Showing 24001 words to 27000 words out of 121208 words
kin cika kula ki kai musu, kuma duk wanda ya shigo kina ba shi saɓanin yanzu da kika daina."
"Ikon Allah!"
_Ita ce kalmar da ta fito bakina ban shirya ba, saboda mamakin zancen da kuma rashin adalcin da suke ƙoƙarin yi mini. Sai da na sauke ajiyar zuciya sannan na ce,_
"To wallahi Sajida ba daga ni ba ne. Shi yake siyo shinkafar kaɗan shi ya sa nake ba su kaɗan. Amma da a ce zai siyo wadatacciya zan ba su kamar yadda na saba, wataƙila ma a fi haka musamman yanzu da ba komai nake iya ci ba." Na ƙare maganar cikin damuwar da ta bayyana kan fuskata.
"Ki ƙyale su Aunty kowa ya yi nagari don kan shi."
_Amsar da ta ba ni kenan a ƙoƙarin ta na kwantar mini da hankali, kuma sosai ta shiga jikina. Saboda zallar gaskiyar da ke ciki tare da jin daɗin fahimtar da ta yi mini._
_Da ya dawo ban ɓoye masa komai ba na sanar da shi, saboda ya yi wa abin tufƙar hanci ta hanyar sauya awon da yake yi domin a samu zaman lafiya. Amma fitittike wa ya yi ya shafa wa idonsa kwalli, a kan cewa; konon shinkafar shi ne daidai ƙarfin shi. Na yi ta so na nuna masa illar ƙaramin awon da matsalolin da zai haifar mana a nan gaba, amma ya nuna mini ya fi ni sanin komai da tsarin rayuwa. Dole na ƙyale shi a yadda yake so don ba ni da ikon saka shi dole, musamman da na ga ya fi ni son dangin shi amma bai ji kunyar yin abin da yake so ba._
_Haka muka ci gaba da tafiya babu jituwa tsakanina da mahaifiyar shi da ƙannen shi, har zuwa lokacin da cikina ya yi wata tara haihuwa yau ko gobe. Wanda a lokacin ya karta mini wani gagarumin laifin da ya so katse igiyoyin au..._
Zuuuu! Shi ne sautin virbration kiran da ke fitowa a cikin wayata saboda tana silent. Wanda ya dawo da mu daga duniyar waiwayen bayan da muka lula daga ni har Amina, wadda ta yi luf tana sauraro na ko motsin kirki ta kasa yi.
Da hanzari na ɗauki wayar saboda ganin sunan Baba Ali ɓaro-ɓaro a jikin fuskar wayar. Gaishe shi na fara yi cikin mutuwar jiki da sanyin murya, bayan fargaban da nake ciki a kan kiran na shi. Wanda ya haifar mini da bugun zuciya da sauri da sauri, kafin na fara jin maƙasudin kiran cikin faɗa da ɗaga murya.
"Mijinki ya kawo ƙarar ki wurina, a kan abubuwan da kike yi a wurin aiki. Waɗanda bai kamata gare ki ba, a matsayinki na matar au..."
"Wallahi Baba ƙazafin da ya saba ne kawai babu gaskiya a ciki. Burin shi kawai na daina aikin nan bayan kuma shi ma yana rufa masa asi..."
Amsar da na ba shi kenan cikin muryar kuka saboda tsabar jin haushin abin da Mukhtar yake yi mini. Shi ma ya tare hanzarina yana faɗin,
"Ko ma dai mene ne ki ji tsoron Allah a matsayinki na matar aure. Don kin san hukuncin matar da ke cin amanar aure, don haka ki kiyaye. Allah ya ƙara miki haƙurin zama da shi tun da Habi ta zaɓar miki zaman. A tunaninta irin wannan zaman ya fi alheri da zaman ki bazawara."
Hawaye na goge a kan fuskata sannan na ce, "Don Allah Baba ka yi haƙuri. Wallahi ba na ƙaunar Mukhtar a rayuwata kuma na tsane shi."
"Ki yi haƙuri Allah yana tare da ke."
Daga wannan maganar da ya katse kiran, sauke wayar na yi daga kunnena ina zuƙar majinar kuka. Kayana kawai na haɗa a jaka na miƙe na fice daga offis ɗin, ba tare da na yi wa Amina sallama ba saboda ƙunar da zuciyata ke yi.
