Showing 96001 words to 99000 words out of 121208 words

Chapter 33 - ABOKIN AIKINA HAUSA NOVEL

24 Nov 2024

6417

musamman idan figaggiyar matarsa ta koya masa hankali."

"Ki dai bi a sannu! Shi kawunki ne Uwa ɗaya uba ɗaya da Mahaifiyarki. Za ki rabu da ni amma shi ba za ki iya sauya shi da wani ba."
Umma ta shigo tana 'yar dariya ta ce, "Ke ni fa na fara zargin Mukhtar bai da lafiyar ƙwaƙwalwa. Saboda yadda ya tuɓure yau a kan cewa zai sake ki amma sai an dawo masa da yaransa. Saɓanin jiya da yake kuka a kan a yi haƙuri ki koma ba zai iya rayuwa babu ke a gidan ba."
Ƙirjina ne ya buga dam-dam! Saboda zancen a ba shi yaransa da na ji ya dake ni babu shiri. Gabana yana cigaba da faɗuwa na fara faɗin,
"Ai wallahi ba zan iya ba shi yarana ba, ko babu Barira a gidan balle tana ciki. Saboda jiya kafin a yi rikicin da Maman Taufiƙ ta cire mata kitso, na kama ta da ƙawarta suna aikata harkar banza. Don haka wallahi komai zai faru sai dai ya faru amma ba zan ba shi yarana ba. Daman ba komai ba ne ya sa ya biyo ta wannan hanyar ba; don kawai ya san ba zan iya rabuwa da su ba. To kada Allah ya sa ya sake ni ɗin ya yi ta riƙon takardar sakin har duniya ta jingine."
Na ƙare maganar jikina yana rawa saboda yadda maganar ta shige ni ba kaɗan ba, kuma ta ƙona mini zuciya.

"Ki bar ni da shi! A wannan karon zai gano kowane gauta ja ne."

Zancen Umma kenan tana ficewa ɗakin, Sajida ta sauke ajiyar zuciya ta ce,
"Na ji matuƙar haushin da na gano mijin Maman Taufiƙ ne muka yi karo da shi, ya ɓoye ni bayansa ya hana Baba Mukhtar ya sauke mini ƙaton icen da ke hannunsa. Allah ya tsare matarsa ba ta fito ba da na san ko kashe ni za ta iya yi a lokacin."

"Ki cire wa zuciyarki tsoronta, kawai dai ki yi iya bakin ƙoƙarin ki wurin hana wa kanki shi ko don zaman lafiya."
Abin da na faɗa mata kenan zuciyata ɗauke da damuwa, saboda gabaɗaya na rasa farincikina. Balle walwalar zuciya a kan zancen Mukhtar da na ji na karɓar yara. Don na san zai yi hakan ne kawai domin ya ƙona mini rai, ba don ya damu da su ba. Ni kuma ba zan taɓa bari tarbiyar yarana ta lalace a kan banzan shirmensa da tunanin kansa maras inganci ba.

Haka muka yi ta bitar abin a tsakaninmu, ni, Umma, Sajida da kuma Inna Kulu. Ban samu zuwa aiki ba, haka ma yaran ba su je makaranta, saboda lokaci ya ƙure sun yi latti sosai. Sajida tana gidan har aka yi sallar Zuhur muna tsaka da cin abinci aka kira ta a waya. Fuskarta a haɗe ta ɗaga kiran ba tare da ta yi magana ba. Babu shiri ta miƙe tsaye dafe da ƙirji tana zaro ido waje ta ce,

"Aure!!!?"

Ban san me aka ce mata a cikin wayar ba ta jefar da wayar ta dunƙule tana kuka. Cikin tashin hankali na miƙe na yi kanta a ruɗe ina tambayar lafiya. Su Umma ma suka shigo ɗakin muka rufu kanta da tambayoyi, amma ba ta fasa kukan da take yi ba har da majina.
Da ƙyar muka samu ta sassauta kukan sannan ta ce,
"Rayuwata ta zo ƙarshe! Tun da aka ɗaura mini aure da Aminu mijin Maman Taufiƙ! Wallahi na fi so na mutu da dai na yi wannan aure."

"Innalillahi wa inna ilaihirraji'uun! Ita ce kalmar da na faɗa a bakina hannuna a kai ina zarya tsakiyar ɗakin."

Umma ta fara faɗin, "Haƙuri za ku yi dukanku, saboda ba ku isa ku hana Allah aiwatar da abin da ya tsara ba. Daman can an ƙaddara akwai aure a tsakaninsu shi ya sa hakan ta kasance. Don haka ku daina jayayya da ikon Allah! Ku rungumi haƙuri dukanku ba ku san abin da Ubangiji ya kulluɓe a cikin auren ba."

