Showing 78001 words to 81000 words out of 121208 words
Dariya suka fashe da ita dukansu har da shewa, na tura ƙofar ɗakina na shige ina juya maganganunsu a zuciyata.
'Waton ita ma jar wuya ce!'
Zancen da na yi kenan a raina, saboda hirar su ta bayyana wace ce ita, bayan abin da na gani zahirin da idona. Babu shiri murmushi mai sauti ya suɓuce mini saboda farincikin kafcen zai fi daɗi a hakan.
Wayata na cire daga caji na tura wa MD saƙon godiya, saboda rashin kyautawata ban yi godiya tun da zafi ba. Abin yana ta cizon raina, sai da na tura masa saƙon sannan na ji tamkar an sauke mini ƙaton dutsi a saman kaina.
'Na ga saƙo na gode sosai! Ubangiji ya ƙara buɗi da rufin asiri'
Mintuna a tsakani ya dawo mini da 'Amin' kawai ba tare da ya ƙara komai a kai ba. Haushi na ji na goge saƙon duka, sannan na mayar da wayar a caji.
Ban san ya aka ƙarge ba tsakanin amarya da angonta ba, balle marasa kunyar ƙawayenta. A cikin bacci na jiyo sautin muryar Barira tare da bugun ƙofar ɗaki, na so kada na bi ta kai don ban san kalar rainin wayon da suka shirya ba.
Amma haƙƙin zamantakewa ya sa na miƙe na buɗe ɗakina na fito, hango ta na yi a bakin ɗakin Mukhtar tana ta dukan ƙofar tare da kiran sunansa.
Da sauri na juya da nufin komawa na ji muryarta ɗauke da damuwa tana cewa,
"Aunty don Allah ki ce ya zo ya buɗe ƙofa, tun yamma da ya shige bai sake fitowa ba. Ga shi ba ya jin daɗin jikinsa kuma ya dace mu san a wane hali yake ciki."
Murmushi kawai na yi, sannan na ƙaraso bakin ɗakin na fara kiran sunansa. Kamar jira yake yi ya buɗe ƙofar a fusace yana faɗin,
"Kun fa dami mutane cikin dare, ko ku ba ku san dare mahutar bawa ba ne?"
Dariyata na ƙumshe sannan na ce da shi, "Amarya ce ke neman sanin halin da kake ciki. Shi ya sa na ga ya dace na taya ta neman ka saboda haƙƙin zamantakewa."
"To lafiyata ƙalau ku je ku kwanta! Don ba na jin ƙarfin jikina ne shi ya sa ban fito ba. Tun da kun gan ni ku je ku kwanta kawai sai da safe!."
Na juya ina 'yar dariya na ce da su, "Mu tashi lafiya."
"Me za ki yi a nan ke kuma? Wuce ɗakinki ki kwanta ko'ina jikina ciwo yake yi wallahi."
Maganarsa kenan da na jiyo kafin na isa ɗakina, 'Garam!' Na ji ya rufe ɗakinsa da ƙarfi. Sai da na shiga zan rufe ƙofata na hango Barira a bakin ɗakin tamkar an dasa ta.
Dariya ta suɓuce mini na yi hanzarin rufe ɗakin, raina fes na koma kan gadona na kwanta ina jin kaina cikin nishaɗi.
Bacci mai daɗi na yi tare da mafarkin MD a cikin wani kyakkyawan yanayi. Rungume nake a jikinsa, hannunsa cikin nawa yana yi mini raɗa a kunne ina ta faman murmushi. Fuskarsa ɗauke da annuri yana fesa mini siririyar dariyar da ta ƙara wa fuskarsa annuri.
'Ina sonki da yawa matata!'
Rufe fuskata na yi tare da lakuce masa karen hanci, kiss ya yi mini a goshi cikin shauƙin ƙauna yana aika mini kallon da da ya haifar mini da kasala. Ya rungume ni gabaɗaya a jikinsa, sannan ya sauke ƙaƙƙarfar ajiyar zuciya mai sauti 'Hummmmmm!' Luf na yi cikin jikinsa numfashina yana fita a hankali cikin wani yanayi mai daɗi.
Kiran sallar asuba ya katse mini daddaɗan mafarkin da na yi, wanda na so na ɗore da shi a hakan ba tare da na farka ba. Jikina ko kaɗan babu kuzari, a haka na yi sallah na tayar da yaran sannan na fito ɗaki da nufin zuwa kitchen.
