Showing 72001 words to 75000 words out of 121208 words

Chapter 25 - ABOKIN AIKINA HAUSA NOVEL

24 Nov 2024

6400


"Hmmm! A dai ba shi haƙuri iya gobe da jibi ne kawai hutun, ranar monday tun da sassafe zan shigo har sai na riga ki zuwa."
"To shi kenan! Amma dai..."
"Ke dai me? Plss! Ki ba shi haƙuri idan kin ga da matsala kuma ki sanar da shi bikin kishiyata na tsaya yi."
Ina ƙare maganar na datse kiran, don na san halinta da jan zance ya yi tsawon da sai ta sa na je aikin dole ko ba na so.

Sajida ba ta bar gidan ba har sai da aka yi magriba, tana tare da Maman Taufiƙ suna aikin gyaran gidan. Bayan gulmar auren Mukhtar da amaryarsa da suka saka wa gaba.
Amma Mamarta da sauran waɗanda suka zo tuni suka yi gida. Ita ma don ta ƙi bin su ne ya sa suka tafi suka bar ta, bayan sun gama jefa mini magana a fakaice sanadin kujerun amarya. Da suka hau suna bitar zancen ba sabon katako ba ne. Ni kuma da bakin ƙaiƙayi na sake faɗar; a haka angon yake son kayan amayarsa mai son shi tsakani da Allah.

***
Da safe ma tun wuri Sajida ta zo da jakar kayanta na walima, saboda an ce da ƙarfe huɗu za a yi walimar. Tare da ita muka sake gyare gidan fes muka feshe shi da turaren wuta mai ƙamshi. Ƙamshin sabon fenti da na turaren ya haɗe wuri ɗaya komai tsaf-tsaf.
Sannan mai lalle ta zo aka tsantsara mana ni da ita, su Ummu Salma suka dawo su ma aka yi musu. Muna tsaka da hira Maman Taufiƙ ta shigo da ƙatuwar leda a hannunta, Sajida ta riƙo mata suka yi ɗakina. Ganin haka na yunƙura zan bi su da busasshen lallena ban wanke ba.
Sai ga sallamar wasu mata daga dangin amarya, gaisawa muka yi da su suna ƙoƙarin buɗe ɗakin na shige ɗakina na rufe. Toilet na shige kai-tsaye na wanke jam lallena da ya fito raɗau ma sha Allah!

Kayan ɗinkinmu da na hango barbaje kan gado wani sanyin daɗi ya ratsa zuciyata. Saboda tun a kallo ɗaya na hango tsaruwar da ɗinkin ya yi. Musamman na shaddodin da suka sha aiki da zare mai kyau sai ƙyallin shuwari stones suke yi.
Tawa shaddar baƙa ce aka yi wa aiki da jan zare da golden color. Sai ta su Ummu Salma mai golden ta sha aikin da ya ƙara fito da ita ma sha Allah. Ɗinkin less ɗina kuma half bubu fensil ne, wanda aka yi adon bakin lesin ta gaba da bayan rigar. Kuma aka yi wa tsaguwar tsakiyar bayan rigar adon tattara ta kwanta luf-luf saboda gugar da lesin ya sha.
Su Ummu Salma ma ɗinkin atamfarsu A.shape ne ya sha adon stone sai ƙyalli yake yi. Haidar ma aikin da aka yi masa irin zaren su Ummu Salma ne ya yi kyau sosai.
Zama na yi gefen gadon bakina har kunne muna ta aikin yaba ɗinkin da mai ɗinkin, saboda alƙwarin da ya cika bai saɓa mana ba.
Yaran ma da suka ga ɗinkin tsallen murnar suka dinga yi. Da ƙyar aka karɓi kayan hannun Haidar saboda ƙoƙarin sakawa da yake yi tun ba a yi masa wanka ba.

Ko da ƙarfe uku da rabi ta yi duka mun shirya cikin shiga ta isa ni da yarana. Mun sha ƙamshin turaruka duk inda muka motsa sai ya tashi, saboda Allah ya ƙawata mini ƙamshi a zuciyata ba na sake da turare koyaushe a jikina.
Hakan ya sa nake lalace rabin kuɗina a wurin masu turaruka, duk da faɗan da Umma take yi mini a kan na yi tanadi ko don yarana mata.

