Showing 75001 words to 78000 words out of 121208 words

Chapter 26 - ABOKIN AIKINA HAUSA NOVEL

24 Nov 2024

6402

abokan nasa suka yi dandazo. Fuskata a sake na fara gayar da su, waɗanda suka san ni suna tsokana ta da sunan uwargida sarautar mata.

"Gaskiya Mukhtar ka yi sa'ar mata, domin kuwa na kasa tantance ita ce uwargidan taka ko kuma amaryar ce?"

Murmushin yaƙe kawai yake yi yana kallona, fari da ido na yi wa mai maganar, duk da ban waye shi ba na ce,
"Ai duk macen da ta yi saurin zama jagwaf daga ita ne. Domin babu inda aka ce shi kaɗai ne da haƙƙin gyara ta koyaushe. Yana da kyau ita ma ta taimaki kanta da 'ya'yanta domin ta rufa wa kanta asiri da mijinta."
Kallona kawai Mukhtar yake yi, domin ya kasa ɗauke idonsa daga kaina. ni ma idona cikin nasa nake jefa masa murmushin,

'Ya ka ji kafcen?'

"Gaskiya abokina ka yi sa'ar aure, domin kuwa ka auri macen da ta dace kuma wadda ta san kanta. Congratulations bros"
Abin da wani ya faɗa kenan yana bubbuga kafaɗarsa, bai ce ƙanzil ba ya bar wurin, yana ƙoƙarin tare wani mai mashin da zai wuce ta gabanmu.
Karantar yanayinsa da halin da ya shiga ya sa na yi musu sallama na juya, zuciyata cike taf da farincikin abin da na yi. Don na san shi ya gano inda zantukana suka nufa, waɗanda ba lalle ba ne su abokansa su fahimci inda na dosa, balle su hankalta da bugun gorar da na yi masa a fakaice cikin siyasa.

Har aka watse taron bikin ban daina jin farinciki a zuciyata ba, bayan magriba wasu daga cikin danginsa suka je ɗauko amarya.
A lokacin da na ji dirar motocin 'yan kawo amarya, ƙirjina ya buga daram-dam-dum! Kafin zuciyata ta karɓa tana ta harbawa ɓal-ɓal sauri-sauri gudu-gudu. Ga uwar guɗar da ake jerawa wata bayan wata a lokacin da aka shigo gidan

"Ayyururui!!!!"

Na daburce na ji ina ma na samu ƙafar tserewa na ɓoye, domin kada na yi kukan da zan fallasa kaina a gaban mutane. Firdausi ta taso daga mazauninta ta zauna tare da yi mini raɗa a kunne.

"Ki natsu da kyau kada ki bari a gano ki plsss!"

Babu shiri wa'azinta ya shiga kaina na mazge, tare da miƙewa na tarbo amaryar. Jikina na saka ta na rungume tare da riƙo hannunta na zaunar da ita a kan kujera.
Zama na yi kusa da ita ina faɗin,
"Yau dai ga amarya a cikin gidanta. Allah ya ba ku zaman lafiya ke da angonki."

"Amin-amin!"

Gabaɗaya mutanen da ke falon suka amsa cikin ɗaga sauti. Wata daga cikin danginta ta matso kusa da mu tana faɗin,
"Ga Barira nan mun kawo muku, sannan mun damƙa ta hannunki amanar Allah!"
Murmushi na yi mai sauti sannan na ce, "Daga ni har ita amanar junanmu muke, saboda zama ya haɗa mu dole ne mu yi haƙuri da juna. Don haka ni a wurina babu wata damuwa, ina mata fatan alheri, zaman lafiyar aurenta da zuri'a ɗayyiba."

"Allahu Akbar! Sannu 'yar aljanna!"

Maganar da na ji wata ta faɗa kenan a cikin matan da suka zagaye mu, ba tare da na ga fuskarta ba balle na gano wace ce. Cike da ƙwarin gwiwa na karɓi kuɗi a hannun Firdausi na ɗora a saman cinyar Barira.
"Ga nawa kuɗin sayen bakin, tun kafin ango ya riga ni jin muryar amarya."

"Na gode Aunty!"

