Showing 93001 words to 96000 words out of 121208 words
zauna, sannan ta kawo mini tuwon dawa da miyar kuka ta sha nama. Na zauna ina ci tare da Haidar tana tsokanar shi da sunan acici ba ya ƙoshi.
Daga nan inda muke na jiyo sautin Umma cikin fushi tana faɗin, "Babu wata gaisuwar ka da nake buƙata. Ka yi gaggawar kawo mata takardar sakinta cikin mutunci, ko kuma kotu ta raba mu da kai cikin tsiya."
Ban san me aka ce da ita cikin wayar ba, amma tabbas wani sanyin daɗi ya ziyarci zuciyata. Domin na tabbatar Mukhtar ne take waya da shi, kuma matakin da ta ɗauka a kan aurenmu ya yi mini daɗi sosai.
"Babu wani daɗin bakinka da zai yi tasiri gare ni a wannan karon. Abin da nake so da kai kenan, ko da arziƙi ko da tsiya-tsiya."
Shiru muka yi dukanmu, ina ta juya maganganun Umma cikin raina. Inna Kulu ta miƙe ta yi ɗakin, Mintuna a tsakani na ji ta fara faɗin,
"Kada ki yanke hukunci cikin fushi Habi. Ki bari a bi komai a hanka..."
"Babu wani hankali da zan bi Mukhtar da shi yanzu! Allah ya tsine wa damarmakin da aka ba shi a baya yana fatali da su cikin izgilanci. Ko ya ɗauka neman kai nake yi da ita ne? Shi ya sa yake abin da ya ga dama ana ƙyale shi don albarkacin 'ya'yan shi. To wannan karon; ko ɗa dubu ne a tsakaninsu sai ya ba ta takardarta. Idan kuma ya ƙi bi ta lallami; zan nuna masa na fi shi zafin kai. Har yaushe zai dinga dawo mana da hannun agogo baya? Sai an yi gaba a dawo baya! Kullum da sabuwar matsala yake zuwa. To idan na danne ta cikin gidansa yana cusguna mata; wallahi a wannan karon ba zan zaunar da ita ta ƙara fuskantar baƙincikin kishiya ba."
Daga nan inda nake zaune, ban san lokacin da na juya gabas na yi Sujudu shukur ba. Saboda tsabar farincikin da ya lulluɓe zuciya, bayan wani sabon kuzarin da na ji ya shiga jikina.
Tuwon da ke gabana na ture gefe, sannan na miƙe na nufi ɗakin Umma cike da karsashi na zauna. Inna Kulu tana ci gaba da tausar ta amma ƙanzil ba ta ce da ita ba. Hakan ya sa na yi gyaran murya na ce,
"Umma ki daina ɓata ranki a kan banza. Ki bar ni da su daga shi har matarsa na fi ƙarfinsu wallahi. Don da kin ga amaryar tasa ma ba za ki ji haushin komai ba, saboda ko matsayin 'yar aiki ba zan ɗauke ta ba balle matsayin kishiya."
"Kishiya ko ta 'yar tsana ce sunanta kishiya! Ke ba ki san ire-iren waɗannan matan sun fi komai iya kissa da kisisina ba? To ki bar raina allura ƙarfe ce! Don tuggun da za ta haɗa ke ba za ki iya yin sa ba."
Abin da Umma ta faɗa kenan idonta a kaina. "Hmmmm!" Ajiyar zuciyar da na sauke kenan ba tare da na sake furta komai ba. Tagumi Inna Kulu ta cire tana faɗin,
"Ko dai ya abin yake don Allah kada a yanke hukunci cikin fushi. A bi abin a hankali ko don yaran nan da suka fito daga jikinsa."
"Yanzu da a ce gayyar marasa albarkar nan sun illata ta ko sun taɓa lafiyarta; me zai ce? Ai ya san da zuwan su amma bai hana ba! Kenan duk abin da za su yi mata su yi kawai ya ba da ƙofa! To wallahi ko ɗiyar riƙo ce na san zafinta, balle ni na durƙusa ƙasa na haifo ta wata tara da kwana tara. Idan ma ya gaji ai babu dole! Ya sauwaƙe mata kawai tun da ba shi ne autan maza ba."
"Ke kuma ke da wa kike ta masifa har ƙofar gida ana jin sautinki?"
Zancen Kawu Sale kenan da carbi a hannunsa yana ja, alamun daga masallaci ya fito.
