Showing 36001 words to 39000 words out of 121208 words
ban san lokacin da aka kawo ni gidan nan ba. Amma yanzu Alhmdulillah da sauƙi komai ya lafa."
"Allah ya ƙara lafiya, amma ki daina cin abin da ke tayar miki da ulcer, sannan ki dinga shan magani saboda ki samu ta lafa miki ki huta."
"In Sha Allah!"
Dukanmu muka bi ƙofa da kallo saboda shigowar Inna Kulu da kula. Gaban Amina ta ajiye tana faɗin, "Ku ci awara tun kafin ta yi sanyi."
Bayan fitar Inna Kulu Amina ta miƙe tana faɗin, "Bari na fara yin sallah don ba na son na ci na kasa motsin kirki. Tun da kin tayar mana da hankali a wurin aiki ana ta jimamin ciwonki, MD ma yau bai zauna ba tun da ya zo da safe ya fita har na baro wurin bai dawo ba."
"Uhumm!" Kawai na ce ta fice na ci gaba da jan carbina, har ta dawo na tashi na ba ta sallayar. Kafin ta gama na zuba mana awarar a plate ɗaya, tare da ruwa a kofuna.
Bayan ta gama muka fara cin awarar ta sha kayan haɗi da daddaɗan yaji, domin sana'ar Inna Kulun ce kuma sosai take samun rufin asiri da ita. Shiru ya ratsa tsakani, kafin Amina ta kawar da shirun da cewa,
"Da zumuɗi na tashi yau domin na zo na ji cigaban labarina, abin haushi sai ga shi na tsinci zancen ciwonki a bakin MD. Bayan na yi ta rangadin zuwa offishinki ina ganin shi a kulle, a zuwa na ƙarshe ne da na gan shi zai fita nake tambayar shi ko kin zo; ya ce da ni kin turo masa saƙo ba kya samun damar zuwa ciwonki ya tashi kina gida. Da ƙyar na samu na kammala aikina na nufi gidanki, ganin gidan a rufe ya sa na kira lambarki ba ta shiga. Dole na na sake neman shi na sanar da shi ba kya gidan, ya sanar da ni kin ce kina gidanku wurin Umma Bafarawa Estate. Adaidaita na ƙara samu na yi gida, sai da na kammala ƙananun ayukana sannan na ƙara shiri zan fito."
Ƙasake ta yi tana lagudar awarar da ke hannunta wanda a take na gano akwai abin da ya faru kafin ta fito gidan. Hakan ya sa na samu kuzarin faɗin, "Ai da kin yi haƙuri gobe ma zan shiga aikin. Kin ga sai mu ɗan samu abin da zai sauwaƙa kafin a tashi."
"Hmm! Ai ba zan iya haƙurin ba wallahi, in da na samu wayarki da ba zan shiga damuwar da na shiga ba. Saboda ina tunanin a wane hali kike ciki duba da yanayin da kika baro wurin aikin jiya, kamar akwai wani abu maras daɗi da ya faru da ke. Hakan ya ƙara tayar mini da hankali ga shi matsalar da na samu ban san gidan da zan faɗa a kawo ni ba. Kuma ina da tabbacin MD ma bai san gidan ba shi ya sa ban neme shi ba."
"Ya aka yi kika gano gidan yanzu?"
"Tambaya muka fara yi ni da mai adaidaitan da muka zo unguwar, har na yi katarin ganin Haidar tare da wasu yara a daidai wani shago. Da hanzari na kira shi yana gani na ya nufo ni yana gaishe ni, a nan yake yi mana kwatance na ce ya shigo ya kawo mu kawai."
Ajiyar zuciya na sauke sannan na ce, "Allah Sarki Amina, na gode sosai da ƙoƙarinki. Allah ya bar zumunci."
"Amin" ta ce sannan ta yi hanzarin fiddo wayarta a jaka saboda kiran da ake yi mata. "Ga ni nan zuwa yanzu." Abin da ta faɗa kenan fuskarta a haɗe bayan ta gama sauraron abin da aka ce cikin wayar. Mere na ga ta yi tare da hurar hanci tana lasar maiƙon da ke hannunta. Ban ce da ita komai don na san tatsuniyar gizo ba ta wuce ta ƙoƙi.