"Wallahi Umma sai dai na bi duniya ba zan zauna gidan mutumin nan ba!"

"Subhanallah! Ki daina faɗar ire-iren waɗannan maganganun ba su da daɗin sauraro. Ki rungumi ƙaddararki wataƙila hakan alheri ne ba ki sani ba."
Inna Kulu ta faɗa tana ƙoƙarin rarrashin ta da hannu.
"Babu wani alheri a cikin irin wannan auren! Tun da ban son shi, kuma ba da amincewata aka yi ba. Don haka wall..."

Kiran wayarta da aka sake yi dukanmu muka mayar da hankalinmu a kanta. Amma ko kallon wayar ba ta yi balle ta ɗauka tana ta kuka har kiran ya tsinke. Sai da aka ƙara wani kiran sannan na yi jarumtar nufar inda wayar take na ɗauka. Ganin sunan mai kiran ya sa na gano Yaya Maimuna ce take kiran ta.
Cike da tsabar jin haushinta na ɗaga kiran ba tare da na ce da ita komai ba.
"Wallahi duk inda kike ki dawo gida yanzun nan ko na tsine miki albarka. Aure kuma ko kina so ba ki so an ɗaura ke kawai ake jira ki dawo a kai ki gidan mijinki. Sai ki je ki yi auren ke ma ki daina shiga rikicin auren wasu, kina ƙoƙarin ci wa ƙanena zarafi a kan Shegiyar matarsa marar tsoron Allah! To wallahi ko ki dawo gida yanzun nan kamar yadda na faɗa ko na tsine miki albarka, sai ki bi duniya ki lalace gabaɗaya kowa ma ya huta da shegen halinki."

Kashe wayar kawai na yi ina Safa da Marwa a cikin ɗakin rungume da hannuna a ƙirji. Wayar na fara bubbugawa a bakina sannan na ce da Ummata,
"Don Allah Umma ki kai Sajida gidansu ki damƙa wa Mamarta ita hannu da hannu, gudun ta ƙi komawa gidan a ce mu ne muka ba ta ƙofar guduwa."

"Me ya faru?"

Tambayar da Inna Kulu ta yi mini kenan a ruɗe, zama na yi a bakin gadon Umma sannan na ce da su.
"Yaya Maimuna tana yunƙurin tsine wa Sajida muddin ba ta koma gida yanzu ba. Don haka yana da kyau a mayar da ita gudun ta tsine mata a kan banza."

"Lalle kin yi magana mai ma'ana. To bari na watsa ruwa sai mu tafi. Amma ba zan iya shiga gidan ba gudun wata matsala ta biyo bayan hakan."
"Inna Kulu ku tafi tare don Allah! Ke ki shiga da ita har gidan ki miƙa wa Mamarta ita ki fito ko ba ki ce komai ba."

Zancen da na yi kenan cikin sanyin jiki saboda na kai maƙurar ɓacin rai da damuwa. Ban iya cewa Sajida komai ba har Umma ta shirya. Inna Kulu ta shigo ta riƙa hannunta suka fita ɗakin, Umma ma ta fita jiki babu kuzari na bi su baya har ƙofar gida. I ta faman share hawayen da ke ta fareti a kan dandamalin fuskata.

Babu zato sai ga wata adaidaitasahu ta tsaya a ƙofar gidan, Maman Taufiƙ na ga ta fito tana biyan mai adaidaitasahun kuɗinsa. Sajida ta ƙwace daga riƙon da Inna Kulu ta yi mata ta zunduma ihu iya ƙarfinta.
Ni ma ganin ta a lokacin da ban yi tsammani ba; sai da na ji cikina ya murɗa hanjina sun dunƙule wuri ɗaya. Da gudu na koma gidan na faɗa bayi, zawo na dinga kwararawa tamkar zallar ruwa ne kawai nake fesowa shaaaa!






Wayyo🥲








D. AUTA CE✍🏼


*ABOKIN AIKINA*


*@HADIZA D. AUTA*


*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*


*Commenters, masu share, 'yan Allah ya ƙara basira, da masu danno mini sticker's da emoji idan na yi posting, har ma da wanda karatu ne kawai na shi ba ya motsi. Dukanku Allah ya saka muku da mafificin alherinsa. Ina son ku gabaɗaya, kuma ina yi maku fatar rayuwa mai kyau tare da gamawa duniya lafiya.👏🏻*