"Ni da mara mutuncin can Mukhtar mana! Don haka ka sani ka ƙara sani; wannan karon babu mai raba ni da shi sai Allah! Sai na nuna masa na fi shi ɗibar albarka da duk abin da yake taƙama da shi!"
Umma ta ƙare maganar a zafafe tare da ɗaga murya. "To ki fara shawo kan matsalar yaransa da ke nan ƙofar ɗakinki suna kuka. Tun da ke kullum ba ki bari a bi komai a hankali sai kin yi faɗa da tashin hankali!"
Yana ƙare faɗar hakan ya bar jikin ƙofar yana ci gaba da surutai. Umma ta yi wani mere sannan ta ce,
"Komai za ka faɗa ka faɗa kawai! Amma wannan karon ba zan ɗaga wa Mukhtar ƙafa ba! Idan kuma ka matsa sai na tattara kayana na bar maka gidanka. Na fi so na kama haya na zauna tare da ita da yaranta duka. Amma ba zan taɓa barin ta cikin baƙincikinsa ya kashe ta ba wallahi!"
"Wannan kuma naki ra'ayi ne! Don ba ki ji na ce komai a kan zamanta gidan nan ba. Idan ma zatonki don ba na so ta zauna mini ne nake so ta zauna gidan mijinta; to ki yi haƙuri na daina daga yau. Ga gida nan ta zauna daga yanzu har mahadi ya bayyana babu mai korar ta."
Ya ƙare maganar hannunsa riƙe da ƙofar ɗakinta, don har ya tafi ya dawo domin ya mayar mata da raddi. Inda da sabo mun saba ganin rikicinsu, wanda sai sun hau sama ita da shi su faɗo ƙasa su shirya kamar ba su ba.
Shi ya sa Inna Kulu da 'ya'yanta suke burge ni, saboda babu ruwansu da shiga faɗansu. Ni ma a baya idan na ga suna yi kuka nake yi, na yi ta bin su ina ba su haƙuri, amma Inna ta fahimtar da ni ba a shiga tsakaninsu kunya ake ji.
Na gasgata hakan don sai sun gama faɗan suna cikin fushi Umma ta ce da ni,
'Ke ni ma fa faɗan ƙarfin hali ne kawai nake yi da Salenmu. Don duniya kaf ban da kamar shi shi ma bai da kama ta.'
Murmushi na yi kawai saboda tuno zancen Ummar. Fuskata a sake na ce,
"Yanzu dai Umma don Allah ku bar maganar nan. Saboda Mukhtar bai kai darajar da zai dinga haɗa ki faɗa da ɗan'uwanki ba. Idan ta ni ce ma ko yanzu na koma gidan na ci gaba da haƙurin da nake yi. Don na san komai daren daɗewa gaskiya za ta yi halinta."
"Ba za ki koma gidansa ba! Idan kuma so kike yi a raunata ki ki je ki jira dawowar masu farautar rayuwarki!"
"Yi haƙuri Umm..."
Sallamar da muka jiyo ana rafkawa a ƙofar gida, hakan ya sa Kawu Sale ya amsa sannan ya fice. Mintuna a tsakani muka yi zaman jugum-jugum har ya dawo yana faɗin,
"Ke aka zo nema!"
Ummar da yake kallo ya sa muka gano da ita yake, miƙewa ta yi tare da mayar da hijabinta ta fice. Inna Kulu ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce,
"Tun da tana jin maganarki Zaituna! Don Allah ki fahimtar da ita. Ta bari a yi komai a hankali ko don yaran nan."
Kawu Sale ya shigo ɗakin yana faɗin,
"Na san mijinki bai da mutunci, amma muddin aka biye ta Habi; ba za a haifi ɗa mai ido ba. Idan ma rabuwar ce a yi ta mutunci ba irin wadda girma zai zube ba."
Murmushi na yi sannan na ce, "Ka yi haƙuri Kawu! In sha Allah komai zai tafi yadda ya dac..."
"Wallahi! Ko kai ne autan maza Zaituna ta gama zama gidanka! Ba kuka da ruwan hawaye ba, ko na jini za ka yi ka daɗe ba ka yi ba. Munafukin banza mutumin kawai!"
Zantukan Umma kenan cikin ɗaga murya, da sauri muka fito ɗakin saboda ba na so tana tayar da jijiyoyinta a kan Mukhtar.
Kawu Sale ya shige ɗakinsa ni da Inna Kulu muka nufi ƙofar gidan.
'Kayan haushi!'
Zancen da yi kenan a zuciyata tare da guntun tsaki. Saboda ganin Mukhtar durƙushe ƙasa gaban Umma yana kuka har da majina.