"Na rasa me na tare wa Mama da ko kaɗan ba ta ƙaunar farincikina. Yanzu fa ba ta ji kunyar kai ƙara ta wurin shi ba. Kuma shi ya bar ni fitar nan amma ƙiri-ƙiri ta so hana ni fitowa, saboda girkin da zan gama wahala a hana ni kwana da miji."
Ta ƙare maganar fuskarta a cure, hakan ya tona mini asirin takaicin da take ƙumsa dangane da baƙar dokar Mama. Wadda mijinta ya mayar tamkar faɗar Allah da ta faɗa sai ya aiwatar ko ba ya so, duk da san kuskure ne yake aikata wa matar shi, bayan alaƙar zumuncin da ke tsakaninsu mai ƙarfi. Domin Mama uwar miji ce gare ta kuma Gwaggonta, saboda Yaya take ga Mahaifin Aminar uwa ɗaya uba ɗaya.
Amina ta so zama na ɗora mata labarin, amma dole na dinga nuna mata rashin dacewar zaman tun da gobe zan fito aiki. Sannan na ba ta haƙuri sosai tare da nuna mata alfanun juriya a kan cutarwar da Mamar take yi mata da gangan, matuƙar tana son ganin ribar a gaba. Cikin nasara na ci kanta ta miƙe tana saɓa jakarta a kafaɗa tana faɗin,
"To ni zan tafi Allah ya ƙara sauƙi. Amma don Allah ki ƙoƙarta ki fito goben."
Har bakin titi muka raka ta ni da su Ummu Salma, tare da ba ta tabbacin zan fito gobe ta tsumaye ni. Ta tafi muna ɗaga wa juna hannu na juyo ina goge ƙwallar tausayin kanmu ni da ita, duk da na fi ta matsala amma har zuciyata ina jin tausayin ta a raina. Saboda ba ta da ƙarfin zuciyar shanye damuwa, saɓanin ni da na zamo turmin tsakar gida sha luguden mahassada. Domin duk wani sara da sukan da aka yi mini bai hana ni kirkiza ba, balle damuwar hakan ta bayyana a jikina. Dalilin hakan ya sa wasu da yawa suke hawa kan batutuwan Mukhtar su zauna. Saboda na kasa zama abin tausayi a kan fuskokin mutane, ta yadda za a gano matsalar da nake ciki ta hanyar rama ko lalacewar da ido zai tabbatar da lalle ina shan wahala a gidan shi.
Da dare misalin ƙarfe tara da rabi na dare, Umma da Inna Kulu suka kai ni gidan Mukhtar. Da motar wani Baban ƙawata kuma maƙocin Kawu Sale kuma abokin shi. Bayan sun gama jan kunnena sosai a kan na yi haƙuri na zauna lafiya da mijina, sai dai ni ko kaɗan ban ɗauki shawarar zama da shi a yadda suke so ba. Don ya gama sire mini kuma mutuncin shi ya daɗe da zubewa a idona. Saboda ba na jin zai iya dawo da martabar shi gare ni ko da zai mallaka mini ƙasar Nigeriya da abin da ke cikinta.
Ko da muka je mun tarad da shi, suka ƙara haɗa mu duka suka yi mana nasiha tare da saka mu neman yafiyar juna. Bayan sun tafi na saka yarana suka kwanta na tofe su da addu'o'in bacci sannan na rufo musu ɗaki.
Ɗakina na nufa na yi sabon wanka don jin daɗin kaina, sannan na kwanta tare da janyo wayata. Messages na shiga dubawa ta inbox da saƙonnin da ake ta turo mini daga waɗanda nake mutunci da su a wurin aikinmu. inda ake ta yi mini ya jiki tare da fatar samun sauƙi, saboda tun an karɓo mini jakata a hannun su Ummita, ban sake kunna wayar ba sai a lokacin. Shi ya sa ban san da shigowar saƙonnin ba. Amsa na shiga bai wa mutanen har na zo kan saƙon MD, haka ƙawa na tsinci kaina da yin guntun tsaki ba tare da na shirya ba. Saboda har lokacin ban daina jin haushin abin da ya yi mini ba, wanda nake ji a raina tamkar ya datse ganin walwalar fuskata har abada. Domin na ci alwashin ko kallo don ya zama dole na gan shi, amma da ina da iko da hana kaina ganin shi saboda tsabar takaicin shi da nake ji.
