Showing 90001 words to 93000 words out of 121208 words

Chapter 31 - ABOKIN AIKINA HAUSA NOVEL

24 Nov 2024

6423

ko ba kya so."

"Wane Aminun!!?"

Zancen Maman Taufiƙ kenan cikin muryar tashin hankali, a lokacin da take shigowa gidan idonta a kan Yaya Maimuna.

"Aminu na ji kina faɗa!"

"Ko ma dai wane ne ba ku isa ku hana abin da Allah ya ƙaddara ba"

Tambaya Maman Taufiƙ kenan da amsar Yaya Maimuna a lokaci ɗaya. Jikina yana rawa na ja Maman Taufiƙ muka shige ciki ina faɗin,
"Ba da ke suke ba ni aka zo yi wa takakkiya. Ni kuma a yanzu daidai nake da kowa tun da abin nasu babu mutunci balle kawaici."
"Wai har na ji sanyi wallahi. Ba ki ji yadda ƙirjina ya buga ba a lokacin da na ji ta kira sunan Amini.."
Zama muka yi a kan kujera tana faɗin, "Ita Sajida aure za ta yi ne?"

"E, kuma ba ta son mutumin."

"Kuma shi ne za a zo wurinki takakkiya miye naki a ciki?"

"Su dai suka sani."

"Hayaniya na ji shi ya sa na zo na gani lafiya? Ashe Mamarta ce take abin da ta saba. Ni na rasa laifin me kika yi wa wannan matar da ta saka ki gaba irin haka."

"Mijinki ake so a manna wa Sajida ba ki da labari."
Maganar Barira kenan da muka jiyo daga ni har Maman Taufiƙa saman kanmu.

"Mijina kuma?"

"E, shi! Kuma babu mai son ta ga auren nan ya ƙullu face wadda kuke zaune da ita yanzu. Don a gabana take saka Sajida ta manne wa mijinki, domin kawai ta ga ƙarshen kishinki."

"Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun!"

Ita ce kalmar da muka haɗa baki wurin faɗa ni da Maman Taufiƙ, tare da miƙewa tsaye dukanmu muna kallon Barira.

"To wasa ce nake yi! Ku yi haƙuri don Allah kada ku cinye ni da raina."





Barcy lamarinki sai ke 🤔😂






D. AUTA CE✍🏼


*ABOKIN AIKINA*


*@HADIZA D. AUTA*


*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*


*TALATIN DA BAKWAI.*

Ban san ya aka yi ba, sai hango Maman Taufiƙ na yi maƙare da wuyan Barira tana kakarin mutuwa. Cikin wani sabon tashin hankali na yi kansu ina ƙoƙarin ɓanɓare hannun Maman Taufiƙ, daga muguwar shaƙar da ta yi wa Barira. Wadda azaba ta sa ta gwalalo ido waje gulu-gulu tamkar idanun mota.
Ganin ba zan iya ni kaɗai ba na fasa ihu saboda gabaɗaya sun fita hayyacinsu, tamkar wasu sababbin halitta. Mukhtar ya iso wurin a ɗari yana faɗin,

"Innalillahi wa inna ilaihirraji'un!"

Ya ja Barira na samu na ƙwace hannun Mama Taufiƙ, sai dai hakan bai yi mata ba ta koma ta cafko ta iya ƙarfinta. Mukhtar ya yi hanzarin ture ta gefe ta faɗi sannan ya rungume Barira yana ƙwala mata kira a haukace, saboda alamunsa ya nuna tsantsar kiɗima da ruɗewar da ya shiga. Ganin halin da Barira take ciki riƙe da wuyanta tana juye-juye tare da kakari a lokaci ɗaya.
Domin a kallo ɗaya za a kira shi da kakarin mutuwa saboda shure-shuren da take yi. Maman Taufiƙ kuma ta baje ƙasa tana gumza tamkar wata raƙuma. Bayan furzar da yawun da take yi yana baltsi a kan fuskarta.
Ruwa na ɗebo da gudu na dawo a firgice saboda na gama kai wa ƙololuwar ruɗewa. Sai dai tun kafin na iso na hango ta zabura tamkar wata zakanya ta yi kan Mukhtar da ke rungume da Barira.
Cakumo shi ta yi ta wurgar gefe tamkar a cikin shirin horror, sannan ta fisgo tsorayen Barira sai ga ta da su a hannu ta jefar ƙasa.
Kukan kura na yi tamkar wata ifirituwa na kai wa Maman Taufiƙ raruma ta baya. Saboda ƙoƙarin fisgo wasu tsorayen da take yi ta sauke su ƙasa kamar yadda ta yi wa na farkon. Kokawa muka shiga da ita tsakiyar falon tana so na sake ta ina damƙe ta iya ƙarfina. Tun muna faɗawa kujeru har muka faɗi ƙasa a tare muna mulmula tamkar wasu macizai.
Addu'a na dinga karanta mata a bakina cikin sauti tun tana fisge-fisgen har ta yi luf! Na ci gaba da karanta mata surorin tsari da kore shaiɗanun aljanu. Saboda na gamsu da cewa ba ta cikin hayyacinta balle hankalin kanta, shi ya sa take ƙoƙarin aikata aika-aikar da dukanmu sai mun yi da-na-sani.