Hmmmm! ABOKIN AIKINA fa rikici ne daddale a cikin shi yasin😅
D. AUTA CE✍🏼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
_*Littafina free ne ban yarda a sayar da shi ba, ko a juya shi ta wani ɓangare ba tare da izina na ba😒*_
*LAMBA SHA UKU.*
Karaf na ci karo da mutum ba tare da na tantance wane ne ba. Amma duk da hakan ban jira komai ba na yi gaba, balle na bai wa wanda muka yi karon da shi haƙuri.
Idona a rufe na fice ma'aikatar tamkar na kifa. Jefa ƙafafuwana kawai nake yi, a dalilin duhun baƙincikin da ya yi mini rumfar da ta lulluɓe mini zuciya.
Ban yi tsayuwar jiran adaidaita ba na ci gaba da jefa ƙafafuwa cikin sauri, har na yi katarin ganin wata za ta wuce babu kowa a ciki na tare. Luf na yi bayan na zauna ina sauraron waƙar da ke tashi a cikin daidaitar. Wadda nake jin ta har tsakiyar zuciyata, domin ta ƙara rura wutar tsanar Mukhtar a cikin zuciyata. Saboda duk wani baiti da ke fita a cikin waƙar, ina alaƙanta shi da ni kuma ina ji a raina tamkar ni ce nake furzo su daga bakina zuwa kunnen Mukhtar.
'Ka rusa soyayyar da zuciya ke ma.'
'Na daina ƙaunar ka zan iya rantse ma.'
'Ba wata alfarmar da za na iya yai ma.'
'Ka naɗe tabarmar kunya ka je Allah ya yafe ma.'
'Maƙaryaci babu ni babu shi.'
'Tuntuni mun raba hanya da shi.'
'Ko da tsautsayi ya gifta.' 'Ni ba ni so nai gamo da shi.'
Waɗannan baitukan ba ƙaramin tasiri suka yi wa zuciyata ba, domin sun ƙara tunzura ni na kai maƙura a kan abin da na kitsa wa zuciyata.
Wanda na gama amanna da cewa shi ne abin da zai kawo ƙarshen zaman yaƙin da nake yi da Mukhtar. Har aka kai ni ƙofar gidan mai adaidaitan bai canza waƙar ZO MU SASANTA ba tamkar da gayya.
Jikina yana rawa na biya shi kuɗin shi na nufi ƙofar gidan, ganin shi a buɗe ya tabbatar mini da su Ummu Salma suna nan. Afujajan na faɗa falon da ƙudurin na aiwatar da nufina, sai ga shi na yi turus babu shiri saboda Ummata na gani zaune a falon cikin yarana.
Har a raina ban ji daɗin ganin ta ba, ƙarin takaicin kuma ƙofar ɗakin Mukhtar a rufe alamun bai dawo daga aiki ba. Gani na ya sa su Ummu Salma suka yo kaina suna ihun murna tare da faɗin,
"Oyoyo Mama!"
Fuskata a haɗe na isa tsakiyar falon na zauna babu yabo babu fallasa na gayar da ita.
Ba ta amsa mini ba, sai kallon da na ga tana yi mini ta gefen idona, Domin na kasa haɗa ido da ita. Don ba na so ta katse mini hanzari dangane da abin da na kitsa wa zuciyata, ko da tsiya-tsiys ko ta halin ƙaƙa.
Ummu Salma ta kawo mini abinci na ce ta mayar da shi sai na tashi, sannan suka yi tsakiyar gidanmu suna wasa suka bar mu mu zanta. Kasancewar ba a zuwa makarantar islamiya a ranar.
Ganin hakan ya sa na miƙe zan shige ɗakina da niyyar na yi sallah, saboda ƙarfe biyu da rabi har gota. Umma ta yi hanzarin faɗin "Wurinki na zo Zaituna."
Cikin dakiya na ce "Sallah zan yi lokaci ya tafi."
"Je ki dawo ina jiran ki, duk da ban so na daɗe ba."
Ban iya sake cewa komai ba na shige ɗakina, a gurguje na yi sallar ba tare da na tsawaita ba.
Dawowa na yi na zauna kan kujerar da muke fuskantar juna ni da Umma, Gyaran murya ta yi sannan ta kira sunana har sau uku.
"Zaituna!"
"Zaituna!"
"Zaituna!"
Sai da ta ɗan tsahirta sannan ta ce, "Sau nawa na kira sunanki?"
Cikin dakiya na ce "Sau uku."
"Idan har da gaske ni ce na haife ki kuma na isa da ke, to ki daina kula wannan mutumin daga yau har zuwa abada!"
Shiru na yi ina maimata kashedin da take ƙoƙarin yi mini da MD a zuciyata, wanda nake ji gara ta ɗiga mini ruwan dalma a jiki da ta yi mini iyaka da shi. Zuciyata a soye na goge hawayen da ke kwarara daga idona zuwa dandamalin fuskarta.
