bar ta da halinta. Idan ma sun ci ai 'ya'yanka ne ba na kowa ba. Mu je na ba ka wanda ta bar mana ai gobe ma rana ce!"

"Da ba ki hana shi ba! Tun da ba ki ji kunyar yin ƙaryar da za ki haɗa ni da shi ba. Na rantse da Allah duk ranar da ka yi gangancin taɓa jikina da sunan duka sai na illata ka. Ke kuma baƙar Munafuka annamimiya sai kin gwammace ba ki san shi ba a faɗin duniya, don sai kin yi kukan da ko uwarki ta mutu iyaka kenan. A dai juri zuwa rafi watarana tulun zai fashe."

Ba su ce da ni komai ba, ta ja shi suka shige kitchen na ce da su Ummu su tashi su je tun da sun ƙare.
Na zauna ina ta huci tare da girgizar ƙafafuwa, saboda na zo wuya komai zan iya aikatawa a lokacin. Su Ummu Salma suka fice gidan tamkar ƙwai ya fashe musu a ciki, su kuma tsuntsayen soyayya suka fito aka baje tsakiyar kujerunta. Shwagaɓa ta dingà yi masa tana ba shi abinci a baki suna hira ƙasa-ƙasa, idan abin ya yi musu daɗi su fashe da dariya.
Komawa ɗaki na yi na ɗauko wayata na kwanta, na fara waya tamkar gaske cikin kashe murya ina faɗin,
"Haba dai ai kai ma ka san bayan kai babu wani a faɗin duniya. Daina zancen wannan lusarin, wanda bai ajiye komai ba face masifa da hargowa tamkar zai cinye mutum da ransa."

Shiru na yi kamar yadda su ma suka yi tsit tamkar ba su cikin falon, dariya na yi mai sauti sannan na ce,
"Cabɗijam! Ai ka yi shiru kawai abin ba a cewa komai. Fankam-fankam ai ba ya kilishi, ita ma kwana biyu za a jone mu bi sahu. Ai na rantse da Allah da ta san kowane ne ba za ta yi gangancin raɓarsa ba. Saboda muddin ya ƙyalla ido ya hango wata ƙawarta sai ta sha mamakin abin da zai aikata mata. Yo nawa aka yi wai an yi wa ɓarawo kashedin sata?"

Wayar na ji an fisge ba tare da na ji lokacin da aka zo a kusa da ni ba. Da sauri na miƙe fuskata a haɗe na ce da shi,

"Ban wayata!"

"Sai kin faɗa mini da uban wa kike waya? Kuma wane ɗan iska ne ya kira ki?"

Raina fes ba tare da shayin komai ba na ce da shi,
"Da uban da ke so na yana dakon aure na! Sannan da ɗan iskan da ka ajiye mini ina lalata da shi a waje."

Kallona ya dinga yi bakinsa yana rawa, na yi 'yar dariya sannan na ce,
To ba ni wayar tun da na amsa tambayar ranka shi daɗe! Romiyo mijin Barcy!"






Kai jama'a🤭Ni dai babu luwana yasin🏃🏻‍♀️



D.AUTA CE✍🏼


*ABOKIN AIKINA*


*@HADIZA D. AUTA*


*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*


*TALATIN DA HUƊU.*

Ƙwafa kawai ya yi sannan ya juya yana ƙoƙarin barin wurin, na bi bayansa da hanzari ina faɗin,
"Ka ba ni wayata!"

"Ba zan bayar ba! Idan akwai wanda zai ƙwatar miki ki kira shi ya zo yanzu!"
"Babu mai ƙwatar mini don ba yau ka saba cin haramun ba, don haka ka ba ni wayata tun muna shaida juna!"
Banza ya yi da ni ya nufi ɗakinsa Barira ta bi shi tana faɗin,
"Don Allah Romiyo ka ba ta wayarta mu je ka ƙarasa cin abincinka."