Ganin ta lafa na hango Mukhtar ya nufi inda Barira da jini ya gama wanke mata jiki kaca-kaca. Ihu ya yi tare da kinkimarta tamkar 'yar tsana ya fice da gudu yana faman kiran sunanta.
Fitar su da ɗan lokaci na saki Maman Taufiƙ na miƙe ina kiran sunanta tare bubbuga jikinta. Firgigit ta miƙe idonta a zare sun yi jawur tana ƙare wa falon kallo, tamkar wadda aka bai wa aikin ƙididdige abin da ke cikin falon duka.

Hannunta na riƙa ta miƙe tana kakkaɓe kayan jikinta ta ce,
"Me ya kawo ni gidan nan?"
Fuskata ɗauke da mamaki na ce, "Kina nufin ba ki ma san kin zo gidan ba?" Na ƙare maganar tare da zuba mata idanuwa domin na tantance ita ce ko sarakan aljanunta masu neman ɗaukar rai.
"Wallahi Maman Haidar ban san na zo gidan nan ba! Iya abin da kawai zan ƙaras tuƙin tuwon da nake yi a kitchen.

"Cabɗijam! To mu je na raka ki gida kada ya ƙone a yi biyu babu"

Hijabinta na mayar mata sannan takalminta na ja nawa hijabin muka nufi gidanta. Abin mamaki tun a ƙofar gidan na fara jiyo ƙaurin ƙonewar shinkafa. Da sauri na sake ta na yi kitchen ɗinta da gudu na saukar da tukunyar tuwon. Wadda ta turnuƙe Kitchen ɗin da hayaƙi ko gabana da ƙyar na gani, har na samu sararin sauke tukunyar a kan gawayin da take girkin da shi.
Na fito ina tari tamkar na shiɗe, saboda ulcer ta ko kaɗan ba ta buƙatar hayaƙi. Dalilin da ya sa na daina aiki da komai sai gass, duk da a lokacin da na saye shi ba ƙaramar rigima muka yi da Mukhtar ba. Saboda ya buga kansa a ƙasa shi ba zai iya wahalar shi ba, na ce masa na ji na ɗauka ni zan ɗauki nauyin komai ko don lafiyata.

Gida na koma na rufe, sannan na dawo na kankare tuwon da fiye da rabinsa ya gama ƙonewa. A gurguje na canza tukunya na ɗora mata wani sabon tuwon, ganin garin semo a buhu ya sa na fara talga tuwon na rufe. Sannan na fito na nufi ƙofar gidan saboda sallamar da na ji Mukhtar yana bugawa.
Hankalina a tashe na isa ina tambayar shi Barira da halin da take ciki, harara ya kwaɗa mini tamkar idonsa su faɗo ya ce,
"Ba ni makulli!"

Na ciro daga aljihun riga ta na miƙa masa ya wuce fuu, duk da alhinin da nake ciki sai da na tuno lokacin da aka jefar da shi ƙasa ya yi zaman 'yan bori. Bayan ya fasa ƙara tare da faɗin,

"Wayyo Allahna uwata!!!!"

Komawa ciki na yi ina 'yar dariya har tuwon ya yi na kwashe mata, a ledodin da na gani an gama buɗewa. Sannan na kashe gawayin na tafi falonta ina kiran sunanta, hango ta da na yi a kan kujera 3seater tana bacci sharkaf. Hakan ya sa na ji wani sanyin daɗi ya ratsa zuciyata.

Ficewa na yi gidan ina ƙoƙarin shigewa gida na hango motar Baban Taufiƙ ya doso. Na dawo baya jikina yana tsuma na isa inda ya yi parking motarsa yana ƙoƙarin fitowa.

"Don Allah! Wata alfarma na zo wurinka a kanta. Na san kana son Sajida, amma ka taimaki rayuwaka da yawa ka janye wannan maganar!"