Hannuwansa ya haɗa yana faman magiya tare da roƙon ta a kan ta janye furucin da ta yi, wanda ta shata mini layin komawa gidansa har abada.
Baban Taufiƙ da ke tsaye rungume da hannuwansa a ƙirji, shiru kawai ya yi kansa a duƙe ban ji ya ce komai ba. Har sai da ya ɗago kai ya gan ni sannan ya ce da ni,
"Don Allah ki bai wa Umma haƙuri. In sha Allah ba za a sake samun matsala ba."
Kallon banza na yi masa sannan na ce da Umma,
"Koma gida abin ki ki bar ni da su."
A fusace ta ce, "Ba zan bar ki da su ba! Wuce mu je ciki! Kuma daga yau kada na sake ganin ƙafarka a ƙofar gidan nan, matuƙar ba takardar sakinta za ka kawo mini ba!"
Tana ƙare faɗar hakan Inna Kulu ta ja ta suka yi ciki tana faɗin,
"Ke ma ki shigo ciki!"
Ko kallon su ban sake yi ba, muka shige muka bar su a ƙofar gidan tamkar ruwa ya ci su. A cikin gidan ma Inna Kulu ta daɗe tana tausar Umma sannan ta daina faɗan da take yi. Ta janyo Umma Salma da Iman da ke ta kuka ta fara rarrashin su. Haidar kam tagumi kawai ya yi hannu bibbiyu, ba tare da ya yi kuka ko ya tashi daga inda na bar shi ba.
Ni dai Umma ki yi haƙuri 😒
Manage plss!
D. AUTA CE✍🏼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*TALATIN DA TARA.*
Daren ranar haka muka kwana cikin tunanin makomar aurena da Mukhtar. Tun da safe Umma ta ce za ta je gidan ta ɗauko mana kayanmu. Na ce ta bari na nemo Sajida ta ɗauko mana duk abin da muke so.
Ba don ta so ba, na kira Sajida tare da yi mata bayanin abin da nake so ta yi mini.
"Aunty ke kina ina?"
Tambayar da ta yi mini kenan cikin sanyin murya. Ina 'yar dariya na yi mata bayanin duk abin da ya faru. "Innalillahi wa inna ilaihirraji'un! Lalle wannan lamari ya wuce tunanina. Ni kam wallahi ba da ni ba gaɗa a hurumi, don ba zan iya dambe da aljanu ba."
"Kwantar da hankalinki, babu abin da zai faru sai alheri."
"Haka ne Aunty! Amma maganin a yi kada a fara, tun yanzu ake shawara ba sai abu ya lalace ba a dawo faɗin da an sani."
"Yanzu dai ki je gidan, zan bai wa Najib makullan gidan da na ɗakina ya kai miki."
"To Aunty bari na je!"
Daga haka na kashe wayar ina kallon Haidar da ke faɗin, "Ni dai Mama da ma mun bar zuwa makarantar yau! Ni wallahi na ma gaji da zuwan ta"
"Ai kuwa ba ni auren da kai tun da ba ka son zuwa makaranta." Inna Kulu ta faɗa a lokacin da take shigowa ɗakin Ummar. Kwanon ɗimamen tuwon jiya ta ajiye mini nawa daban na su Ummu Salma daban.
"To ai kullum sai na je! Ki tambayi Mama. Yanzu kuma na gaji gaskiya! Koyaushe makaranta-makaranta dai. Jiya na je, gobe na je, jibi ma na je, don Allah Mama yau ki ce ban zuwa."
Godiya na yi wa Inna Kulu ina dariyar Haidar, saboda yadda yake lissafin! jiya ya je gobe ya je, yana lanƙwasa yatsun shi kamar mai lissafin wasu manyan kuɗi.
"To ai ba a gajiya da karatu!" Cewar Inna Kulu tana ƙoƙarin ficewa daga ɗakin. Ya ba ta amsa da cewa,
"Ni dai na gaji gaskiya!"
Wayata na cire daga caji na kira Najib, na ce ya zo ya karɓi key ya kai wa Sajida can gidan. Sannan na ajiye wayar na ja tuwona ina ci tare da Haidar. Su Ummu Salma suna cin nasu muna bitar azkar ɗin safiya da ake yi a tashar Tauraruwa. Umma ta shigo ɗauke da taliyar da ta dafa muna a tire.
Sannu da ƙoƙari na yi mata sannan na ce, "Dama ba ki wahalar da kanki dafuwar ba. Saboda tuwon nan ma zai ishe mu ni da su."