Gidanmu ya cika da 'yan'uwa da abokan arziƙina, irin su Maman Taufiƙ, Firdausi, Amina da wata maƙociyata da muke ɗan gaisawa. Saboda masu kuɗin gaske ne a cikin unguwar ba kowa take kulawa ba.
Da motarta aka yi ta ɗaukar mutane zuwa inda ake yin walimar, sai da aka kai kowa sannan ni da su Maman Taufiƙ da su Firdausi suka take mini baya.
Tun da muka fito daga motar kallo ya dawo kanmu, fuskata a sake nake kallon mutane tare da gaisawa da waɗanda ke ra'ayin gaisuwar.
Kujeru na musamman aka tanadar mana muka zauna, ina ta shan ƙamshi da jin kaina wata sarauniya a cikin bayi. Saboda kallo ɗaya da na yi wa matan wurin na raina su. Tsakanin Yayun Mukhtar mata da matan ƙannensa, tare da 'yanmatan gidansu da zawarawan duka. Sannan dangin amaryar da na gama karance muzantar da ke kan fuskokinsu.

Kasancewar ko da muka je an fara gabatar da walimar, ban samu ganin fuskar amarya ba saboda ta duƙe fuskarta cikin gyalen da ya yi wa kanta lulluɓi.
A kan ƙafarta idanuwana suka sauka babu shiri na ɗauke kaina ina basarwa. Saboda ganin baƙar ƙafar da wani mahaukacin lallen da na hango kamar an zana tsutsotsi.
Na shiga latsar wayata zuciyata cike da son ƙara kallon ƙafar amaryar Mukhtar, domin na tabbatar da abin da idanuwana suka hango mini tun a kallo ɗayan da na yi.
Bayan an gama walimar aka fara rabon ledodin takeaway. Har gabana Sajida ta ajiye mana buhu bayan ta gama raba wa danginsu nasu. Tare da sanar da ni kayanmu ne ni da mutanena.
Godiya na yi na miƙe tare da mayar da wayar a jakata ina gaisawa da mutane. Saboda nuno ni da mutane suke yi ana faɗin,

"Ga Kishiyar Barira."

Babu shiri dariya ta so suɓuce mini, saboda ganin Sajida riƙe da kafaɗar amarya tana ƙoƙarin isowa da ita inda nake.
"Aunty ga Amaryarki na kawo miki ita ku gaisa!"
Ta ƙare maganar tare da saka mini hannunta a cikin hannuna. Ido na ɗan zaro saboda ƙarfin da na ji a hannun amarya mai kama da kantar daka.

"Buɗe fuskarki amarya ku gaisa da Auntynki!"

Maman Taufiƙ ta yi maganar tare da sauke gyalen amarya domin mu ga fuskarta. Rungumo ta na yi a jikina cikin sigar duniyanci na ce,

"Ku daina kalle wa Abban su Haidar amarya...Rufe fuskarki duk mai son ya gan ki sai ya biya mu kuɗi."

Dariya aka yi duka wurin tare da ihu saboda mamakin da na bar su da shi a zuciya har muka bar wurin. Domin kuwa wasu daga cikin danginta sai da suka biyo mu har bakin mota; suna yi mini addua'r gamawa lafiya tare da zaman lafiya ni da ita da angon duka.
A cikin mota ma zancen kawai su Amina ke yi Maman Taufiƙ tana ta jinjina abin da na yi.

"Gaskiya samun irin Maman Haidar a wannan lokaci sai an tona. Cabɗijam! Ni yaushe zan iya yin irin wannan ƙarfin halin ga Kishiya?."

Firdausi tana dariya ta ce, "Ki bar ta nan da kika gan ta, ita ma ta ciki tana ciki ne fa! Amma da mun watse mun bar ta sai ta sha kukan kishin mijinta."

"Ai kuma ƙawata ba dai jarumta ba! Don ko haka da ta yi ta ci galabar yaƙin a idon amarya da danginta. Domin ni kaina nan duk da nake da kishiyar a yanzu; Allah ya gani ba zan iya yin hakan ba idan za a ƙaro mana wata." Zancen da Amina ta yi kenan tana 'yar dariyar da ta ba ni dariya ni ma.

****
A ƙofar gidanmu maƙociyar tawa ta sauke Firdausi da Amina tare da Maman Taufiƙ da Sajida. Saboda su Ummu Salma tun kafin mu baro wurin na kira Najib ya ɗauko su.
Godiya muka yi mata sosai, sannan ta shige gidanta da motarta bayan an ba ta ledar walimar. A nan Sajida ta bai wa kowa ledarsa Maman Taufiƙ ta yi mana sallama ta shige.
Firdausi da Amina saboda mazajensu za su zo ɗaukar su, tare muka yi gidan suna ta tsokana ta.
A nan ma bayan mun yi sallah wata sabuwar hira aka dasa. Sajida ta tuntsure da wata mahaukaciyar dariya tana cewa,

"Wai Aunty kin ji ƙaimon da hannunta yake yi, tamkar busassar takarda?"




