Showing 48001 words to 51000 words out of 121208 words
amarya muke yi. Shi ya sa kika ji ni shiru, ga kuma aiki da yake hana ni zama kullum ina zarya kan titi."
Kallo mamaki take yi mini sannan ta ce, "Wace Amarya kuma?"
"Amaryar Mukhtar!"
Amsar da na ba ta kai tsaye kenan, murmushi a kan fuskata. Baki a sake take kallo na bayan tagumin da ta rafka, dariya na shiga yi mata alamun ko a jikina illa tsabar farincikin da nake ciki. Wanda ya kasa ɓoyuwa har sai da ya bayyana kan fuskata.
"Yanzu ke don Allah a kan auren Mukhtar kike wannan murnar?"
"Sosai ma! To miye cikin ido ban da ruwa? Ai inda akuyar gaba ta sha ruwa, ko ta baya idan ta zo a nan za ta sha."
"Hmmmmm! Kina wasa da lamarin maza Maman Haidar. Ke a tunaninki abin da ya yi miki shi zai yi wa wata idan ta shigo?"
"Sosai ma kuwa! Don ƙwaryar sama ce take dukan ta ƙasa. Kuma ni wannan auren ma da ina da dama har sadaki ni zan biya masa. Domin kawai ya gano na fi shi farinciki da ƙulluwar auren."
"Lalle da sauranki har yanzu Maman Haidar. Ai wallahi ni da na ga ranar da Amini zai yi aure, gwara na ga ranar mutuwata."
Dariya ta suɓuce mini babu shiri, da abun ya yi mini daɗi ma har da bajewa na yi a kan kujerarta riƙe da ciki. Saboda zancenta ba ƙaramar dariya ya ba ni ba, domin zurfin da ta yi a kan sha'anin maza, ya nuna har yanzu ba ta san zafin duniya ba.
Natsuwar dole na gayyato, saboda yanayinta da na ga ya juya zuwa kalar tausayi.
"Ko ni na samu mijin ƙwarai wanda ya san zafina, wajibi ne kuma dole na yi kishin abuna. Amma kuma ba zan zafafa kishina irin haka ba, saboda ba gare ni aka fara ba kuma ba za a ƙare kaina ba. Sannan shi ɗa namiji, a duk lokacin da kika zafafa kishinki a kansa, matuƙar ba ki yi dace da mai dogon nazari da hangen nesa ba. To zai yi miki kallon wata shashasha wadda ba ta san abin da take yi ba, ƙarshe ma ya ce ba kya son zaman lafiya, ko kin cika fitina da janyo abin da zai kawo muku faɗa. Saboda a lokacin idonsa a rufe yake da son auren, duk abin da za ki yi masa ba zai burge shi ba, matuƙar ba goya masa baya za ki yi a kan auren ba."
"Ai kuwa wallahi sai dai kada ya gani, domin ba zan taɓa goya masa baya ya yi mini kishiya ba. Cabɗijam! Allah kada ya nuna mini wannan ranar, don na san tun kafin lokacin auren ya yi zan mutu saboda mugun kishin Amini da nake yi. Shi ma ya sani ba zai taɓa zo mini da irin wannan zancen ba."
Shiru na yi ina kallon ta, domin idan akwai naƙasunta da na sani duniya bai wuce kishi ba. Kuma ina yi mata uzuri saboda shaƙuwar da ke tsakaninta da Aminin mijinta. Wanda saboda tsabar so da shaƙuwar da ke tsakaninsu yake kiran ta Aminiya ita ma ta kira shi Amini.
"Ni dai kam! Ko a kwalar rigata Maman Taufiƙ. Idan zai yi huɗu a rana ɗaya wallahi babu abin da zai ɗaga ni sama balle ya buga ni a ƙasa. Tsuntsun da ya ja ruwa shi ruwa kan doka. Kuma wanda duk ya ce zai iya haɗiye gatari ya dace a riƙe masa ɓota."
"Wallahi Zaituna kina ba ni mamaki, shin wai ba auren soyayya kuka yi da Abban su Haidar ba?"
"Soyayyar gaske ma, irin ta bugawa ga jarida a yi talla. Amma yanzu, ƙiren sonsa ba na ji a cikin zuciyata, kamar yadda ko wulagawar shi na hango daga nesa, sai na ji haushin sa ya yi mini rumfa."