"Ba zan iya daina kula shi ba, duk da babu komai tsakanina da shi. Amma a matsayin shi na babba a wurin aikinmu, akwai abubuwan da za su haɗa ni magana da shi ko ba na so. Matuƙar dai ina aiki wurin ba sauya mini wani aka yi ba."
Amsar da na ba ta kenan kafin shiru ya ratsa tsakani, tsawon mintuna ba ta ce da ni komai. Wanda ba na raba ɗaya biyu a kan maganganun da na yi ne take juyawa a ranta.
Kuka na shiga yi marar sauti domin a lokacin ba na iya taɓuka komai idan ba shi ba. Cikin muryar kuka na ji sautinta yana fita daga bakinta zuwa kunnena.
"Na san ina tauye ki Zaituna, amma ni Allah ya sani akwai tunanin da nake yi miki daban, dangane da tarbiyyar 'ya'yanki. Domin sun kai lokacin da suka fi buƙatarki, kuma sun kai lokacin da kike cin moriyar abinki. Ba na so ki bar yaranki a gantale domin kin fi kowa sanin ubansu ba zai iya kula da su kamar yadda kike yi ba. Abu na biyu babu inda za ki je da su matuƙar kina buƙatar zama lafiya a wani gidan auren. Sannan ni ba ni da muhallin kaina balle na kwashe su na riƙe a hannuna. Kuma kin san babu kyatawa idan kika tare gidan Alhaji Ali daga ke har su, saboda ɗawainiyar kan shi ma ta ishe shi balle a ƙara masa da wata, bayan ya gama taki tun ƙurciya har girma. Saboda gidan zumu ba kasuwa ba ce balle a shiga duk lokacin da aka ga dama. Ki yi nazari da kyau zawarci a wannan lokacin da muke ciki ba abu ne mai kyau ba. Idan kika saka wa kanki haƙuri a yadda kike yanzu, a gaba za ki tsinci ribar hakan a wurin 'ya'yanki, a lokacin da ƙafafuwansu za su tsayu."
Ruwan hawayena ya ƙara ɓallewa, domin na san gaskiya ce take faɗa mini. Amma ta kasa gano har yanzu ban mori aure ba, ban san daɗin aure ba balle more wa saduwar aure tsawon shekara goma sha biyu da na yi a gidan Mukhtar. Wanda na canye lokutan ina bautar auren kuma ta sani amma take ta kawar da kai.
'Shin idan ban ƙwaci wuyan hannuna na samu 'yanci a yanzu ba, yaushe ne zan taimaki kaina domin na fita daga wannan bahaguwar rayuwar aure, marar fasalin da nake ciki?'
Tambayar da na jefi kaina da ita kenan kafin na yi jarumtar furta mata cewa, "Ba zan iya ci gaba da wannan zaman ba, domin Allah ma bai ce na yi irin shi ba. Asali ma ya ba ni damar na kai kotu a raba mana auren matuƙar na ji ba zan iya jurewa ba."
"Ana barin halas ko don kunya Zaituna, idan ba ki raga wa Mukhtar saboda yana aurenki ba, za ki raga masa ko don 'ya'yan da ke tsakaninki da shi. Ki yi haƙuri ki bar wa Allah lamarinki, da yardar Ubangiji sai ya kawo miki haske a cikin rayuwarki ta nan gaba. Matuƙar kika saka dauriya kuma kika iyar da ladarki domin ki kai matakin nasararki."
Ban ce da ita komai ba, domin na sani duk yadda zan nuna mata abin da nake nufi, ba za ta fuskance ni ba, balle ta gamsu da ra'ayina mu daidaita.
Nasiha ta shiga yi mini wadda fiye da rabinta a kan na ji tsoron Allah ne, sannan da ƙoƙarin gina mini katangar ƙarfen da take yi a tsakanina da MD.
Har ta yi ta gama ban sake cewa komai ba, raka ta na yi ƙofar gida ta tafi tana goge ƙwalla tare da saka mini albarka. Dawowa na yi na zauna, zuciyata a cunkushe ina tunanin me zan yi na raba kaina da auren Mukhtar.
"Ki gudu kawai!"
Amsar da zuciyata ta ba ni kenan, na nutsu sosai ina nazarin hanyoyin da zan bi na gudun ba tare da wani tarnaƙi ba.
