Showing 87001 words to 90000 words out of 121208 words
da su a cikin ɗakin. Bayan sallar Isha muka koma falo muna kallo, Barira ma tana ta wayoyinta da mutane tana shewa. Bayan zagin da take kamfatowa iri-iri tana sauke wa ƙawayenta.
"Ke shegiya! Gobe ki zo akwai sabuwar chepter...Sosai ma ke dai ki zo kawai akwai labarai...Yawwa 'yar gari ki zo da kayan duka mu ɗan kora an kwana biyu ba a haɗu ba."
Maganganunta sun saka jikina sanyi, saboda tunanin yarana da za su dawo ba na gidan. Kai-tsaye wata sabuwar idea ta zo mini, na yanke hukuncin tura su wurin Ummata goben. Gudun na taras da tashin hankalin da ya fi na yau, kuma ba zan juri rainin hankalin kowa ba a kan yarana.
Matsayar da na kai kenan wadda kuma na kwana da ita a cikin raina. Da kayansu na fita na miƙa wa Najib tare da yi masa kwatancen gidan Kawu Sale, sannan muka rabu da zummar idan aka tashi ya kai su gidan. Zuciyata wasai saboda ganin na kashe gobarar da take ƙoƙarin tashi ta ƙone zuciyata da ta yarana.
Hmmmmm! Akwai badaƙala fa!🥲
D. AUTA CE✍🏼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*TALATIN DA SHIDA.*
Zuciyata ɗauke da tunanin wace irin waina ce Barira take ƙoƙarin toyawa ita da ƙawayenta. Har na kammala aikina na miƙe na fito offis ɗin, saboda Amina ba ta zo ofishina kamar yadda ta saba ba.
Ɓangaren su na nufa cike da burin na gan ta domin na sanar da ita rikicin da ke ƙoƙarin ruftawa da ni. Wanda nake ji a raina muddin Baban Taufiƙ ya nace da son auren Sajida; tamkar ya saka takobi mai kaifi ya datse alaƙar da ke tsakanina da matarsa.
Saboda duk abin da zan faɗa mata ba zai goge kallon da za ta yi mini ba. Samun ta na yi cikin 'yan ofishin su suna ta hira, gani na ya sa ta miƙe tana faɗin,
"Yanzu nake son na je hirar Sara ya riƙe ni."
Gaisawa muka fara yi da mutanen sannan na fito Amina ta biyo ni, wuri muka samu muka zauna Amina ta fara faɗin,
"Duk abin da mutum yake yi a ɓoye, watarana sai Allah ya tona masa asiri. Ka yi alheri ma ya ka ƙare balle ka ce ɗan akuya za ka mayar da kanka?"
"Me ya faru da Sarar ne?"
Tambayar da na cillo mata kenan, saboda ina so na ji domin mu tattauna abin da ya kawo ni.
"Sara dai halinta na tumasanci ta aikata, har ta janyo Basiru ya darza mata ɗan banzan kashi. Sannan ya yi mata saki uku ringis, saboda ya kama ta da almajirin gidansu turmi da taɓarya a cikin ɗakinta."
Babu shiri na furta, "Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun! Ke duniya ina za ki da mu?"
"Bari kawai! Ta gama aibata ki cikin mutane ta manna miki sharri. Sai ga shi ita kuma abin ya zo kanta, bayan tayar da jijiyoyin wuyan da Basiru ya gama yi a dalilinta. Duk da kuma shi da ita duka kanwar ja ce! Amma dai nata ya fi muni a matsayinta na 'ya mace."
Ajiyar zuciya na sauke sannan na ce, "Kada ki shiga cikin masu zancen duk abin da namiji ya yi ado ne. Saboda shi kansa rami ne yake haƙa wa kansa da kansa, wanda idan ba Allah ya tsare ba; shi zai rufta cikinsa tare da Iyalansa duka. Saboda shi ya sayi komai da hannunsa kuma zai girbi abin da ya aikata ko da bayan ya manta. Duk da ban san wane ne Basiru ba sai a bakinku, amma ina da cikakken tabbaci a ksn haƙƙin abin da ya yi ne yake bin sa sanadin Sara."
"Ban gane ba! Ita ma fa haka halinta yake kuma ya sani tun kafin su yi auren sun yi rayuwa."