*LAMBA ARBA'IN.*

Jiki babu kuzari na fito daga bayin, ƙirjina yana dakan luguden uku-uku. Takalman Maman Taufiƙ na hango a ƙofar ɗakin Umma, hakan ya tabbatar mini da har ta shigo gidan, su sun tafi.
Haka kawai na tsinci zuciyata wasai, fargabar da nake ciki fiye da rabinta ya zumame. Daidaita natsuwata na yi sannan na shiga ɗakin, fuskata ɗauke da murmushin yaƙe na fara faɗin,
"Sannu matar mijinta, shi ne za a zo mini babu sanarwa?" Na ƙare maganar tare da zama kusa da ita ina ƙoƙarin karantar yanayinta.
"Ke ce da sannu Maman Haidar! Saboda ke kika yi abin da dole sai na zo ba tare da kin sani ba. Kin ci sa'a ma da ban yi tsuntsuwa na dire saman kanki ba, domin na yi ta tsige miki gashin kai har sai kin gama tattara komatsanki mun juya tare."
Ajiyar zuciya na sauke mai ƙarfi, tamkar an sauke mini ƙaton dutsen da ya danne mini zuciya. Saboda lafuzzanta sun tabbatar mini har yanzu ba ta san wainar da ake toyawa ba.

"Idan ma kin tsige gashin, ke za ki tsinto shi ki dawo ki mayar da shi inda kika gan shi."

Na ƙare maganar ina 'yar dariya, Maman Taufiƙ ta gyara zamanta sannan ta ce da ni,
"Wallahi ko kaɗan ban ji daɗin abin da ya faru ba, abin haushin ma ban san da rikicin ba kwata-kwata sai yau. Saboda kwana biyun nan duka wani masifaffen bacci nake yi tamkar wata 'yar maye. Sai yau da safe Amini yake sanar da ni wai ba kya gidan, ashe shi ma sun zo biko gidan nan Umma ta hana su ke? To ni dai don Allah kada ki ba ni kunya. Don na gama cika baki a kan zan shawo kanki, na rarrashi Umma ta yi haƙuri ki dawo gidanki ko don yaranki."

"To ki furzar da abin da kika cika bakin da shi Hajiyata! Don ni kam sai dai idan gawata za a sake kaiwa gidan Mukhtar. Daman can zaman Umma nake yi a gidan ba don ina so ba, yanzu kuma tun da ita ma ta gaji ni me zai sa na koma?"
Na ƙare maganar idona a kanta, tagumi ta cire sannan ta yi shiru na ɗan lokaci. Mintuna a tsakani ta ce,
"Yanzu ke za ki iya barin yaranki a hannun waccan ballagazar yarinyar, wadda ko ita yana da kyau a ce har yanzu ba a gama ba ta tarbiyar ba. Yanzu haka da zan fito na gan ta ƙofar gidan tana siyen kifin Malami Sabo, ga wani garjejen ƙato sai hira suke yi tana cin kifin a gabansa tamkar wani ɗan gidansu."

"Tsuntsun da ya ja ruwa, shi ruwa kan doka! Saboda ban ci nanin ba, nanin ba za ta faɗo mini ba. Shi ya ji zai iya da ita ne shi ya sa ya nemi a kassara ni saboda ita. Wai har ni za a turowa 'yan daba da wasu karuwai har gida su dake ni, sannan shi don bai san darajar kansa da ta wanda yake tare da shi ba; ya ba da ƙofar su halaka ni don bai da asara. To na bar masa gidan kenan har abada, daman can kamar a saman ƙaya nake zaune ba don ina so ba."
"Ban gane ba! Kina nufin wasu suka zo har gidan za su dake ki? To me kika yi musu?" Murmushi kawai na yi mai sauti ina kallon ƙwayar idonta, sannan na miƙe na fice ɗakin tare da faɗin,
"Ni dai jira ni na kawo miki ruwa ki sha, tun da kin saka mu zuba daga zuwan ki tamkar 'ya'yan kanya."
"Dole ne ai! Don haka ki je ki dawo a yi ta ƙare, haƙuri za ki yi ki koma tun da kin saba da halinsa."
Ruwa na dire mata da kunun ayar da Umma take sayarwa, sannan na zauna ƙasa ina faɗin,
"Allah dai ya ƙara shiga tsakanin nagari da mugu. Amma ni kam na kammala rayuwa gidan Mukhtar daga wannan karon."
Sakato ta yi tana kallon na ba tare da ta ce komai ba, sannan ta miƙe tana gyara zaman jakarta ta ce,
"To ni zan tafi! Tun da zuwan nawa bai da wani amfani. Idan Umma ta zo ki ce zan dawo ganin ta wani lokaci, amma ke ko a hanya na gan ki ba zan nuna na san ki ba."