Ita ce maganar da ta fito bakin Barira bayan ta damƙe kuɗinta a hannu, tamkar wadda aka ce za a yi wa ƙwace. Dariya aka shiga yi da ihun murna, Na riƙa ta har zuwa ɗakinta, bayan na saka ta yin basmala da shiga ɗakin da ƙafar dama.
Sai da na zaunar da ita kan gadonta, sannan na baro ɗakin da ban gama tantance tsarinsa ba. Saboda ko da wasa ban ji ina sha'awar shiga ba bayan an gama jeren, haka ma duk zaryar da danginta suke yi kawo kaya da gyare-gyare ban bi ta kan ɗakin ba, balle na ga kalar kayan gadonta da su Yaya Maimuna suke gulma.

Su Firdausi suka ja ni ɗakina, haƙuri suka shiga ba ni sosai irin wanda ya sa na ji kuka ya zo mini babu shiri. Sannan suka tafi kowa ya watse aka bar ni daga ni sai yarana da amarya Barira a cikin ɗakinta.
Ƙarfe goma da mintuna na ji Mukhtar yana rufe gida, sannan ya turo ƙofar ɗakina ya shigo kamar an jefo shi. Ledar da ke hannunsa ya ajiye a kan bed side, sannan ya zo daidai kaina yana faɗin,
"Yanzu ke abin da kika yi mini a gaban abokaina kin kyauta kike gani? To wallahi duk abin da kike taƙama da shi na fi ki."

"Ni ce shaida! Domin kuwa ko rashin adalcin da ka fara da shi; ya nuna mini zahirin wane ne kai a yanzu ko da ban san ka a baya ba."

Amsar da na ba shi kenan ina ƙoƙarin tashi daga kwanciyar da nake. Duk da a raina ba na so mu yi abin da zai raba mana hali, gudun amarya ta jiyo mu.
"Idan ma don ban ba ki kayan da aka ce ana bayarwa ba ne kike son tozarta ni; to ki yi duk abin da za ki iya. Amma wallahi ba zan ƙara wa mai ƙarfi ƙarfi ba, don kina da kuɗin albashinki, wanda kaɗan ne za a ƙara a kan wanda nake karɓa. Kuma ina da hidimar da ta fi zama dole fiye da saya miki kayan dannar ƙirjin."

A harzuƙe na ce da shi, "To da ba ka saya ba sai me!? Ai dai ba ka gan ni a wulaƙance ba ko?"
"Kanki ake ji! Ga kazar amarya nan ki sa albarka. Ni na shige! Kuma idan an ga ban fito da wuri ba kada a neme ni, don ba ɓata zan yi a cikin gidan ba."

Sai da na fashe da dariya sannan na ce, "Allah na tuba ka yafe ni! Wane dare ne jemage bai gani ba?"

"Na ranar mutuwarsa!"

"Idan haka ne kuwa babu abin da zai sa na damu da barazanar da iyakacinta a baki. Da ma a ce kai namijin gaske ne mai iya gamsar da mace ya cire mata kwaɗayin wasu mazan; da zan ji zafin aurenka da wannan daren da kake tinƙaho yanzu. Amma abu kamar lagwani ranar me za ta yi mini balle na ji haushin masu zuwa aro?"






Laaaa!😱🤭🏃🏻‍♀️







D. AUTA CE✍🏼


*ABOKIN AIKINA*


*@HADIZA D. AUTA*


*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*


*TALATIN DA BIYU.*

"Iyyeeeee! Ke Ni kike faɗa wa magana irin haka mai kama da cin zarafi?"
"Ina da tabbacin babu ƙarya a cikin maganganun da na faɗa. Kai ma idan za ka yi wa kanka adalci; ka san ƙarin aure na masu cikakkiyar lafiya ne ba irinka ba. Don na sha faɗa maka mace ɗaya ma ta yi maka yawa, amma ka kasa ganewa. To ka yi auren ga ka ga amaryar, muna daga gefe mu ga kalar wainar da za a toya, don duk wanda bai ji bari ba ai ya ji hoho!"
Takowa ya yi a fusace ya tsaya gabana, nuna ni yske yi da hannu tamkar zai kai mini duka, ƙwafa ya yi ya nufi hanyar fita ɗakin yana faɗin,
"Idan ma burinki ɓata mini daren amarci ne; to haƙar ki ba za ta cim ma ruwan ba."

Ya fice tare da bugo mini ƙofa da ƙarfi. Harara na aika wa ƙofar sannan na miƙe da nufin rufewa da makulli. Sautin maganganun da na ji ya sa na yi riƙe hannun ƙofar ba tare da na bar wurin ba.
"Don Allah ki yi haƙuri, wallahi ba hirar arziƙi ce muka yi ni da ita ba."
"Ka je kawai ka kwanta ni ina nan, don wallahi ba zan bari ka taɓa jikina ba bayan ka gama holewa da uwargidanka."