Kai jama'a😂
Ni dai babu luwana🏃🏻‍♀️🏃🏻‍♀️




D.AUTA CE✍🏼


*ABOKIN AIKINA*


*@HADIZA D. AUTA*


*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*


*TALATIN DA ƊAYA.*

"Innalillahi Sajida! Lamarinki da girma fa! Shi kenan kin saka wa yarinya ido komai nata kin kushe."
Zancen da na yi kenan ina ƙoƙarin danne dariyata, saboda iskancin Sajida a kan amaryar Mukhtar ya shalle tunanina.
"Tsakani da Allah ni ma dai na raina ganin ta! Sai ka ce wanda ya hango ta idonsa rufe?" Amina ta ƙare maganar tare da tagumi, bayan jimamin da ya bayyana kan fuskarta a zahiri.
"Hmmmmm! Ni gaskiyar ma ta yi mini yawa walla..."
Kiran da ya shigo wayar Firdausi ya datse sauran maganar da ke ƙoƙarin fitowa daga bakinta.

"Yawwa! Bari na fito!"

Abin da ta faɗa kenan ta miƙe tare da saɓa jakarta a kafaɗa ta ce da mu, "To ni zan wuce, sai gobe kuma idan mun dawo tarbar amarya." Sallama su Amina suka yi mata ta fice, na raka ta har bakin ƙofa. Zuciyata a cunkushe na ce da ita,
"Wai kin san Mukhtar bai ba ni komai na faɗar kishiya ba?"
"Cabɗijam! Hmm! Ki zura masa ido kawai, don babu inda cin amana take zuwa wallahi! Ko an yi gaba sai haƙƙi ya dawo da mutum baya. Idan ban da ya rasa mafaɗi; wannan ƙazamar yarinya me zai yi da ita?"
Shiru kawai na yi saboda hawaye masu zafin da suke malala a kan fuskata. "Ki daina damar da kanki a kan Mukhtar! Na sha faɗa miki tun ba yau ba, saboda kuka bai da amfani a wurin da ba za a share maka hawaye ba. Da yardar Allah sai haƙƙinki ya fita a kan wannan auren takaicin da ya ɗebo wa kansa. Dauriyar da kike yi ki ƙara ƙaimi, domin salon takun kisa da mummuƙe ne daga kan shi har amaryar da danginsa duka. Marsiyatan banza azzalumai, marasa tsoron Allah..."
Odar da maigidanta yake yi ya sa ta fice da sauri fuskarta a haɗe cikin ƙololuwar ɓacin rai. Domin tana matuƙar jin haushin halayen Mukhtar da matsin lambar da Umma take yi mini a kansa.
Abin da na sani ne, da ace tana da iko; da tuni ta raba aurena da Mukhtar. Saboda ƙawata ce da ba na ɓoye mata komai nawa, wani lokaci ma idan ta zo gidan tana gani da idonta. A wasu lokutan baya da suka shuɗe ma; ita ce ƙashin bayan ɗauke kwatar lalurorin da Mukhtar ya bar ni da su a cikin gidansa.

Sai da motarsu ta tashi sannan na koma cikin gidan bayan na daidaita natsuwata. Shiga ta ɗakin ke da wuya Amina ta miƙe tana faɗin, "Ni ma zan tafi, ga shi can a ƙofar gida ya zo!"
Ita ma na raka ta tare da yi mata godiyar karamcin da ta yi mini. Na dawo muka dasa wata sabuwar hira da Sajida, inda take nuna zallar takaicinta a kan auren Mukhtar. Na dinga nuna mata komai nufi ne na Allah kuma babu wanda ya isa ya kauce wa ƙaddarar shi.

Bayan kowa ya yi bacci tsakanin Sajida da su Haidar, na yi shiru ina nazarin makomata ta gaba idan rayuwa ta ci gaba da shura mini a haka. Ƙarar shigowar saƙo ya sa na janyo wayata na duba, alert na yi tozali da shi wanda ya sa babu shiri na tashi zaune.
Dubu talatin na gani ɗauke da sunan MD na asali ALIYU S. NOMA, a matsayin wanda ya turo mini da kuɗin. Shiru na yi ina nazarin waɗanni irin kuɗi ne ya turo mini, saboda ban san wata ajandar da muka yi da shi ba, wadda kuɗin za su zo mini da yawa haka.
Ga shi dare ya yi ƙarfe ɗaya saura balle na nemo shi na ji kuɗin na mene ne. Shigowar wani saƙon ya sa na rarumi wayar da sauri na duba, babu shiri jikina ya yi sanyi ƙalau, saboda wani sanyin daɗi ya ratsa zuciyata.