Turus na yi saboda hango Barira a yashe ƙofar ɗakin Mukhtar, rigar barcin da ke jikinta gabaɗaya ta kware cinyoyinta a buɗe.
"Ita kuma wannan me ya same ta?"
To fa😱 amaryar Romiyo ya take ne?😂
D. AUTA CE✍🏼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*Ina ƙara tunatarwa!Ban yarda ba! Ban amince ba! Kada a ɗora mini littafi YouTube ba tare da izina na ba! Masu nema daga farko ku yi haƙuri har a kammala🙏*
*TALATIN DA UKU.*
Tambayar da na yi wa kaina kenan a zuciya, sannan na yi tattaki a hankali har na isa inda take. Sunanta na fara kira domin alamu ya nuna mini ƙarara bacci take yi sharkaf!
Ba ta motsa ba har sai da na duƙa na bugi hannunta tare faɗin, "Barira!"
Ta miƙe firgigit tana waige-waige tare da faɗin, "Don Allah Romiyo ka buɗe mini ƙofar"
"Lafiya kike kuwa?"
Na faɗi maganar cike da jin haushin banzancin da take ƙoƙarin yi wa kanta. Kallo ta bi ni da shi sannan ta yi hanzarin miƙewa tana gyara zaman rigar barcin da ke jikinta. Soshe-soshen kai ta fara yi tana mayar da hularta bisa kai, ta nufi hanyar ɗakinta ranta a haɗe cikin maƙoshi ta ce da ni,
"Lafiya lau!"
Bayanta na bi da kallo har ta shige ɗakinta ta rufe, murmushi na yi tare da girgiza kaina ina maimata sunan Romiyon a raina, wanda ta raɗa wa Mukhtar ba tare da ta san bai cancanta da sunan ba. Domin bai san komai a kan soyayya ba balle abin da ta ƙumsa, saboda iya sanin da na yi a rayuwar zamana da shi; ko kiss irin na haɗuwar leɓe da leɓe bai taɓa haɗa ni da shi ba.
Kitchen na koma ina ta hada-hadar ɗora mana abin kari. Zuciyata cike da tunanin rashin kawaici irin na Barira, da rashin sanin darajar Mukhtar balle ya sauke haƙƙoƙan da ke kansa.
Kasancewar muna da sauran kayan tea na soya mana Irish da ƙwai. Ina ƙoƙarin fitowa daga Kitchen ɗin hannuna ɗauke da cups da flack's, na ji sautin muryar Barira a sama tana masifa.
"Na rantse da Allah sai ka san ni ka wulaƙanta. Babu wata magana da za ka faɗa mini yanzu na yarda, saboda ni ma ba ka ji kalolin kiran da na yi maka ba amma ka ƙi buɗe mini ƙofa."
Abin da na ji kenan bayan na fito daga Kitchen ɗin, saman carpet ɗin tsakiyar kujeruna na ajiye kayan sannan na ƙwala wa su Ummu Salma kira. Duk da ina jin sautin Mukhtar ƙasa-ƙasa yana magana amma ban ji me yake cewa ba.
Fitowar su Ummu Salma ta yi daidai da fitowar Barira a fusace ta nufi kitchen. Mukhtar ya bi ta yana kiran sunanta cikin ƙaramar murya kafin ya rufe ƙofar.
Baki a sake yaran suke bin ƙofar kitchen da kallo, karantar da na yi wa fuskokinsu na gano mamakin da suke yi. Murmushi na yi mai sauti na miƙe daga durƙushen da nake ina faɗin,
"Ku bari na kawo muku madarar"
Kitchen ɗin na nufa na tura ƙofar, cikin sa'a bai rufe da makulli ba. Kai-tsaye na nufi kular da na saka soyayyen Irish ɗin, duk da na tarar da kular a buɗe Barira tsaye tana ci a cikin plate ɗin da ta shaƙe taf! Ba tare da ta jira na ba ta ba, ko kuma ta tuna da cewa akwai wasu masu haƙƙi da shi a cikin gidan bayan ita.
Sai girgiza ƙafafuwa take yi tana cin abinta shi kuma yana faman yi mata magiya. Na so na yi magana, sai na ga duk abin da zan faɗa a lokacin zai janyo wani sabon tashin hankali a tsakanina da ita.