"To kin ji inda tushen matsalar ya samo asali! Daman an ce wanzam ba ya son aska a jikinsa. Ba wai ina goyon bayan abin da Sara ta aikata ba, amma wallahi Basiru shi ne silar komai. Wataƙila akwai haƙƙin wasu da yake bin sa, wanda Allah ya jarrabe shi ta wannan hanyar domin a rama abin da ya aikata. Saboda sau da yawa mutane su suke janyo wa kansu bala'i da hannunsu, don ba zai taɓa yiyuwa ka yi wa 'yar wani kai ma abin ya ƙi zuwa kanka ba. Idan ba ka da 'ya'ya akwai na dangi ko kuma a juye komai a kan matarka. Allah dai ya ƙara kare mu ya kare zuri'armu, amma wallahi maza da yawa suna aikata abin da suke kira ado, daga baya haƙƙi ya bibiye su har ya samu hawa kansu ya zauna daram!"
Murya a sanyaye Amina ta ce, "Na yarda da zancenki Maman Haidar. Don ko shi an ce ta sha kama shi da mata, wai da ta zo aiki sai ya kwashi mata ya kai gidan. Watarana ta mamaye shi ta koma gidan ba lokacin tashi ba, ta kama shi hannu dumu-dumu da macen banza suna lalata."
Murmushi na yi mai sauti sannan na ce, "A tunaninki idan da a ce shi ne ya sha kama ta aurensu zai yi ƙarkon da zai kawo yanzu?"
"Gaskiya ba zai yi ba! Don a tashi guda zai hankaɗa ta gida, tare da takardar sakinta kamar yadda ya yi mata yanzu."
"Kenan shi ne kawai mutum ita daga sama ta faɗo? Wallahi sha'anin maza yana ba ni mamaki. Laifi goma suke yi wa mace ta danne ta yi haƙuri, har ma ta yi ƙoƙarin ɓoyewa gudun wani ya ji a yi masa ɗan kallo. Amma shi guda kacal za ta aikata masa ya tona mata asiri ya rabu da ita."
"Wallahi haka ne tabbas! Allah dai ya kyauta kawai, amma maza ba za su iya yin kwatar haƙurin da muke yi da su ba. Miye labari? Don tun da na gan ki na san ruwa ba ya tsami banza."
'Yar dariya na yi sannan na ce, "Kenan dai idan babu dalili ba zan zo ba?"
"Sosai ma! Yan ofishimu har gori suke yi mini a kan zuwan da nake yi wurinki kullum ke ba ki zuwa. Don na san yau sai na sha surutunsu, duk da zuwan naki zai yi amfani, ko ba komai kin wanke mini gorin da suke yi mini koyaushe."
"Su dai mutane ba su raina abin magana." Abin da na faɗa kenan ina murmushi tare da gyara zamana na labarta mata komai.
Shiru muka yi dukanmu kafin Amina ta sauke ajiyar zuciya tare da faɗin, "Danƙari!" Dariya muka yi a tare sannan ta ce,
"Gaskiya dole ki shiga tashin hankali a kan wannan lamari. Kuma ba abu ne mai sauƙi ba balle ki faɗa wa Maman Taufiƙ ta sani tun wuri, kafin labari ya dawo kunnenta ta zargi da sa hannunki a ciki."
"Kuma ba zan iya tunkarar ta da wannan batun ba. Domin ba zan taɓa zama sanadin rura wutar bala'i tsakaninta da mijinta ba."
"To ya za ki yi yanzu?"
Tambayar da Amina ta jefo mini kenan tana kallo na, "Sajida ce kawai makamin da zan riƙa domin na hana ta karɓar abin. Sai dai kuma idan Allah ya ƙaddara babu yadda zan yi da ikon Allah!"
"Ni dai da kin bi shawara kin faɗa mata komai ki fitar da wuyan hannunki."
Shiru na yi ina tunanin maganganun da muka taɓa yi har tana zancen ina mata fatar kishiya. Ina 'yar dariya na ce, "Ba za a ji mutuwar Sarki a bakina. Zan dai yi iya bakin ƙoƙarina wurin hana Sajida shi."
"To Allah ya kawar da fitinar da ke ciki."
"Amin"
Daga haka muka rabu saboda lokacin tashi ya yi. Har muka je inda muke tsayuwa neman abin hawa ba mu daina zancen ba.
****
Zuciyata cike da damuwa na shiga gida bayan mai adaidaitasahu ya ajiye ni. Na kwashe sauran canjin da suka rage mini na miƙa masa, jakata empty take saboda na yi ƙaf daga gida har daji.