'Ga tawa gudunmawa nan, Allah ya ba ku zaman lafiya'

Abin da na yi ta maimaitawa a zuciyata kenan, kuma na kasa ɗauke idanuwana a kan saƙon. Juya kwanciyata kawai na yi saboda ban san da wace kalma zan yi masa godiya ba.
Duk da har lokacin ban daina jin haushinsa a raina ba. Haka na yi kwanan daɗi da tunanin abin da zan yi da kuɗin idan safiya ta waye.

****
Da safe danginsa suka cika gidan ana ta hada-hadar dafa abincin bikin. Duk da na ji zafin rashin saka ni cikin hidimarsa, amma haka na danne zuciyata saboda ba na so a ga kasawa ta.
Sai dai ko kaɗan ban saka hannuna a cikin aikin ba. Abinci ma nawa na sa aka girka mini a gidan Maman Taufiƙ, da kuɗin da MD ya ba ni na yi komai a wadace.
Na shiga tarbon mutanena da ke zuwa daga dangin Ummata da waɗanda muke gaisuwar mutunci. Duk da ban yi gayya ba an yi mini kara sosai.
Wanka kala biyu na ɗauka na safe daban na marece daban, musamman shiga ta biyu da na saka baƙar shaddata kuma ɗinkin ya zauna jikina daram. Sannan na ƙawata kwalliyar da ɗan kunne da sarƙata mai kama da zinari. Don waɗanda ba su san zinarin a ido ba; kai-tsaye za su gasgata ita ce a kunne da wuyana.
Na saka gyalena ja da takalmina half shoes jajaye da wata ƙaramar jaka mahaɗinsu, bayan agogon fata baƙi da ke tsintsiyar hannuna.
Na fito sharr ina ta haske idon maƙiya tamkar sabon wata ɗan daren goma sha biyu, saboda duk inda na doso sai an lalace wurin kallona da sakakken baki. Haka ma idan na juya baya hararar 'yan hassada ta raka ni tare da cizon yatsan ba haka aka so ba; wai ƙanen miji ya fi miji kyau.
Tsakar gida muka fito ana ta ɗaukar hotuna, saboda mai hoton ma Sajida ta nace a kan sai ta nemo shi. Domin kwalliyar da muka yi kada ta tafi a iska ba tare da an bar wa bikin tarihi ba.
Muna tsaka da hotunan ni da su Ummu Salma sun saka ni tsakiya an saka mana rumfar hoton. Sai ga Mukhtar ya shigo yana baza babbar rigar shadda fara da ke sanye jikinsa. Ihu aka saka ana faɗin ga ango nan, saboda ya yi kyau gwanin burgewa don daman can bai da makusa a halittarsa.

Sajida ta isa wurin shi tana faɗin, "Don Allah Abban Haidar ka zo a yi hoton nan da kai."
Har ya yi gaba yana 'yar dariya mutane suka fara roƙonsa a kan ya zo a yi da shi, fuskarsa a washe ya zo wurinmu ya tsaya gefen Iman. Mai hoton ya ce ya dawo kusa da ni Ummu Salma a gefensa, Iman gefena Haidar ya tsaya ta gabansa.
Ma sha Allah kawai mutane suke ta faɗa saboda babu ƙarya mun ɗauki na kuti. Bayan an gama mana hoton in group aka ce ya tsaya a yi muna ni da shi, yana shan ƙamshi aka yi mana hoton yayin da na ƙawata fuskata da mayalwacin murmushi.
Ana gama ɗaukar hoton ya yi ciki ya bar mu muna ci gaba da hotunan, ba tare da ya yi mini kallon tsanaki ba balle mu haɗa ido ya ga kwalliyata. Mintuna a tsakani ya fito ya fice gidan, jim kaɗan da fitar shi wata Yayarsa ta zo kira na.

"Mukhtar ne a ƙofar gida yake so ku gaisa da abokansa."

Mayafina na ɗora a saman kai duk da ɗaurin da aka yi mini mai tozo sama. Ina gaf da fita sabon tunani ya shiga kaina, saboda burin da nake da shi a kan na ɓata masa kamar yadda yake ƙoƙarin yi mini a bikin.
Mayafin na sauke a kafaɗa, na fara taku irin na isa na doshi inda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login