"Anya ba namijin dare ne yake aurenki ba?" Tambayar da ta jefo mini kenan na ba ta amsa.
"Idan ma shi ne ya burge ni, domin ya nuna zallar kishin da yake yi mini wanda ba ya son kowa ya raɓe ni. Domin ina da tabbacin zai ba ni kulawar da za ta gamsar da ni, kuma zai hana ni kukan kaɗaaicin da nake yi yanzu."
"Hu'ummm! Kin yi nisa Zaituna, amma ni kam har abada ba na fatar Amini ya yi mini kishiya ko da a mafarki. Ke akwai wata da ta so zautar da ni a kan nacin da ta yi masa ya aure ta, don bala'i macen da yaranta har sun je jami'a. Wai a haka ta nace masa dole sai ya aure ta tun da mijinta ya mutu ya bar mata gado. Ai na rantse da Allah ranar da na gano, daga ni har shi ba mu yi bacci ba, asubar farin na bar garin nan na yi Kano. Domin gabaɗaya idona rufewa suka yi ba na hangen komai a lokacin face mutuwata. Abin baƙinciki kuma babu wanda ya goya mini baya a gidanmu, sai laifina da aka dinga gani ana ƙoƙarin nuna ya fi ni gaskiya. Sun kasa gano zafin da nake ji idan na tuno girman matar da manyan 'ya'yanta. Don akwai wata 'yarta da ta ci ta ƙoshi, wadda ko yanzu aka ce ta haifi yara uku ba zan musa ba. Amma wai a hakan take son Amini ya aure ta don baƙar zalama irin ta wasu ƙattin mata."
🤭sannu Maman Taufiƙ😂
D. AUTA CE✍🏼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*ASHIRIN DA BIYU.*
Dariya na sha sosai har ta nemi ƙulle mini ciki, saboda maganganun Maman Taufiƙ sun saka ni dariya ba tare da na shirya ba. Fuskarta na kalla bayan na gama dariyar, hadarin da fuskar ta ɗoro tare da ƙwafar da na ga ta yi, alamunta ya nuna mini har lokacin kishin matar bai daina cizon ranta ba.
"To ke Maman Taufiƙ, ai ita ce ke son shi idan na fahimci labarin da kyau. Da kin bari an yi auren, wataƙila da yanzu har mu maƙotanki mun je hajji. Saboda bauta ce kawai za ta zo yi miki tun da kin fi ta power a wurin Baban Taufiƙ."
"Hmmmmm! Ba za ki gane ba!"
Zancen da ta yi kenan tana haɗe fuska tamkar ta yi kuka, kafin ta cire tagumin da ta rafka hannu bibbiyu ta sake cewa,
"Kin san me? Ko da za ta kwanta ƙasa na dinga taka ta da ƙafafuwana saboda biyayya, ba zan taɓa cire takaicin ta a raina ba. Wai ko ki san yadda nake kishin Amini kuwa? Ke ni fa da dai a ce ya haɗa ni sharing ɗinsa da wata, gara kawai ni na haƙura na bar wa kowace ce shi. Na fi son haka da a ce na zauna baƙinciki ya kashe ni."
"Ba fa za ki mutu ba! Matuƙar ba ke ce kika ƙwallafa wa kanki hakan ba. Saboda duk abin da kika gani daman can muƙaddari ne daga Allah, don haka ki daina zafafa kishinki gudun ki saka kanki matsala a banza."
Na yi maganar cike da burin saka mata ƙwarin gwiwa a zuciya, sai dai ko kaɗan zancen bai yi tasiri ba. Domin idonta a rufe ta ce da ni,
"Ni fa komai za ki faɗa in dai a kan zancen kishiya ne, to ba zan fahimta ba balle na gane. Don haka mu bar zancen kawai raina suya yake yi sosai wallahi."
Shiru ya ratsa tsakani sannan na sauke ajiyar zuciya, bayan na dawo daga zuzzurfan tunanin da na lula, a kan tashin hankalin da za ta shiga a lokacin da ta ji Baban Taufiƙ yana neman aure, domin da idanuwana na gan shi da wata bazawara a bayan layinmu suna taɗi.