Tsayuwarsa ya gyara sannan cikin murmushi ya ce da ni, "Allah fa bai haramta mini ba, don haka ban ga abin tashin hankali a cikin lamarin ba. Idan ma matsalar Aminiya ne ku bar komai a hannuna na san yadda zan tafiyar da ita har ta amince."

"Ba za ta amince ba! Don yanzu haka da ƙyar amaryar Mukhtar ta sha a hannunta. Saboda ta yi gangancin sanar da ita shi ne ta shaƙe ta har da cire mata tsoro uku."

"Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun! Me ya sa ba ku nemo ni tun wuri ba?"

"Share da ita kawai duk ita ce ta ƙulla komai! Kuma ko za ta mutu wallahi ban ce ka janye ƙudurinka ba! Ita kuma Barira; ki sani duk abin da aka yi mata danginta suna tafe gun ki, domin su ɗaukar mata fansa a kan abin da kika sa aka yi mata."

Hannuna na rungume a ƙirji bakina yana rawa na ce, "Idan har sun fasa zuwa Allah ya tsine musu albarka. Idan sun zo ka ce kada su bar ni da raina tun da kai ba ka taɓa sanin mene ne adalci ba!"

"Haka kika ce!?"

"Haka na ce!"

Ina ƙare maganar na kai kallona a kan Baban Taufiƙ cikin matsancin fushi na ce,
"Ko ka janye zancen auren nan! Ko ka yi sanadin salwantar rayuwaka da yawa, ciki kuma har da kai idan ka nace wa abin tun da ku maza ba za ku damu da damuwar mace ba; muddin kuna son faranta wa zukatanku babu ruwanku."

Ina gama faɗar hakan na yi cikin gida da sauri tamkar zan tashi sama saboda tsananin ɓacin ran da nake ciki.

Ummata na kira a waya bayan na saita kaina na ce, "Su Ummu Salma su kwana a can, saboda gidan babu kwanciyar hankali."

"Me ya faru!?"

Ta jefo mini tambayar cikin sauri tare da ɗaga murya.
"Mijin Maman Taufiƙ ne yake son auren Sajida, shi ne Mukhtar da Yaya Maimuna da amaryarsa suke ƙoƙarin haɗa mini tuggu a wurinta. Garin tsegumtawa Maman Taufiƙ da Amaryar tasa ta yi ƙoƙarin yi. Ta shaƙe ta har da cire mata tsoro uku, kuma Mukhtar ya ƙi tsayawa na yi masa bayanin yadda abin yake. Sai sanar da ni yake yi dangin amaryar za su zo su ɗauki fansa kaina."

"Innalillahi wa inna ilaihirraji'un! To ki dawo gida kawai tun kafin hakan ta kasance. Don wallahi duk uban da ya taɓa ki a faɗin garin nan sai na nuna masa kina da gatanki. Shi kuma Mukhtar ki bar ni da shi zan ci uban shi a wannan gaɓar."
"Kwantar da hankalinki Umma, wallahi babu inda zan je! Don za su zargi tsoro ne ya sa ni guduwa."

"To ki jira ni gani nan zuwa yanzu!"

Tana ƙare maganar ra kashe wayar, wanka na sake yi saboda gabaɗaya jikina ciwo yake yi. Domin ba ƙaramin gumurzu na yi da aljanun Maman Taufiƙ ba, don ni kaina ban san ina da irin wannan ƙarfin halin ba sai a lokacin.

Ina ƙare sallar magrib ko tashi ban yi daga kan sallaya ba, na fara jiyo sautin mata da maza suna aiko mini zagi tare da faɗin ina nake na fito.
Tsam na miƙe na fito cikin jarumta kamar yadda suke umurta ta, sai da na rufe ɗakina da makulli sannan na fara faɗin,

"Ga ni ta nan! Idan akwai abin da za ku yi mini; don Allah kada ku bar ni da raina!"

Wani matashin saurayin da a kallo ɗaya na gano ɗan daba ne, ya fara buga zabgegiyar bulalar da ke hannunsa ƙasa yana faɗin,

"Jarkutumar babakeren alllin karmatakon..."

Ya ƙare da lailayo wata uwar ashariya ya sauke mini, tare da yin ihu yana ƙoƙarin kai mini duka aka rirriƙe shi. Ya fara yunƙurin kufce taron dangin riƙon da suka yi masa, yana ta zillo domin ya dake ni.
Sai ga jiniyar 'yansanda wiwi tamkar unguwar za ta tashi, saboda dirin motocin da na ji har cikin gidan. Mintuna a tsakani sai harbi muka jiyo.