Juyowa ya yi yana huci tare da nuna wayar a sama yana cewa, "In dai wannan wayar ce! To ba zan bayar da ita ba, gobe ma idan na sake ganin tana waya da wani ɗan iskan; sai na sake ƙwace wata."
Wurinsa isa a fusace na yi tsalle zan cafke wayar, ya yi hanzarin saukar da hannun tare da tura wayar aljihunsa. Raina a ɓace na ce,
"Ba ni wayata wallahi ko yanzu na yi abin da bai dace ba!"

"Ba zan bayar ba ki yi abin da za ki iya."

Cikinsa na yi na mamaye shi na cafko jarumarsa na murɗe iya ƙarfina, ihu ya saki tare da faɗin,

"Wayyo! Za ta kashe ni!"

Jikinsa yana rawa ya fiddo wayar daga aljihu ya miƙo mini sannan na sake shi, barin wurin na yi a fusace ina faɗin,
"Ai da kada ka bayar! Da na tsinke ta na dafa maka a tukunya ka cinye ƙazantarka."
"Ta Allah ba taki ba wallahi! Idan burin ki nakasa ni ki yi wa Barcy asara, to gani nan bari nan! A gabanki za mu shimfiɗa rayuwa mai daɗi sai dai baƙinciki ya kashe ki."
"Soloɓiyo mai aiki irin na matan ne zai iya rayuwa mai daɗi da mace? Ka bari sai ka samu cikakkiyar lafiya sannan ka yi alfakhari da burgar da iyakarta cikin baki."

"Gaskiya Aunty wallahi abin da kike yi kwata-kwata ba kya kyautawa. Ai Romiyo ko ba mijinki ba ne ya dace ki girmama shi balle yana matsayin uban 'ya'yanki."
Barira ta yi maganar tare da isa wurinsa ta lafe jikinsa tana faɗin,
"Ka yi haƙuri Romiyo, wasu matan haka suke yi wa mazajensu komai a tsaitsaye, tamkar tsararrrakinsu."

Kallon ta kawai nake yi saboda gaskiya ta yi mini yawan da ban san me zan faɗa mata na huce ba, dawowa na yi gabansu ina nuna ta da hannu na ce,
"Kada ki sake shiga sabgata idan kika ga ina yi da shi! Idan kuma kika sake zan bambance miki tsakanin aya da tsakuwa."
Shiru kawai ta yi tana turo baki bayan muimui ɗin da take yi ban san me take faɗa ba. Sannan ta ɗage kanta sama ta ja hannunsa suka yi ɗakinsa.
Bayansu na bi da kallo ina wassafa irin bugun wahalar da zan yi mata idan ta kai ni bango. Ban san ya suka yi ba, ina zaune kan kujerar na ga ta fito ɗakin a fusace ta yi ɗakinta.

Sallamar Sajida da su Ummu Salma ta katse mini tunanin da na shiga tsawon lokaci, sannan ganin su ya kore mini rabin damuwar da Mukhtar da Barcynsa suka cusa mini a zuciya.
Riƙe da hannun Haidar ta iso tana gaishe ni a ladafce, sannan ta zauna tana faɗin,
"Tun ɗazu na so zuwa bazawarina ne ya zo!"

"Sannu Sajiji! Gaskiya ki fito da miji haka nan mu aurad da ke."

Shiru ta yi sannan ta sauke ajiyar zuciya ta ce, "Wallahi Aunty har yanzu ban daina jin mutuwar Abbakar cikin raina ba. Shi ya sa duk wanda ya zo nake jin kamar ba zan iya rayuwa da shi ba."

"Haƙuri za ki yi, don Allah ba ya barin mutum don wani ya ji daɗi. Lokacinsa ne ya yi, kuma Allah ya tsara ba za ku yi rayuwa mai tsawo da shi ba. Allah dai ya ƙara haske cikin ƙabarinsa"
"Hmmmmm! Haka ne gaskiya, amin Ya Allah. Wai kin san wani abu Aunty?"

"A'a sai kin faɗa"

Na ba ta amsa cike da ƙaguwar na ji me za ta faɗa mini. Tagumi ta yi sannan ta ce da ni,
"Mijin maƙociyar nan taki ne yake ta damuna da zancen aure. Ni kuma wallahi kirkin da na ga kuna yi da ita, ya sa ba na son na rufta. Amma ke ya kike ganin lamarin? Don na ga matarsa da shegen kishin tsiya."