Saboda kusa da gidan su bazawarar nake zuwa kitso, da tunani fal raina na shiga gidan a lokacin, bayan zancen zucin da nake yi. Ina ta jefa wa kaina tambayoyin da ba amsa, a kan miye haɗin shi da ita? Duk da yanayinsu ya bayyana mini zahirin abin da ya haɗa sun. Amma ban gasgata ba sai lokacin da bazawarar ta shigo gidan ana tsaka da yi mini kitso, mai kitson tana 'yar dariya ta ce da ita,
'Har ya tafi?' Ita ko bakinta har kunne ta zauna tana faɗin,
'Ya tafi! Ai mutumin ya san kansa, sosai yake da qualitys ɗin da nake so, kuma nake fatar samun su a wurin namijin da nake muradin ya zama mijina. Yanzu haka duk da ba mu jima tare ba, amma ya nuna mini shi ba ya son a ja lokaci. Idan na shirya wata biyu masu zuwa a yi komai a gama.'
'Caɓji! Lalle wannan da zafinsa ya zo.'
Haka na yi ta tuno hirar bazawarar da mai kitsona, wadda har suka ci suka cinye ban ce da su ƙanzil ba. Saboda ba na so na katse musu zancen, sannan kuma ba zan iya shiga sabgar da ba a kasa ta da ni ba.
'Yanzu idan ta ji wannan batun ya za ta yi?'
Tambayar da na jefi kaina da ita kenan, wadda ban samu amsarta a zuciyata ba na fara jiyo sallamar da su Ummu Salma suke ta rafkawa.
Tare muka amsa musu ni da Maman Taufiƙ, sai da aka ba su umurni sannan suka shigo. Gayar da ita suka fara yi ni ma suka gaishe ni, na miƙa musu makulli suka fice suna faɗin sai na zo.
Ajiyar zuciya na sauke sannan na ce da ita, "Wallahi kin sa jikina ya yi sanyi Maman Taufiƙ. Saboda har raina, ba na jin daɗin zafin kishin nan naki, da ina da iko da na rage miki shi ko da kaɗan ne. Domin ina jin tsoron abin da zai faru a lokacin da ƙaddarar aure ta haɗa Baban Taufiƙ da wata."
"Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun! Don girman Allah ki daina ambatar wannan magana, kada tsautsayi ya sa 'yan amin su amsa ki janyo mini masifa. To idan ma wannan ne in Sha Allah babu shi babu aure nan gaba, saboda ni kaɗai na ishe shi rayuwar duniya, kuma ni kaɗai yake da buri zama da ni. Baya hangen kowace mace balle ya yi mata kallon daraja, saboda Allah ya karɓi addu'ar da nake yi masa koyaushe. A kan duk matan duniya, fuskarsu ta koma ta akuyoyi a idonsa, balle ya ga kyawunsu ya ƙyasa ya ɗauko mini jangwam!"
"Hmmm! Kin fi ƙarfina Maman Taufiƙ! Ni zan tafi don babu amfanin duk wata maganar da zan ƙara yi a kan hakan. Saboda kin fi ƙarfina, amma duk da haka, na yi alƙawarin zan dinga yi miki addu'a a kan wannan kishin balbal, domin ina da burin Allah ya rage miki shi ki samu sukunin zuciya ko don ki ji daɗin fuskantar rayuwa."
Zancen da na yi mata kenan a lokacin da na miƙe, fuskarta a haɗe ta rako ni tana faɗin, "Ban ji daɗin wannan zuwan ba, domin kin fama mini mikin da na daɗe ina jinyar zuciyata kafin ya warke."
"Kwantar da hankalinki, in Sha Allah sai kin daɗe ba ki gan ni cikin gidan nan ba. Sai dai kuma hakan ba shi zai hana ni yi miki fatan shiriya daga wannan azababben kishin naki ba."
Ina gama faɗin hakan na fice gidan, ta raka ni da faɗin, "Kishi halas ne! Ke da ba kya yi kuma ai kin hutar da kanki daga ladar da ake samu."
Dariya na ƙumshe gudun ta ga damata, sai da na shiga gida sannan na tuntsure da dariyar tamkar wata zautacciya, 'Waton shi ma zazzafan kishin miji ibada ne da ake samun lada a ciki idan an yi?' Tambayar da na yi wa kaina kenan ina dariya.
"Wallahi sai dai kada na samu wannan lada, da dai a ce na yi kishin Mukhtar irin haka. Cabɗijam! Da sake!"
