Showing 30001 words to 33000 words out of 121208 words

Chapter 11 - ABOKIN AIKINA HAUSA NOVEL

24 Nov 2024

6389

"Ok! Tom da safe za mu koma ki karɓo jakar."

"Ba sai mun koma ba na yafe musu." Na yi hanzarin faɗin maganar don ba na son su yi masa rashin mutunci, domin na fahimci tsagerun mutane ne. Kuma 'yan iska ne ajin farko.
"Za mu koma! Idan ma sun kawo mana rashin kunya sai na haɗa su da jami'an tsaro."

Shiru kawai na yi masa don a ɗan zaman da na yi da shi, na gano mutum ne mai magana ɗaya. Kuma duk abin da ya furta ta tabbata babu sauyi ko da bai yi wa mutum daɗi ba. Jikin jakata na rakuɓe tare da yin tagumi har zuwa lokacin da yaron ya sake motsawa yana kuka.
Wanda ban lura da shi a kan gado ba har sai da kukan shi ya shiga dodon kunnena. Na yi hanzarin miƙewa na riga MD ɗaukar shi, jijjiga shi na fara yi tare da bubbuga bayan shi har ya sake komawa bacci.
MD ya ce na kawo shi ya kai wa mai aikinsu na ce ya bar shi wurina, daga haka ya fice ɗakin bai musa ba. Na lallaɓa na ajiye shi a kan gadon, sannan na zauna ƙasa na ɗora kaina saman katifar gadon. Hannuna riƙe da hannun yaron na shiga nazarin tafiyar da zan yi idan safiya ta waye. A gefe ɗaya kuma zuciyata cike take da fargabar abin da zai faru, idan matar MD ta yi ido biyu da ni a cikin gidanta.
Ban san lokacin da bacci ya yi awon gaba da ni ba, sai bayan na farka idona ya kai kan agogon da ke manne cikin ɗakin. Wanda nake tantama a kan gaske ne abin da na gani ko kuma daman can ba ya aiki. Domin kuwa ƙarfe bakwai saura na gani. Abin da ya ƙara ba ni mamaki kuma; yaron da nake riƙe da hannun shi ba ya kan gadon, wanda alamu ya nuna an ɗauke shi ba tare da na san an shigo ɗakin ba.
Zumbur na miƙe na faɗa toilet na yi wanka agurguje saboda fitsarin da ke jikina har lokacin. Na yi arwala na fito na ƙargame ɗakin da makulli, sannan na yi sallah a gaggauce cike da tsoron kada ina sallah na ji saukar duka.
Na shirya cikin doguwar rigar shaddar da ke cikin kayana, sannan na saka mayafi mahaɗin shaddar ba tare da na shafa ko da mai ba. Jakata na ɗauka na fito daga ɗakin babu shiri na ja baya na rakuɓe, saboda ganin wata dattijuwar mata ta nufo ni da tire a hannunta, wanda nake da tabbacin abinci ne za ta kawo mini.
Kallon mamaki na bi ta da shi har ta shige ɗakin, saboda ganin ta gaishe ni cikin mutunci da sakin fuska tamkar ta san ni. Yaƙe kawai na yi mata a lokacin da ta ce da ni,
"Hajiya ki koma ki karya kafin ki tafi. Yar laɓai ya ce idan kin gama ki same shi waje."
Bayan ta wuce na ja jakata ba tare da na bi ta kan abincin ba. Sauka na yi ƙasa da sauri har da sassarfa cike da burin na fita gidan ko da hankalina zai kwanta, domin na huta da fargaban da nake ciki.

Cikin motar na same shi yana sauraron ƙira'ar sudes daga cikin ayoyin ƙarshe na suratul Rahman. Ban jira ya ba ni umurni ba na buɗe motar na shige ina zarar ido rungume da jakar kayana. Kai-tsaye ya fice gidan ba tare da ya ce da ni komai ba ya cilla motar a kan titi. Sai da muka yi doguwar tafiya muna gaf da shiga unguwar da na baro jakar, sannan ya ce da ni,
"Idan mun kai gidan ki sanar da ni."
Daga haka ya ja bakin shi ya tsuke ni ma ban ce komai ba sai kai da na ɗaga alamu 'To'. Tun daga nesa na nuna masa gidan ya ci birki a daidai ƙofar gidan, sannan dukanmu muka fito ya ce na jira shi a nan. Cikin gidan ya ɗan tura kai tare da ɗaga murya ya fara rafka musu sallama, sannan na ga ya dawo ya jingina bayan shi jikin motar shi yana dannar waya.
"Ku ƙaraso za ku hango motata."