Dariya ta suɓuce mini duk da mugun haushin maganganun amarya da na ji. barin ƙofar kawai na yi na kwanta, zuciyata cike da tunani tare da tausayin Barira a raina.
Saboda ko maƙiyiyata ba na mata fatar auren Mukhtar, balle irinta da tashi ɗaya na fahimci rawar kan da take yi a kansa.
Ban san ya suka ƙarge ba saboda addu'o'in baccin da na karanta, sun yi tasiri wurin mantar da ni komai a dalilin nannauyan barcin da ya ɗebe ni.

Da safe na tashi da wuri na shirya mana breakfast, saboda na taras da doya da kiret ɗin ƙwai har biyu a kitchen. Hakan ya sa na fahimci abin da yake so a yi kenan, Ummu Salma ta taya ni muka kammala.
Namu muka ci sannan suka tafi islamiyya, na koma ɗakina na kwanta ina huce gajiya. Ba tare da na kalli ƙofar ɗakin amarya ba balle na nemi inda take, saboda maganganun jiya da kunnuwana suka jiyo sun sa na ji ta sire mini. Sannan gargaɗin da Mukhtar ya yi mini ya ƙara tunzura ni na tsaya inda Allah ya ajiye ni.
Misalin ƙarfe goma saura na ji an fara ƙwanƙwasa mini ƙofar ɗaki. Sanin cewa ba su Haidar ba ne; na miƙe jikina babu ƙarfi saboda baccin da ya kwashe ni, a kasalance na buɗe ƙofar.

"Ina kwana Aunty?"
"Lafiya lau!"
Na amsa mata a gajarce, tana wasa da yatsun hannunta ta sake cewa,
"Abin karinmu ya ce na karɓo"
"Ki je Kitchen za ki ga komai a kan table. Na zaci bacci kuke yi shi ya sa ban yi karambanin tayar da ku ba."

Na ƙare maganar ina murmushin yaƙe, "Hmm! Aunty ai tun ɗazu idonmu biyu."
"Ok tom! Ki je ki ɗauka."
Ta juya na bi shamulallen ƙugunta da kallo ina ƙumshe dariya, saboda yadda take ƙoƙarin karkaɗa shi ta ƙarfi amma ko motsi babu balle su taka rawar disko.

Wanka na faɗa sharp-sharp na shirya cikin riga da wandon atamfa, wadda ta zamo half gown da falalin wandonta ya baje a ƙasa. Na kafa ɗaurin ture ka ga tsiya na koma kitchen da zummar ɗora girkin rana. Shigowar su Ummu Salma suna ihun Mama mun dawo, ya sa na yi saurim ƙwala wa Haidar kira. Saboda shi ne mara jin cikinsu kuma ba na so ya ce zai je ɗakin amarya, gudun ya gano abin da ya fi ƙarfin idonsa.

Ya gida suka fara yi mini, sannan na ce da su kada wanda ya shiga ɗakin amarya. Su jira idan ta fito su gaishe ta, ficewa suka yi bayan sun tabbatar mini da ba za su je ba.
Hankalina a kwance na kammala girkin cikin ɗan lokaci, zuba wa tsuntsayen soyayya na yi a kula na ajiye gefe. Sannan na zuba namu a tire ɗaya muka baje tsakiyar kujeruna.
Muna tsaka da cin abincin, na ji sallamar wani a bakin ƙofar falonmu. Haidar ya amsa ya miƙe ya isa inda mai sallamar da gudu, domin ya ji mana abin da ya kawo shi.

"Ka faɗa wa babanka ga ni na zo!"

"Mama Nura mai Chemist ne yake neman Abbanmu!"

"Nura kuma? To waye bai da lafiya a gidan nan?"

Tambayar da na yi kenan a zuciyata ashe ta fito fili. Tsintar muryar Barira na yi bayan ta buɗe ɗakinta tana faɗin,
"Romiyo ne yake zazzaɓi! Shi ne ya kira likita domin a zo a yi masa allura."

'Romiyo?'