"Wace maƙociyar daga ciki?"

"Wannan Maman Taufiƙ ɗin."

Daram-dam! Shi ne sautin bugun da ƙirjina ya yi zuciyata ta hau bugawa.

"Ina ya gan ki?"

Na jefo mata tambayar a ruɗe bakina yana rawa. "Bari kawai Aunty! Tun ranar bikin da muka je gidanta dafa abincin baƙinki. Ina hankalce da shi yana satar kallo na, hakan ya sa na mayar da hijabina da na cire saboda aiki. Ban san ya aka yi ya samu lambata ba, kawai da dare bayan na koma gida sai ga kiransa a wayata. Bai ɓoye mini komai ba ya sanar da ni so na yake yi da aure, saboda wadda zai aura tsohon mijinta ya dawo Iyayenta sun matsa mata sai ta koma gidansa, ko don yaran da ke tsakaninsu. To ni kuma wallahi ina tsoron kishin matarsa, ga shi mun yi mutunci da ita sosai a lokacin hidimar bikin nan. Har ga Allah ina jin kunyar na auri mijinta, ga shi kuma ya nace mini da kira dole sai na faɗa masa ra'ayina. Shi ya sa na ce zan yi shawara da ke duk yadda kika ce shi kenan."
"Cabɗijam! Akwai matsala Sajida! Don wallahi matar nan ta shi ba dai kishi ba. Hmmm! Kin san me? Kawai ki ce da shi ya yi haƙuri kina da wanda za ki aura."

"Haka za a yi Aunty! Don ni ma dai ina jin nauyi wallahi. Sannan ɗan banzan kishin nan na matarsa ma ba zai bari mutum ya ji daɗin auren ba."
"Kin gane karatun! Allah ya ba ki wani nagari ki yi auren ki ki huta."

"Amin wallahi!"

Shiru muka yi dukanmu kafin muryar Barira ta katse mana tunanin zucin da muke yi, saboda waƙar da take yi cikin ɗaga murya tana faɗin,
"Allah ya aika munafukinmu ƙarshen nesa."
"Tafiyar ƙasa ko da lafiya ko babu."
"Na sha tabara na sha yasin."

Ƙaƙƙarfan tsaki Sajida ta buga mata sannan ta ce da ni,
"Aunty kawo wayarki na saka miki hotunan biki da aka yi mana. Na so tura miki ta WhatsApp, ganin zan zo gidan ya sa na fasa"

Na miƙa mata wayar ta loda mini su duka. Ta miƙo mini wayar tana faɗin,
"Hotunan sun yi kyau duba ki gani. Na ma saka miki wasu status ɗinki."

Ras na ji gabana ya faɗi, saboda ban so ta ɗora wanda muke da Mukhtar ba. Na goge inda nake da shi duk da na san masu GB dole sai sun gan shi.
Hira muka ci gaba da yi, da ta tashi tafiya muka yi sallama na raka ta har bakin ƙofar gida. Daidai lokacin da Baban Taufiƙ ya danno kan motarsa ya durfafi ƙofar gidansa.
Juyawa kawai na yi don ba na so ma na ga abin da zai biyo baya. Saboda har ga Allah ba na fatar Sajida ta aure shi ko don Maman Taufiƙ da halinta.

***
Daren ranar ban yi bacci mai daɗi ba, hakan ya sa safiyar Litinin ta waye mini babu kuzari, na ji kamar kada na fita wurin aiki. Ƙarfafa kaina na yi dole na shirya tare da su Ummu Salma, da ke nasu shirin zuwa makaranta.
Sai dai inda gizon ke saƙar babu komai na kalacin safiya a kitchen, domin alamu ya nuna Barira ba ta fito ba ma balle ta girka mana. Haushi ya sa na yi mana boiling ruwa na jefa Indomie ta jiƙa, a gurguje na saka mana mai da yaji.
Nan take muka lamushe saboda mun daɗe ba mu ci ta a hakan ba ta yi mana daɗi sosai. Kiran da Najib ya mini a waya ya sa muka fito tare da su duka za mu fice.
"Ai wallahi ba zan girka komai ba a gidan nan don ba boyar kowa nake ba."