Bubbugar da na ji ana yi wa ƙofar ɗakina ya sa na yi kasaƙe ina sauraron muryar Mukhtar da ke ta faɗin, "Ki buɗe magana za mu yi." Tsaki kawai na ja sannan kashe wayar tare da juya kwanciyata, yawan bugun da yake yi wa ƙofar ya sa na miƙe a fusace na buɗe ƙofar tare da tare hanya, ƙugu na riƙe fuskata a cure na ce,
"Malam lafiya?"
"Lafiyar ce ta kawo hakan!"
Amsar da ya ba ni kenan ya ratsa ta gefena ya shigo ɗakin. Zama ya yi a kan gadona yana murmushin shi da ke nuna mini alamun wata sabuwar yaudara ta kawo shi ɗakina. Domin ba na kawo ƙarshen zuwan shi ɗakin cikin lalama ba tare da tashin hankali ya ingizo ƙeyar shi ba.
"Zo ki zauna."
Abin da ya faɗa kenan yana nuna mini kan gadon a kusa da shi, kallon banza na aika masa tare da sakin guntun tsaki na rungume hannuna a ƙirji ina kallon gefe. Tasowa ya yi kai-tsaye na ɗauka fita zai yi kawai na ji ya rufe ɗakin da key yana ƙoƙarin tuɓe kayan shi.
Kallon mamaki na bi shi da shi tare yin dariyar takaici saboda na san ƙarshen wasar. Domin fankam-fankam ba shi ne kilishi ba, an sha yin ruwa ƙasa tana shanyewa. Idan ba yaudarar kan shi yake so ya yi ba ya san ba zai iya ba komai ba a nan fagen, amma don ya nuna mini shi ma jan wuya ne ya zo mini da ɗanyen kan da babu inda zai ƙare sai rabuwa baram-baram ni da shi.
Shin wane shiri ne Mukhtar yake yi wa Zaituna? Domin alamu ya nuna shi ma wannan karon zai zo da sabon salo.🤔
D. AUTA CE✍🏼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*LAMBA SHA TAKWAS.*
Nufo ni ya yi gadan-gadan yana ƙoƙarin haɗa jikin shi da nawa, cikin zafin nama na tura shi ya yi baya. Sannan na nuna shi da hannu cikin ƙololuwar ɓacin ran da ya ziyarce ni.
"Kada ka yi gangancin zo mini da wani sabon sanabe, don sanin kanka ne babu wata alaƙa da ta yi saura tsakanina da kai yanzu. Sawunka a likkafa ka fice mini daga ɗaki tun muna shaida juna, idan kuma ka fi so ka tunzura ni na yi maka aika-aika to ka sake zuwa kusa da ni."
Kallo na ya tsaya yi na ɗan lokaci, kafin ya sake nufo ni yana dariya kamar bai ji kashedin da na yi masa ba. Janyo ni ya yi da ƙarfi na zille, nan take muka fara kokawa ni da shi, cike da ƙarfin zuciya nake ta hana shi abin da yake ƙoƙarin aikata mini.
Ganin da gaske ba zai samu haɗin kaina ba, ya dawo magana cikin haki yana faɗin, "Wallahi duk abin da ya biyo baya kada ki ga laifina. Ba dai kin hana ni haƙƙina ba? To ke kuma ki jira me zai faru cikin kwanan..."
"Kai har kana da bakin faɗar wani haƙƙinka da ke kaina yanzu? Kenan ka manta tsawon lokacin da ka ɗauka ba tare da ka neme ni ba? Ko an faɗa maka kai kaɗai ne mai haƙƙi ni ko oho? To ka je ka ɗauki matakin kada ka yi sanya, idan kuma ka fasa wallahi ban gode maka ba. Mitsssss! Aikin banza tura agwagwa cikin ruwa."
Na ƙare maganar a fusace saboda furutan shi sun sa na ji ya kai ni bango Ya jingine.
"Za ki gani!"
Zancen da ya yi kenan ya ja rigar shi ya fice fuu tare da bugo ƙofar ɗakin da ƙarfi. Ƙofar na bi da harara tamkar idona zai faɗo ƙasa, sannan na je na saka makulli na rufe na dawo na zauna ina haki. Mamaki na shiga yi a kan rashin adalci irin na Mukhtar, saboda rabon da ya nemi ni a matsayin matar shi ta sunnah sama da shekara uku. Kuma duk na yi haƙuri na jure amma sai yanzu zai zo mini da guntun rainin hankali.