Da guntuwar sallama na shiga falon, saboda sanin yarana ba su gidan. Ban ji motsin komai ba don ɗakin Mukhtar ma a rufe yake ruf alamun ba ya gidan. Har na gota ɗakin Barira na dawo babu shiri na tsaya jikin ƙofar, domin na ji tabbacin abin da kunnena ya jiyo mini.
Sambatu na ji wanda cikin muryoyi biyu masu ɗauke da tsantsar shauƙi. Sai ihu suke yi suna shan yaji tamkar duniyar don su kaɗai aka yi ta.
Cikin tashin hankali na nufi ɗakina saboda zuciyata da ke zargin Mukhtar ne tare da Barira a ɗakin. Amma har na zauna kan gadona ban daina jin sautinsu ƙasa-ƙasa ba, wanda kuma alamu ya tabbatar mini ba Mukhtar ba ne take tare da shi.
Don tun da aka kawo ta gidan ko daren farkonsu ban ji irin wannan ihu da sambatun ba. Haka kawai zuciyata ta kasa natsuwa da hakan, duk da na yi ƙoƙarin ture abin gefe na yi sallah.
Na fito zuwa kitchen sai dai ban ji surutan ba a lokacin, sharp-sharp na girka taliya ƙwaya ɗaya na zabga mata kayan haɗi. Nan take ƙamshi ya karaɗe gidan saboda ni kaina na san za ta yi daɗi ko a ido.
Falo na dawo na zauna, ina cin taliyar na ji ƙarar buɗe ɗakin Barira. Ban damu da kallon wurin ba balle na ga masu fitowa.
Shirun da na ji ya sa na ɗaga kaina na kalli bakin ɗakin, Barira na gani tare da wata ƙawarta sun sha jinin jikinsu. Wataƙila ganin da suka yi mini ya sa suka razana.
"Daman kin dawo Aunty?"
"E!"
"Yaushe kika shigo ban sani ba?"
"Tun lokacin da kuka fara ihu ke da ƙawarki."
Na ba ta amsa ina ci gaba da cin abincina alamun ko a jikina. Barira ta fara rawar murya tana faɗin,
"Aljanun..ta ne..suka ta..shi..shi ne fa..na yi mata addu'a..da ƙyar suka kwanta."
"Allah Sarki! Gara da suka kwanta da wuri, don har na kira Mukhtar na faɗa masa; ya yi gaggawar zuwa Barcynsa da ƙawarta suna ɗaki suna ta sambatu. Domin ya ji daɗin cin uban aljanun da kyau har sai sun daina ihun daɗi"
"Wallahi Aunty da gaske nake yi ko gidansu an san suna tashi lokaci bayan lokaci." Abin da Barira ta faɗa kenan tare da isowa inda nake jikinta yana ɓari.
"Daman ai ban ce kina ƙarya ba."
"Zo Aunty Suby ki yi mata bayani ko za ta gane" Ta ƙare maganar tana zarar ido alamun rashin gaskiya ɓaro-ɓaro a kan fuskarta.
Murmushi na yi mai sauti, sannan na ajiye plate ɗin na ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya a kan teburin na ce,
"Kun fi ni tashanci, ni kuma na fi ku wayo saboda dukanku na girme ku. Don haka na ji duk abin da kuke faɗa a cikin sambatunku. Kuma na san me kuka aikata, saboda haka zaɓi ɗaya na ba ki. Ko ki daina wannan shashancin daga yau. Ko na faɗa wa Mukhtar gaskiya ya ɗauki mummunan mataki a kanku daga ke har ita."
"Wallahi Aunty na daina, daman can magani ne muka sha muka yi bacci. Ba mu san duk abin da ya faru ba har sai da muka farka."
"Wane irin magani ne haka?"
"Ke kam Barira kin sha haushi! Ita kishiyar kike yi wa wannan rawar muryar? To ki zauna tana yi miki titsiye tun da uwarki ce! Mitsssss! Aikin banza kawai, ni kin ga tafiya kya ji da kayan takaicin ki ke kaɗai."
Zancen ƙawar Barira kenan wadda na ji ta kira da sunan Suby. Na yi hanzarin miƙewa na biyo ta, gani na ya sa ta ja ta tsaya tana hurar hanci ta ce,
"Wallahi daidai nake da ke, don ba tsoron ki nake ji ba"
Gidan na rufe da kwaɗo ta ciki, sannan na koma ɗakina na ɗauko waya na kira Mukhtar. Kira ɗaya biyu ya ɗaga yana faɗin,
'Lafiya?'