Maganar da Barira ta yi kenan tana ƙoƙarin fitowa daga ɗakinta Mukhtar yana bayanta. Turus ta yi a lokacin da ta gan mu ni da yaran za mu fice,
"Aunty ina za ku je ba ku karya ba?"

Kallo ma ba ta ishe ni ba daga ni har yaran muka fice ba tare da mun tanka su ba dukansu. Muna ƙoƙarin shiga adaidaitar Mukhtar ya iso wurin yana faɗin,
"Yanzu abin naki har ya kai ki hana yarana su gaishe ni?"

"Ina kwana?"

Ita ce gaisuwar da Najib mai adaidaita ya yi wa Mukhtar yana sosa ƙeya, ni kam kallo ma bai ishe ni ba illa umurnin da na bai wa Najib,

"Mu tafi ka ji!?"

Ya buga adaidaitarsa ya tafi muka bar Mukhtar a nan tsaye yana kallon mu.

'Dole na canza tsari'

Zancen zucin da na yi kenan saboda ganin tsarin da na ɗauka a kan girki, ba zai haifa mini ɗa mai ido ba. Domin ni da 'ya'yana ne za mu tagayyara, ita da shi ko a jikinsu mu ne a wahala. Na tsayu a kan ci gaba da girkina daga ni sai yarana, tun da ba wani amfani yake yi mini ba ba zan jira ta yi girkin kwanakinta na yi nawa ba.

'Zan fita sabgarsu duka, kuma zan dinga abincina daga ni sai 'ya'yana.'

Tunanin da na yi kenan a cikin zancen zuci, na sauke ajiyar zuciya sannan na ce da Ummu Salma. Idan suka dawo ta yi mana abinci kamar yadda take yi kafin zuwan Barira, kuma kada su yi abin da zai janyo rikici a dake su a banza.

Bayan an ajiye ni na fara taku a hankali zuciyata cike da tunanin abin da zai faru, idan sun dawo ba na gidan. Gaisawa na yi da mutane suna yi mini ya jiki ina amswa har na isa offis ɗina.
Key na saka na buɗe sannan na shiga da sallama a maƙoshina. Kujerun na kakkaɓe sannan na share Ofishin tas na goge, saboda ƙurar da ya yi tsawon kwanakin da ban zo ba. Ga shi makullin yana hannuna na mance ban bai wa Amina ba a lokacin bikin.
Zama na yi ina sauke numfashi sai ga ɗaya daga cikin masu shararmu ta ƙwanƙwasa mini ƙofa. Umurni kawai na bayar a kan a shigo ta fara gaishe ni na amsa mata a mutunce.

"Hajiya shara za a yi!"

"Ki je kawai Inna har na share!"
"Allah ya saka miki da alheri ya ƙara duba gabanki da bayanki."

"Amin." Na faɗa zuciyata a sake saboda na ji daɗin addu'ar sosai. Fitar ta ke da wuya wani masinja ya zo yana faɗin,
"Ranki shi daɗe Oga yana kiran ki."

"Ok!" Ita ce iya maganar da na yi ya fice na miƙe ina kakkaɓe ƙurar da ta ƙi sakin jikina, sannan na nufi ofishin fuskata a haɗe ƙirjina yana bugawa.

Sallama na yi cikin siririyar murya ya amsa mini a gadarance tamkar ba ya so. Takardu na gani a gansa tsibi guda da hannu ya yi mini nuni da su a kan na ɗauka. Harara na wurga wa kwantaccen gashin kansa da ya sha gyara, saboda haushin izzar da yake ji da ita a lokacin.

Ɗauka na yi kawai ba tare da na ce da shi komai ba na nufi hanyar fita.
"Ya hidimar bikin? Fatan Allah ya ba da zaman lafiya."

"Amin" Kawai na faɗa na fice, tunanin ƙara yi masa godiya ya faɗo mini a rai na koma. Bakin ƙofar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login