Kular kawai na ɗauke sannan na ja biredi, wanda shi ma ta fasa ledar ta bar shi a buɗe, na fice ba tare da na ce da su komai. Raina a ɓace na dire kular na koma na ɗauko tire na kasa musu kowa ya ɗauki na shi.
Zuciyata a ƙuntace saboda mummunan ganin da na yi musu a kitchen ɗin. Sai da yaran suka cinye sannan na ce da su,
"Oya ku tashi ku je islamiyya kada ku yi latti"
Suka ɗauko jakunkunansu suka wuce, na bi su da addu'ar a dowa lafiya sannan na karya. Na kasa tashi daga wurin na baje saman 3seater tare da rufe idona kamar mai barci, sai hotonsu nake gani a lokacin da suke shagalinsu.
"Ina nawa breakfast?"
Zancen Mukhtar da na ji kenan cikin tsakiyar kwanyata, ban motsa ba kamar yadda ban yi niyyar amsa masa ba.
"Da ke fa nake magana!"
Ya sake maimaitawa a fusace cikin ɗaga murya, gyara kwanciyata na yi ba tare da na ce ƙanzil ba.
"Ni za ki wulaƙanta ina yi miki magana kina sharewa?"
"Wane breakfast zan ba ka bayan wanda ka yi a kitchen?"
"Haƙƙina ne aka ba ni a can, wannan kuma shi kike da haƙƙin bayarwa"
Wani ɓacin rai ya taso mini, nan take ya yi mini lulluɓin da ya rufe mini idon gani, domin ban san lokacin da na diro daga kan kujerar ba ina faɗin,
"An canye haƙƙin ko kana da abin da za ka yi ne idan an hana ka!?"
"Kwantas Hajiya! Ai kuma yanzu babu kare bin damo! Ki yi yadda kike so ni ma na yi nawa."
Yana ƙare faɗar hakan Barira ta fito daga kitchen ɗin sum-sum tamkar munafuka ta shige ɗakinta. Harara na wurga masa saboda kallon da ya bi ta da shi yana 'yar dariya. Na danna masa wani kafurin tsaki har sai da na dantse naman ƙasan leɓena. Sannan na bar wurin ina ƙoƙarin shigewa ɗakina ya ce,
"Sai haƙuri kuma, ni kam na samu inda aka san muhimmancina."
Baya na dawo saboda ganin idan na yi masa banza bai san kawaici ba,
"Bari na faɗa maka zancen da ba ya tashi! Wallahi daga wannan karin safiyar; ba zan sake yi mata girki ba. Tun da ta san muhimmancinka ta girka ta ba ka ka ci kai da yaranka."
"Hahahahahh!"
Sautin dariyar da ya yi kenan har da buga ƙafa ƙasa, sannan ya yage baki yana ƙwala mata kira cikin ɗaga murya.
"Barcy!!!"
"Na'am Romiyo!"
Barira ta fito daga ɗakinta cikin sauri ta iso wurinsa da gudu, towel ɗaure a faƙon ƙirjinta da babu tudun komai face na fatar da ke jikinta.
"Ki shirya yi mana girkin rana ni da yarana. Zan aiko miki da kayan cefane idan an dafa a zuba wa Uwargida nata."
Tana fari da ido ta ce, "Haba Aunty! Me ya yi zafi ne haka tsakaninki da Romiyo?"
Baki a sake na dinga kallonsu ɗaya bayan ɗaya, maimakon na ji raina ya ci gaba da suya; sai na ji wata dariya ta suɓuce mini ban shirya ba. Sannan na gyara tsayuwata na ce da ita,
"To ke Barcy ina ke ina sanin sirrin mata da mijinta? Yana da kyau ki tsaya inda kike da iko da inda ya ajiye ki, ki daina ƙoƙarin shiga hurumin da ba naki ba har sai an kasa da ke. Girki dai ne ya ce ki shirya yi mana saboda yana so na huta da aikin da na sha haka nan, domin tun da aka fara shagalin bikin aurenku ban zauna ba, kullum ina tsaye tamkar haƙori. Don haka idan kin gama ki zuba mana namu a kula ni da yaransa, kamar yadda ya faɗa miki."