'Ɗwa-ɗwa!!'

Babu shiri dukansu suka fara ihu tare da gude-guden neman maɓoya. Rungume hannuwa na yi a ƙirji ina yar dariyar mugunta tare da komawa cikin kujeruna na hakimce.
Sai ga ɗan wiwin ya zo kusa da ni yana dafa tafin ƙafata, tare da duƙar da ƙansa ƙasa yana faɗin,

"Don Allah ki yi mini rai! Wallahi ko sati ban yi ba da dawowa kurkuku. Idan na koma ban san loakacin da zan fito ba!"

Ƙafa na saka na kai masa harbi a muƙamuƙi, ya yi saurin dafe gefen bakinsa yana muzurai. Fuskata a haɗe na ce da shi,
"Gara ka koma can ka ci gaba da rayuwa don har yanzu ba ka san Annabi ya faku ba!"


Ummata na ga ta shigo gaba 'yansandan a bayanta fuskarta a cure cikin takun taƙama. Sannan ta ja ta tsaya inda nake tana dudduba kujerun jikina, wanda kai-tsaye na gano raunin da take zaton sun yi mini take dubawa.
Ganin ina murmushin ƙarfin hali har da gaishe ta, hakan ya sa ta ce,
"Alhmdulillah!"

Sannan ta juya wurin 'yansandan tana faɗin, "Ofisa! A tafi da su dukansu har matan babu wanda za ku bari!"

Haka aka dinga tasa ƙeyarsu ana dukan ɗuwawunsu da kan bindiga har aka fice da su dukansu. Sannan Umma ta sauke ajiyar zuciya ta ce da ni,

"Tashi mu je gida!"

Kallonta na dinga yi kamar ba ita ba, saboda umurnin da take ba ni a kan mu je gida tamkar almara.
Domin wannan ne karo na biyu da ta ba ni umurnin zuwa gida da kanta ba tare da na nema ba. Na farko lokacin da Mukhtar ya faɗa wa danginsa da mutanen unguwar na ce sai na kashe shi, ko na kashe kaina idan bai sake ni ba.

Tana gaba ina bayanta muka fice gidan, adaidaitar da ta zo da ita muka shiga. Bayan Yansandan sun tafi da dangin Barira. Sai dai har muka je gidan Kawu Sale ba ta sake cewa da ni komai ba.
Domin na fahimci fushinta ya gama kai wa maƙurar, tun daga fuskarta da yanayin iskan da take furzarwa. Bayan ajiyar zuciyar da take saukewa lokaci bayan lokaci.








Manage plss😢 ni da yarona duka babu lafiya.





D. AUTA CE✍🏼


*ABOKIN AIKINA*


*@HADIZA D. AUTA*


*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*


*Alhamdullah! Jiki da sauƙi. Na gode sosai da addu'o'inku. Allah ya saka da alheri. Luv u all😘*


*TALATIN DA TAKWAS.*

Shiga muka yi gidan tare da Umma tana gaba ina bayanta, yaran suka zo da gudu suna murnar gani na. Rungume ni suka yi dukansu tare da faɗin,
"Oyoyo Mama!"
Babu shiri na yi hanzarin shanye ƙwallar tausayin su da ta cika mini ido. Saboda har kullum ina tausaya musu a raina, a kan zaɓen tumun daren da na yi musu, wurin nemar musu kamilin uba kuma majinginarsu. Inna Kulu ta fara tsokanar su da cewa,
"Lalle ɗan aro ba ɗa ne ba, waton saboda ganin uwarku har kuna ƙoƙarin ture Kakarku. To ke Habi ki san zaman da kike yi da su, duk wani daɗin bakin da suke yi miki na rashin ganin ta ne a kusa da su.
"Kai Inna Kulu! Kada ki haɗa mu da Umma, ki sa gobe ta ce ba za ta yi mana ɗan malele ba."

Abin da Ummu Salma ta faɗa kenan tana dariya tare da tsalle tana son rufe wa Inna Kulu baki, a kan ta yi shiru.
"Daina rufe mini baki sai na faɗi gaskiya."

"To ai muna son Umma ita ma ta sani."

Haidar ya faɗa yana wata tafiyar gayu hannuwansa duka a aljihu. Daga ni har Inna Kulu dariya muka yi, saboda har da doro yake haɗawa yayin tafiyar yana jefa ƙafa tamkar wani sabon gurgu.
Duk abin da muke yi Umma tana cikin ɗakinta ba tare da ta ce da mu komai ba.
Inna Kulu ta shimfiɗa mini tabarma a tsakar gidan na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login