Na miƙe ina faɗin, "Ya za ki tafi ba ki sha ruwan ba?"
"Ba zan sha ba!"
Tana ƙare faɗar hakan ta fice tana saka takalminta. Har ta yi gaba ta juyo tana faɗin, "Ke! Ji na manta ban tambaye ki ba! Na ga 'yar gidanki a hargitse da na zo, me ya same ta?"

"Aljanunta ne suka tashi. Shi ya sa su Umma za su kai ta gida." Na ƙare maganar ina murmushi.

"Allah Sarki! Ki ce ita ma tana ciwo irin nawa? Kai! Allah ya yaye wa mutane wannan lalura."
Cikin sanyin murya ta yi magana, na amsa da "Amin" cikin sanyin jiki da na muryar duka. Saboda jikina ya ba ni ba ta san komai da ke faruwa ba, tun daga tsige kitson Barira har wannan badaƙalar auren da Amininta ya rikito. Haka kawai na ji tausayinta ya kama ni, saboda sanin duk ranar da ta ji wannan labarin; zuciyarta ma za ta iya bugawa ta mutu faraɗ ɗaya, balle tashin hankali ko damuwar da za ta shiga sai ta fi gaban kwatance.

Ganin damuwa a kan fuskata ya sa ta yi gaba tana faɗin, "Ke ai yanzu na samu lafiya sosai saɓanin baya da nake ɓacewa ba a san inda nake ba tsawon kwanaki. Ni ma ba na sanin ina nake sai dai na tsinci kaina a tsakiyar daji babu komai da kowa sai kukan tsuntsaye. Amma tun da muka bar gidan da muka fara zama farkon aurenmu, shi kenan matsalar ta kau sai dai lokaci bayan lokaci hargitsattssun kayan suna motsawa."

"To Allah Ubangiji ya yaye muku gabaɗaya, ya kawo sauƙi da salama a cikin lamarin da rayuwarku gabaɗaya."

"Amin Ya Allah! Ke ma ya sa ki dawo mana, don ba za mu yarda ki suɓuce ba!"

Ta ƙare maganar da yar dariya bayan ta juyo muna kallon juna, saɓanin tafiyar da take yi tana gaba ina bayanta har ƙofar gida. Taka mata na yi har muka je bakin titi, sai ga su Umma cikin adaidaitasahu har sun yi gaba na ga mai adaidaitar ya ja ya tsaya. Su Umma suka fito Inna Kulu tana cewa da ni,

"Ta zo ya kai ta mu sai mu ƙarasa kawai!"

Tare muka nufi wurin tana faɗin, "Sai wani murna kike yi kin zo gida kina 'yanmatanci. Ni na manta ma ban ga su Ummu Salma a gidan ba, ina suka je?"

"Suna gidan ƙanwata ɗiyar Kawuna."

"Allah Sarki ki gaishe mini da su, yawwa ma har na tuna.."

Ta fito da wata leda a jakarta ta miƙa mini tana faɗin, "Ki ba su don Allah! Kwanan nan gabaɗaya a hargitse nake ji na wallahi."
Karɓa na yi su Umma suka taya ni godiya ta shige tana cewa Umma, "Zan miki tafiyarki ke kaɗai Umma. Amma don Allah a sassauta kada abin ya yi tsauri ta dawo mana haka nan, don har mun fara kewar ta."

Murmushi Umma ta yi tana faɗin,
"Allah ya zaɓa abin da ya fi alheri."
Daga haka suka tafi muna ɗaga mata hannu har suka yi mana nisa, sannan muka juya tare da su muna hira.

"Gaskiyar magana mijin yarinyar can bai yi mata adalci ba! Don alamunta ya nuna ba ta san komai ba. Saboda yadda ta nuna alhininta a fili a lokacin da ta zo, dangane da yadda ta ga Sajida ta ruɗe sosai tana zunduma ihu. Haƙuri ta dinga ba ta bayan ta gama tambayar mu me aka yi mata. Har muka bar ƙofar gidan tana ta jera mata sannu da Allah ya ba ta lafiya."

Zancen Inna Kulu kenan a lokacin da muke ƙoƙarin shigewa gida,
"Ai duk mutumin da kika gani tare da Mukhtar, ba mutumin arziƙi ba ne. Shi ya sa idonsa ba su yi mini girma ba, balle na fasa sauke musu duk abin da ya fito bakina. Ai dai duniya ce, su yi duk abin da suke so Allah yana jiran su a madakata, domin su karɓi sakamakon abin da duk suka shuka."

Ummu ta ƙare maganar tare da cire hijabinta ta ja buta zuwa bayi. Na ja kujera 'yar tsugunno na zauna, sannan na sauke ajiyar zuciya na ce,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login