Ina ƙare maganar na juya ba tare da na damu da kallon tuhumar da take aika masa ba. Na je ƙofar ɗakina na ja na tsaya rungume da hannuwa a ƙirji ina musmushin mugunta.
"Wallahi ba haka muka yi da ita ba Allah ma ya sani."
Maganar da ya yi kenan yana ɗaga manunansa duka biyu a ƙoƙarin son ta yarda da zancen shi.
"Daina rantsuwa zan yi girkin kamar yadda ka saka ni, amma wallahi sai ka biya duk wata wahalar da na sha yau."
Ɗakinta ta nufa karaf ta dantse ƙofar, ya fara aiko mini da harara yana nuna ni da hannu yana cewa,
"Ko shaiɗan sai ya shafa miki lafiya a wurin ibilisanci. Don haka ki je kawai akwai Allah!"
Dariya na fashe da ita sannan na yi masa gwalo, ƙwafa kawai ya yi sannan ya tsaya bakin ƙofarta yana faɗin,
"Ki yarda da ni Barcy! Wallahi ba haka muka yi da ita ba."
****
Tun da na shige ɗaki ban sake fitowa ba, sai da su Ummu Salma suka dawo na ce su je su yi wanke-wanke. Bayan na yi wanka na haye gado ina ta faman chatting da na gaji na koma kallo har bacci mai ƙarfi ya yi awon gaba da ni.
Ƙarfe uku lis na fito ɗakin, saboda hayaniyar faɗan da yaran suke yi. Kokawa sosai suke suna dambacewa tsakanin Haidar da Iman, Ummu Salma tana raba su Haidar bai bari. Ganin Barira a kan kujerarta zaune tana latsar waya ko a jikinta; hakan ya sa na ji raina ya ɓace.
Fakar Haidar na yi cikin fushi na fara yi masa faɗa sannan na dawo kan Iman. Ummu Salma ce ta fara yi mini bayanin abin da ya haɗa su faɗan.
"Wai don ba a ba mu abinci muka ci ba, shi ne ya ce dole sai ya je ya ɗauko. Kuma amarya ba ta ce mu ɗauko ba, ta ce mu jira har Abbanmu ya dawo shi ya ce zai ba mu."
"Ban gane ba! An gama abincin shi ne ba za a ba ku ba sai ya dawo ya ba ku?"
Ummu Salma ta ɗaga kai alamun tabbatarwa,
"To ai shi ne zan je na ɗauko mana mu ci Iman tana riƙe ni. Ni Ko da na gaji haushi na dinga kai mata duka, daga nan muka fara kokawa."
Kitchen kawai na nufa ba tare da na ce da su komai ba balle Barirar, kulolin da na gani ajiye na fara buɗewa. Shinkafa da miya na gani a cikin kuloli biyu, ban tsaya neman bayani a kansu ba na ɗauki wadda ta fi girma na fice.
Ina tsaka da zuba musu abincin na ji muryar ta a saman kaina tana faɗin,
"Kan ubancan! Abincin Romiyo kike zuba musu?"
Ban fasa juye musu abincin a tire ba, na bi abincin da miya tare da zuƙa-zuƙan namun da na gani duk na juye musu. Ina ƙoƙarin tura musu gabansu ta fara faɗin,
"Gaskiya Aunty wallahi ba ki kyauta mini ba! Saboda Allah yaushe zan yi wa mijina girki ki zube wa yara su cinye?"
"Abincin daga gidanku kika zo da shi ne? Ina ga ai har yanzu ba a kawo miki kayan garar da ake kai wa kowace amarya ba. Ki jira idan aka kawo ki yi iko da abin ki, amma wannan ba ki da halin hana wa yara abincinsu. Domin ubansu ya sayi shinkafar kuma shi ya yi cefanen da aka yi gurkin."
"Haka ma za ki ce?"
"E, haka na ce!"
Kuka ta fashe da shi wiwi tamkar wadda aka daka, saboda sallamar da Mukhtar ya yi tun kafin ya shigo falon. Wurinsa ta yi da gudu ta faɗa jikinsa tana rera sani sabon kukan, a ruɗe ya fara tambayar,
"Lafiya? Me aka yi mata?"
Kallo ma bai ishe ni ba, na zauna ina faɗin su yi sauri su gama su tafi. Isowa ya yi wurinmu tare da ita a jikinsa yana faɗin,
"Wai me yake faruwa ne!?"