Ajiyar zuciya na sauke saboda kai wa matsaya ɗaya a kan wannan shawarar da zuciyata ta gama ba ni. Amma hakan ba zai yiwu ba har sai ya dawo na fara ta kan shi, idan ya ƙi bin ra'ayina sai na ɗaukar wa kaina matakin gaggawar da ya fi dacewa da ni.
Ranar bai dawo ba sai da dare ya yi sosai sawu ya ɗauke. Ƙarfe ɗaya saura na ji yana rufe gida, na miƙe zumbur tamkar wadda aka tsikari da allura. Na buɗe ɗakina na fito a daidai lokacin da ya shigo falon, hanzarin shan gaban shi na yi ban yi jinkirin komai ba na ci kwalar shi. Cikin matsanancin fushi da kai wa ƙololuwar ɓacin rai na fara faɗin,
"Idan ka haifu cikin uwarka da ubanka ka sake ni yanzun nan!"
Ƙwace kan shi kawai ya shiga yi yana shegen murmushin shi, wanda a koyaushe yake tura mini haushi da shi idan irin haka ta kama. "Shin ba ka ji maganata ba ne? Ka sake ni na ce! Idan har ka haifu cikin uwarka da ubanka!"
Fisge kwalar shi kawai ya yi, sannan ya bangaje ni ya shige ɗakin shi, ba tare da ya ce da ni komai ba balle na san matsayata. Kuka na fashe da shi mai sauti tare da fasa ihu cikin ƙaraji na zube ƙasa ina turmuza tamkar ƙaramar yarinya.
Ban san ya aka yi ba na ji muryar su Ummu Salma a kaina, suna kuka tare da rungumata suna faɗin don Allah na yi shiru. Tausayinsu ya sa na ƙara sautin kukana maimakon na rage kamar yadda suke da muradi.
Mun ɗauki lokaci muna kukan daga ni har su kafin ya fito ya janye su daga jikina, suna tirjiya ya tura su ɗakinsu ya rufe ƙofar ya zare key. Ko kallo na bai yi ba ya koma ɗakin shi ya rufe tare da saka masa key a lokaci ɗaya.
Idona a rufe na miƙe tamkar wata zakanya na yi ɗakina, kayana na shiga haɗawa a jaka maidaidaiciya. Wadda ke ɗaukar kala biyar da wasu tarkacen da ba a rasa ba, sannan na saka abubuwan da zan buƙata dole a jakar hannuna.
Agogon da ke manne jikin bangon ɗakina na kalla, wanda ke bugawa yana nuna ƙarfe ɗaya da minti goma sha shida na dare. Amma ban ji ko ɗar ba wurin janyo jakata na rataya ta hannun a kafaɗata na fito. Cikin ƙunar rai da bushewar zuciya na durfafi ƙofar gidanmu na buɗe, kai-tsaye na fice ina jan jakata ba tare da na ji tsoron duhun daren ba, balle abin da zai same ni.
Wayyo!😨🙆🏻♀️ Don Allah ku ce ta dawo🤦🏻♀️
D. AUTA CE✍🏼
*ABOKIN AIKINA*
*@HADIZA D. AUTA*
*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*
*LAMBA SHA HUƊU.*
Tafe nake ina sharɓen kuka tare da jan jakata har na fita unguwarmu. Babu motsin komai da kowa, garin ya tsit illa karnukan da nake jin kukansu nesa da ni jefi-jefi.
Sai da na yi tafiya mai nisa sannan na fara jin wani ƙugi da gurnani a bayana, cikin sauri na juya tare da dakan luguden da zuciyata ke yi. Ido na zare ina ƙoƙarin tafiya da baya-baya saboda wani Mahaukacin karen da na yi tozali da shi yana zaro harshe. Jefar da jakar kayana na yi cikin matsanancin tsoro na zunduma da gudu. Shi ma ƙaton baƙin karen ya biyo ni aguje yana ta haushi "Wu! Wu!" Tamkar an ba shi kwangilar cinye ni da raina.
Gudu nake yi iya ƙarfina yana bi na da ihu tamkar yana ƙoƙarin kama ɓarauniyar da ta yi gagarumar sata. Cikin sa'a na afka wani gida da na hango ƙofar shi a buɗe. Saboda duka gidajen da ke unguwar a rufe suke ruf, kuma ban yi Hausar samun wata kwana ko lungun da zan ɓoye masa ba.
Sakata na danna wa ƙofar gidan jikina yana rawa, ga numfashina da ke ta hawa da sauka cikin sauri saboda tsabar tashin hankalin da na shiga. Haushin da karen yake yi a bakin gidan yana yagar ƙofar ya sa na