Maganar da na ji ya faɗa kenan a cikin wayar sannan ya mayar da ita aljihu, a daidai lokacin da wani ya fito daga cikin gidan yana ƙare mana kallon sama da ƙasa.
Yana ƙoƙarin yin magana muka jiyo jiniyar motar 'yansanda, a ruɗe na kai kallona ga fuskar MD, cike da mamakin abin da ya sa shi kiran su tun kafin a yi musu zancen jakar.
Ko da na dawo da kallona a kan ƙofar gidan wayam na gani babu mutumin da ya fito gidan balle alamun shi. Yansandan suka ƙaraso wurin suka bai wa juna hannu da MD suk gaisa, sannan wani daga cikinsu ya ce da shi,
"Ya kuka yi da su?"

"A fito mana da su duka idan har sun ƙi bayar da jakar da kayan cikinta a yi musu duk abin da ya dace."
Abin da MD ya faɗa kenan fuskarsa a haɗe tare da rungume hannun shi a ƙirji yana feso iska a bakin shi. Ɗaya ɗan sandan ya fara yi musu sallama kamar yadda MD ya yi a farko. Mintuna a tsakani sai ga maza da mata suna fitowa daga cikin gidan fuskokinsu ɗauke da tsoro.
Sai da 'yansandan suka ƙare musu kallo sannan ɗaya ya ce da su, "Ina jakar wannan yarinyar da kuka ƙwace a cikin gidanku?" Kallon juna suka fara yi kamar ba su san komai ba.
"A gaskiya ranku ya daɗe ba mu san komai dangane da batun jaka ba."
Zancen wata koɗaɗɗiya kenan wadda fuskarta ta gama ƙonewa da bilicin. Maganar MD na ji a fusace cikin ɗaga murya ya ce, "A cikinsu wace ce ta zare miki hajabi?" Idona a kan Ummita na nuna ta da hannu tare da ƙarin bayani kamar haka,
"Ita ce ta cire mini hijabi, wurin kiciniyar cire mini riga jakar ta faɗi a wurin, lokacin da zan fito kuma na bar ta a can, saboda gudun tsira na manta shaf ban bi ta kan jakar ba."
"Minti biyar aka ba ki ki fito da jakar nan yanzun nan."
Wani daga cikin 'yan sandan ya yi maganar tare da nuna Ummita da bakin bindigar da ke hannun shi. Ummita ta fara zarar ido tana nuna kanta cikin wayancewa da ƙoƙarin zare kai ta ce,
"Ni ban ɗauki jakarta ba, sai dai idan a cikinsu wani ya ɗauka ban sani..."
Bahagon marin da wani ɗan sanda ya kwaɗa mata, babu shi ta fasa ihu tare da komawa cikin gidan da gudu tamkar wata zararriya. Tara-tara 'yansandan suka yi da sauran maza da matan gidan suka jefa su motar shiga-ba-biya, sannan wata 'yar sandar da ke cikinsu ta faɗa gidan a sukwane.

Minti biyar kacal ta fito riƙe da ƙugun Ummita da ke riƙe da jakata tare da wani matashi hannun shi da ya ɗaga hannun shi sama alamun miƙa wuya. Motar aka watsa su duka sannan aka ba ni jakata bayan na buɗe ta gaban kowa, kuma na tabbatar musu da komai yana ciki yadda na saka.
Motar 'yansandan ta fara barin ƙofar gidan tare da mutanen gidan da suka kwasa, kafin ta MD ta bar wurin tare da ni da ke baya na hakimce ina hurar hanci. Amma duk da hakan nan take gumi ya jiƙa mini fuska, zuciyata ta hau bugawa da sauri tamkar za ta fasa ƙirjina ta fito waje.
Saboda hango Mukhtar dumu-dumu a cikin 'yan kallon da suka zagaye mu suna rabon idon ganin ƙwam. Wanda shi ma nake da tabbacin ya gan ni a lokacin da zan shiga motar MD, na yi mamaki matuƙa da ganin shi wurin, tare da ko-in-kulan da ya yi wa ganina ba tare ya nuna ya san ni ba, balle ya ɗauki mataki a kaina ko a kan MD.