Na jefi kaina da faɗar sunan a zuciyata, a take na faɗaɗa fuskata da murmushi na ce.
"Allah Sarki! Haidar je ka ce da Nuran ya shigo"

Bayan na gama ba shi umurnin na ci gaba da cin abincina. Haidar a gaba Nuran yana bayansa suka doshi ɗakin Barira, na yi hanzarin cewa da shi,
"To kai Alhaji zo mu kammala cin abincin kai muke jira." Saboda ba na so ya shiga ɗakin.
Ya dawo ya zauna muka ci gaba da cin abincinmu, Barira ta juya ta koma ɗakinta ta bar ni da mamakin ciwon Mukhtar a farkon daren amaryarsa. Saboda sanin da na yi masa shekara yake yi bai kwanta ciwo ba, domin Allah ya wadata masa lafiya ba kamar ni mai yawan laulayin ciwo kala-kala ba.

Mintuna a tsakani Nuran ya fito Barira a bayansa yana faɗin,
"Don Allah kada a dame shi a bar shi ya huta sosai."
Muƙus na ga ta yi ba tare da ta tanka masa ba, alamunta ya nuna a zahiri ba ta ji daɗin maganarsa ba.
Kitchen na ga ta wuce, ɗan lokaci a tsakani ta fito da kulolin da na saka musu abinci, ta yi ɗakinta tare da rufo ƙofa. tun daga lokacin ban sake jin motsinsu ba daga ita har shi.
Baƙinta ma da ke zuwa haƙura suke yi su tafi idan sun gaji da zama, saboda ta ƙi buɗe ɗaƙin balle ta fito ta bi kan 'yan taya ta murnar auren. A taƙaice dai ranar Mukhtar bai fito ba har sai da aka yi sallar Asr. Sannan ya fito dafe da ƙugu yana tafiya tamkar mai tata, sai nishi yake yi yana faɗin,

"Wash! Allah! Wayyo-wayyo!"

Barira tana riƙe da hannunsa suka yi ɗakinsa tana jera masa sannu. Haka kawai na nemi annurin zuciyata na rasa, sanadin abin da na gani da idona; ya tabbatar mini da sun kwana suna shan ganimar aure. Tuƙuƙin baƙinciki ya taso mini nan take ya rufe mini zuciya.
Volume na ƙara wa tv'n da nake kallo, dumar waƙar SAI DA KE ta karaɗe falon gabaɗaya.

Abin da ya so ba ni dariya, lokacin da suka je bakin ƙofar ɗakinsa ya dakatar da ita a nan. Ban ji me ya faɗa mata ba, na hango ta tsaye rungume da hannu a ƙirji. Na ƙara ɗora idanuwana a kansu ba don na so ba, ya shige ɗakin shi kaɗai yana jinjina mata hannu sama alamun ta yi haƙuri, kawai ya kulle ƙofarsa dafe da ƙugunsa. Ya bar ta a nan bayan ya gama yi mata dariyar yaƙen kamar an yi masa dole.
Wani juyi ta yi tamkar ta kifa tana fisgar jiki ta faɗa ɗakinta ta rufe ƙofa da ƙarfi. Ajiyar zuciya na sauke tare da kashe tv'n na miƙe kamar wadda aka tsikara, na fito tsakar gidanmu domin na shaƙi iska mai sanyi.
Safa da marya na shiga yi a tsakar gidan saboda na rasa me ke mini daɗi a lokacin. Sallamar wasu mata biyu ya sa na shiga natsuwata tare da amsa musu sallama. Wani kallo suka bi ni da shi a lalace suka gaishe ni kamar ba su so suka shige ciki.
Sosai na ji zafin abin da suka yi mini, amma dole na danne don ba zan bari na fara takun-saƙa da ita tun yanzu ba, balle masu zuwa wurinta su tafi. Zama na yi a kan kujerar robar da ke wurin ina nazarin abin a raina.
Har su Ummu Salma suka dawo ban tashi daga zaman da nake yi ba, umurnin cire kayan makaranta na yi musu suka yi ciki da gudu. Mintuna a tsakani na miƙe na bi bayansu zuciyata a cunkushe raina babu daɗi.

"Ke Ruky ina ganin jalala! Ke ko dare ɗaya tak! Amma Romiyo ya susuce tamkar ba namijin kirki ba?"
"Ga shi kuma ke a nan ɓangaren ba ki da mutunci! To ki dai yi a hankali, kuma ki tuna kina da kishiya ba ke kaɗai ba ce a gidan."
"Babu ruwana da kowa wallahi kaina na sani, idan ban ga haske ba kuma na tayar da tubana don ba na iya juriya gaskiya."
"Ba ki da mutunci Barira!"

"E ɗin, a bar ni a hakan! Wa ya ƙi daɗi?"

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login