"Ba lafiya ba! Ka zo gida yanzun nan ga wata ƙatuwa nan ta zo har gida tana lalata da Barira."
'Ban gane ba!'
"Ka zo gidan za ka gane"
Ina ƙare faɗar hakan na nuna ta da hannu na ce, sai kin san ƙaryar bariki kike yi yau. Don sai kin raina kanki tun da ke kwartanci ba komai ba ne a wurinki.
"Idan ya zo ki ce ya kashe ni!"
"Ba zai kashe ki ba, amma za ki raina kanki."
"Don Allah Aunty kada ki biye ta, wallahi ba na so Romiyo ya ji maganar nan. In Sha Allah daga yau ko gidan nan ba za ta sake zuwa ba."
"Ke kam kina da abin takaici Barira! Har yaushe za ki dinga kwantar da kai ga kishiya irin haka tamkar za ki yi mata sujada. Abin da take tunanin an yi kuma shi aka aikata, idan akwai wani abu da za ta yi kafin soloɓiyon mijin ya zo ta fara yi kafin shi. Ni wallahi da na auri irin wannan ragon mazan ƙara na lalace a kan titi."
Dariya ta so ba ni, amma kuma na mazge na ce,
"Oh ita Barirar ce ta faɗa miki soloɓiyo ne?"
"Ko ma dai mene ne hakan yake."
Bubbugar ƙofar da ake yi ya sa na je na buɗe kwaɗon na ja gefe, saboda ganin Yaya Maimuna fuskarta a haɗe. Tana ƙoƙarin yin magana Barira ta iso wurinta da gudu tana kuka tare da kai mata ƙara ta.
"Kin ga Aunty nan ta saka Aunty Suby gaba tana ƙoƙarin manna mata sharri. Don Allah ki ce ta bar ta ta tafi tun da ba gaskiya ba ne abin da take zargi."
"Yi shiru! Faɗa mini me ya faru?"
Zancen Yaya Maimuna kenan tana ƙoƙarin rarrashin Barira, ta hanyar bubbuga bayanta tana share mata hawaye.
Suby ta fara magana tana cewa,
"Wai daga ta dawo ta gan ni cikin gidan, shi kenan take neman haɗa ni da sharri. To wallahi ni daidai nake da zamaninta don na ci dubu sai ce..."
Marin da na kai mata a haukace ya sa ta haɗiye sauran maganar da ke bakinta. Ban jira komai ba, na yi cikinta da duka cikin sa'a na jefar da ita ƙasa na haye. Yaya Maimuna da Barira suna ƙoƙarin ture ni kanta na yi wata zabura na watsar da su ƙasa warwas suka faɗi.
Sannan na ci gaba da kai wa Suby naushi a baki su ma suka rufe ni da duka. Hargowar Mukhtar ta sa dukanmu muka shiga hankalin kanmu. Gefen bakin Suby ya kumbure tamkar zunɓutun kaza, amma a hakan ta dinga aika mini zagi ta uwa ta uba.
Mukhtar ya dakatar da ita, sannan ya tambayi dalilin faɗan. Na yi masa bayanin komai Barira ta fashe da kuka tana faɗin ƙarya nake yi mata. Suby ma ta tuɓure a kan sharri ne na yi musu ba gaskiya ba ne.
Yaya Maimuna ta dinga jifa ta da miyagun maganganun da suke nuni; da fatar abin da nake yi wa Barira ƙazafi da shi ya hau kaina ko 'ya'yana.
Raina a ɓace na ce, "Bakinki ya sari ƙaton dutse, don har abada ni ko yarana ba za mu yi irin wannan halin tumakai ba."
Mukhtar ya taso mini da masifa kamar ya dake ni, wai na yi wa Barira da Subyn ƙazafi kuma idan na sake duk abin da na janyo wa kaina babu ruwan shi. Haushi ya sa na dinga mayar masa da raddi bakina yana kumfa tamkar na kai masa duka.
Sanin halina ya sa bai taɓa ni ba, ya dawo kan Suby yana ba ta haƙuri tare da lallaɓa ta har ta fice gidan. Yaya Maimuna kuma ta dawo da faɗan sabo don daman can shi ya kawo ta.
"Daman wurinki na zo! Zugar da kike yi wa Sajida ta yi aiki. Amma ki sani wallahi muddin kika ga ba a yi auren nan ba; to sai idan ba na numfashi a cikin duniya. Amma wajibi ne sai Sajida ta auri Aminu ko kina so