Wanda na sani idan da zan kai shi kotun musulunci take yanke za a raba aurena da shi, saboda iya cutarwar duniya ya yi mini kuma ya tauye ni da baƙar igiyar da yake tinƙaho da ita.
Daren ranar ma sai da na gamsar da kaina sannan na samu damar yin bacci cikin nishaɗi, saboda ya tayar mini da tsohuwar jarabar da kullum nake ƙoƙarin kawar da kaina kanta, tare da addu'ar samun sauƙinta a wurin Allah.
Da safe ma tun da ya fita bai dawo gidan ba, sai dare bayan mun shige bacci sannan na ji yana rufe gida, ban wani damu ba don daman can bai ɗaɗa ni a ƙasa ba. Haka ma ranar Lahadi bai zauna ba, don ko yaran bai bi ta kansu ba a lokacin. Saboda ba wannan ne karon farko da fara yi musu hakan ba, domin ya sha shafa musu laifina a duk lokacin da na samu saɓani da shi, don a baya ma ko abu ya siyo ba zai bai wa kowa ba ko da yaran sun gani. Haka zai cinye abin shi muna kallo ba tare da ya ba mu ba, tun yaran suna jin haushin abin har suka daina zuwa kusa da shi idan sun gan shi da leda. Saboda a can baya ma idan ta yi masa daɗi, miƙa wa ɗiyan 'yan'uwan shi yake yi Ummu Salma tana kallo ya hana ta. A tunanin shi ni yake yi wa baƙinciki don na ji haushi.
Ranar Litinin tun da sassafe na tashi, na haɗa wa yarana abin kari sannan muka shirya tare da su muka fice. Ganin ɗakin shi a rufe ya sa na gano ya yi wurin aiki don ban san fitar shi ba.
Bayan na ajiye su makarantarsu, na ba su kuɗin tara da waɗanda za su hau abin hawa idan aka tashi. Sannan mai adaidaitan ya ajiye ni wurin aiki bayan na nemi alfarmarsa, a kan idan lokacin tashi ya yi daga makaranta ya koma ya ɗauko mini su Ummu Salm.
Saboda akwai sanayya tsakanina da shi kuma sosai yake girmama mutuncina a zahiri. Ina tafe zuciyata cike da tunanin riƙon shi a matsayin wanda zai dinga kai su Ummu Salma makaranta, kuma ya ɗauko su a duk lokacin da aka tashi. Da zummar idan an yi mana albashi na dinga biyan shi kuɗin shi gabaɗaya.
Zancen zucin da nake yi ya katse a daidai lokacin da mutanen wurin suke ta yi mini ya ƙarfin jikin ina amsawa. Turus na yi saboda babu makullin ofishin a hannuna, domin a ranar Alhamis da na bar wurin tashin hankali bai sa na tsaya rufe offishin ba. Ficewa kawai na yi saboda kwata-kwata na manta kowa da komai, face neman hanyar da zille wa auren Mukhtar a idona.
Ofishin MD na nufa raina yana suya, saboda ba na farinciki da ganin shi saboda haushin shi da nake ji. Na yi wa kaina katanga da shi kuma na kwance ƙaƙƙarfar alaƙar son da na fara ginawa a tsakanina da shi. Kaina a ƙasa ina shan ƙamshi na ƙwanƙwasa masa ƙofa,
"Yes! Come in"
Ita ce maganar da na ji ya faɗa na tura ƙofar kaina a tsaye na isa gaban shi. Ban damu da gaishe shi ba cikin haɗe fuska na ce,
"Key za a ba ni."
Ya miƙo mini yana ta rubutun shi ba tare da ya kalle ni ba, cike da haushi na fice saboda ganin ko-in-kular da ya yi mini.
Zama na yi bayan na zauna, ina nazarin abubuwa da yawa a cikin kwanyata. Sannan na fara duba files ɗin da na gani a saman teburina, na shiga aiki tuƙuru ba tare da na nemi ba'asin komai kansu ba. Saboda ina da masaniyar komai nasu, bayan lissafin da na shiga bugawa da calculator, ina ta rubuta adadin da na samu a wuraren da ya dace a jikin files ɗin.
Turo ƙofar ofishin da sallamar Amina bai sa na ɗago daga aikin da nake yi ba, na dai amsa mata sallamar saboda ba na so ta katse mini aikin har sai na gama.