Maganar da na yi kenan a fili lokacin da nake shiga falon, kiran sallar magrib da na ji an fara yi ya sa na ce da yaran,
"Oya a tashi a yi sallah."
Sannan na shige ɗakina na faɗa toilet. Har na gama sallah tunanin hira ta da Maman Taufiƙ nake yi, ban tashi daga kan sallayar ba sai da aka yi Isha. Na daɗe ina yi wa Maman Taufiƙ addu'a tamkar damuwarta ce kaɗai abin da yake damu na.
wayata na ɗauka na fito falo inda su Ummu Salma, tare muka ci abinci da su ina duba saƙonnin da ya tarar mini. Waɗanda suke buƙatar amsa ta dole, saƙon MD na fara buɗewa raina a haɗe tamkar yana gabana.
'Na gamsu da hangen nesanki. Kuma in sha Allah na janye ƙarar daga yau. Na gode sosai!'
Mere na yi kaɗan sannan na tura masa 'Ana tare!'
Daga haka ban sake bi ta kan shi ba duk da yana online a lokacin. Bugun da ƙirjina yake yi, ya sa na bar WhatsApp na koma facebook. Saboda a duk lokacin da na hango sanarwar da ake yi mini a kan yana online, sai na ji gabana ya ƙire ya faɗi dam-dam!
Bacci ya ci idona, ban san lokacin da Mukhtar ya dawo gidan ba, sai da safiya ta waye muna shirin fita. Sannan na hango shi ya nufo ɗakin su Ummu Salma ya buɗe da makulli ya shiga, jim kaɗan sai ga wani garjejen ƙato ya shigo da bokitin fenti biyu a hannunsa ya shige ɗakin. Mintuna kaɗan wani ya ƙara shigowa da wasu bokitan ya shige.
Raina ya fara turirin baƙinciki, saboda haushin shigowar mutunen ba tare da Mukhtar ya sanar da ni ba, domin a tunanina ko ba gidan aure ba ne, yana da kyau a sanar wa masu gida wasu gardawa za su shigo, domin su kimtsa. A matsayin su na mata ko ba su da aure, tun da ba maza ne danginsu ba balle a ce duk ɗaya ne.
Zuciyata ta zo wuya, na dinga ji kamar na shiga na shaƙe wuyan Mukhtar a gaban mutanen, kuma na gasa masa baƙaƙen maganganun da ke cizon raina. Da ƙyar na iya furta 'Innalillahi wa inna ilaihirraji'un!' A zuciyata, domin na samu sauƙin da nake ji, dangane da ingizanin da take yi, a kan na yi abin da zai rage mini takaicin da aka ƙumsa mini.
A gurguje muka shirya muka fice gidan, daga ni har yaran babu wanda ya bi ta kan shi, ko mai adaidaitan a kan hanya ya haɗu da mu ya ɗauke mu, saboda gudun na yi jinkirin jiran shi cikin gidan, na aikata aika-aikar da zan raba halina a gaban gardawan.
Raina a jagule na kammala aikin da na taras ofishina, ko da Amina ta zo ta daɗe ban ce da ita uffan ba bayan gaisuwar da muka yi. Har sai da ta kasa haƙuri ta ce da ni,
"Yau dai kamar an sake taɓa mana ke?"
Shiru na yi mata tsawon lokaci, sannan na sauke ajiyar zuciya tare da fesar da iska a bakina na ce, "Ina muka tsaya a labarin?"
"Inda kika shiga ɗaki"
Amsar da ta ba ni kenan a taƙaice cikin sanyin murya. Na cire gilashin da ke sanye a idona, sannan na gyara zama na ce da ita,
_"Baƙin tozalin da na yi ya sa na yi salatin da na yi babu shiri. Saboda falona babu komai a ciki face ledar tsakar ɗaki da agogon da ke manne jikin bango, da sassarfa na yi ƙuryar ɗakin, a nan ma sai da jiri ya so kayar da ni. Bango na yi hanzarin kaiwa na jingina bayana ina sauke numfashi da sauri da sauri. Nauyin da ƙafafuwana suka yi mini, ya janyo na kasa ɗaukar kaina a hankali na sulale na yi ƙasa. Zaman dirsham na yi rungume da Ummu Salma da ke baccinta sharkaf ba tare da ta san wainar da ubanta ke toya mini ba._