"Wahala rashi! Ni kuma ban gan ta a nan ba! Ku dai ci ku ƙoshi kawai!"
Sai da ta zauna tana rage volume ɗin tv'n sannan ta ce, "Yaran nan kamar ba za su je makaranta yau ba. Har yaushe aka ɗauko kayan? Yaushe suka shirya suka tafi?"
"Sai a tara gobe, duk da ba haka aka so ba."
Zancen da na yi kenan wanda ya sa Haidar ihun jin daɗi, har da 'yar rawarsa yana yi wa su Ummu Salma gwalo. Saboda yadda ya ga sun haɗe fuska alamun ba haka suka so ba. Najib ya kira ni ga shi ya zo, na miƙa wa Haidar makullan ya kai masa. Bayan tafiyar shi na ƙara kiran Sajida ta ce da ni ta kusa kai gidan. Saboda ita tana Gwiwa Low-cost, mu kuma muna Runjin Sambo.
Bayan mun gama cin abincin na yi wa Iman da Haidar wanka, ni ma na yi wankan sannan Umma Salma ta shiga. Ina tsaka da shafa mai Sajida ta kira ni, tana sanar da ni Mukhtar ya hana ta ɗauko kayan. Raina a ɓace na ce da ita ta jira ni zan zo da kaina tun da abin nashi babu arziƙi.
Umma ta ce "Lafiya?" Na sanar da ita abin da Sajida ta faɗa mini. Fuskarta a haɗe ta ce da ni na yi zamana ita za ta je da kanta.
"Jiyan ma mantawa na yi da ɗaukar komai shi ya sa muka fito ba ki ɗauko kayanku ba."
Tana ƙare maganar ta ja hijabinta ta fice, Allah ya tsare na ce da ita sannan na sauke ajiyar zuciya cike da jin haushin Mukhtar da tsanarsa a cikin raina.
Ban san ya aka yi ba misalin ƙarfe goma sai ga Umma da Sajida ɗauke da kayanmu niƙi-niƙi. Da fara'a na tarbe su na karɓi kayan ina yi musu sannu muka shige ɗakin Umma.
Sajida ta zauna tana faɗin, "Wash! Allah!" Yar dariya na yi mata ina buɗe jakunkunan kayanmu na ce,
"Sannu da ƙoƙari, ai kun sha aiki."
"In da ma a ce aikin ne da sauƙi. Don ba ki ga irin tataɓurzar da aka sha tsakanin Umma da Baba Mukhtar ba. Shegiyar matarsa sai leƙe take yi kai ya sha bandeji tana gulma. Ai ni yau na san na kaɗe har hanjina, saboda Baba Mukhtar har dukana ya so yi mijin maƙociyarki ne ya hana shi."
"Duka kuma!?"
Tambayar da na yi mata kenan tare da samun wurin zama na zauna, saboda labarin da take ba ni mai cike da kayan haushi da takaici.
"Duka tabbas! Ba ki ga yadda muka zagaye gidan da shi ba yana ƙoƙarin kamo ni ina gudu har ya faɗi. Lokacin da ya tashi ne na fice gidan don na san zai iya halaka ni. Babu zato na ji na faɗa jikin mutum ya yi hanzarin riƙe ni Allah ya tsare ban faɗi ba. Sai ga Baba Mukhtar ɗin da gudu, ice a hannunsa yana neman kwaɗa mini na laɓe a bayan mutumin."
"Cabɗijam! Ki ce artabu kawai kuka sha ke da shi."
Dariya ta fashe da ita sannan ta ce,
"Ai ba ni kaɗai ba har da Umma, don ita ma ba ki ga abin da ta yi masa ba. Sai da mutanen unguwar suka taru ana ba ta haƙuri. Sannan na ja ta muka shiga gidan muka kwaso kayan, munafukar matarsa sai kallon mu take yi, tana harare-harare. Na so ta tanka na rage haushinta da nake ji, don wallahi sai na darji bakinta babu ruwana da ciwon da ke kanta baƙar makira."
"Gara dai da ba ki taɓa ta ba, ko yanzu ba ki san wane irin mataki zai ɗauka a kanki ba balle kin taɓa masa amarya."
Mere ta yi sannan ta ce, "Hu'ummm! Ai wallahi komai zai yi sai dai ya yi, don ba na tsoron komai tun da gaskiya nake goyon baya ba ƙarya ba. Shi ma watarana zai yi da-na-sanin abin da ya aikata