Ban dawo natsuwata ba har sai da na ga mun shiga gidajen Sama road, mamaki ya so kashe ni saboda ganin da na yi ya doshi hanyar da za ta kai mu Bafarawa Estate.
'Ina zai kai ni?'
Ita ce tambayar da na yi wa kaina a zuciya, sai ga amsa tiryan-tiryan ta bayyana kanta. Domin kuwa ƙofar gidan Kawu Sale ya ci birki, gidan da Ummata take rayuwa tun da jajayen sawu har yanzu da girma ya kamata.
"Fita ki je! Kuma ki yi mini sallama da Umma!"
Zancen MD kenan a fusace kuma cikin ɗaga murya. Haka na fito tamkar wadda aka kama ta yi wa Sarki ƙarya. Haka na fito jiki a mace na ja jakar kayana da ta hannuna na yi cikin gidan, ba tare da na waigo ba balle na damu da ce masa na gode.
Saboda har raina ban ji daɗin taimakon da ya yi mini ba, tun da har ya kawo ni gidan a maimakon tashar da nake so ya kai ni.
'Tukunna ma wa ya sanar da shi unguwar su Umma da gidan duka?'
Tsaki na ja sannan na faɗa gidan ko sallama babu na yi ɗakin Inna Kulu ina haɗe fuska. Ummata da Inna Kulun duk suna tsakar gidan amma babu wanda na yi wa magana. Saboda tsabar mugun haushin da MD ya cusa mini a zuciya, ji nake yi tamkar na kama da wuta na ƙone ƙurmus kowa ma ya huta.
Ina ji lokacin da wani yaro ya shigo yana sanar da Ummata ana sallama da ita waje. Ban san ya aka yi ba ni dai na ji ta shigo tana balbala faɗa tamkar ta ci babu.
Sai ga ta cikin ɗakin tamkar an jefota, ba ta yi ƙasa a gwiwa ba kawai ta fara kai mini duka da hannu bibbiyu tana kuka. Da ƙyar Inna Kulu ta taɓe ni a hannunta bayan ta gama jibga ta son ranta har da gwabra kaina a bango.
Ban haushin abin da ta yi mini ba, domin ba na tantama a kan ta yi hakan ne kawai saboda ta huce haushin da na ba ta a lokacin, wanda ni ko kaɗan ban ji dukan ba, don zafin da zuciyata ke yi ya fi dukan da take yi mini linkin.
Inna Kulu ta fitar da ita daga ɗakin tana haki, tare da jifa ta da miyagun maganganun da suka tsaya mini a zuciya. Wanɗanda suka saka ni sabon kuka tare da yi wa Mukhtar Allah ya isa ta fi dubu, saboda shi ne ya shiga tsakanina da ita, kuma sanadin shi ne ta fara kyara ta, tare da jifa ta da miyagun kalamai munana, a duk lokacin da rigima ta haɗa ni da shi.

'Ina mafita?'
Tambayar da na yi wa kaina kenan bayan na gama naɗe maganganun Umma a kwanyata. Domin babu komai a cikinsu sai muguwar fata gare ni, a kan muddin ban koma gidan Mukhtar na ci gaba da zaman 'ya'yana ba.





Hmmmm! Ana dara ga dare ya yi



*ABOKIN AIKINA*


*@HADIZA D. AUTA*


*SADAUKARWA: DAUGHTER ANUP*


*LAMBA SHA SHIDA.*

Daga nan ɗakin da nake ina jiyo sautinsu ita da Inna Kulu tar-tar a cikin kunnuwana. "Haba Kulu! Shi kenan kullum abu ɗaya za a dinga yi? Har yaushe Zaituna za ta gano abin da nake lurar da ita? To ni kam a wannan karon, wallahi zan fitar da wuyan hannuna a cikin duk abin da ya shafe ta. Ta je ta yi duk abin da take so tun da ta isa da kanta da rayuwarta, amma wallahi ba zan zauna da ita cikin gidan nan ina ganin wulgawar ta ba. Don duk lokacin da na tuna ta kashe aurenta ta bar 'ya'yanta a wulaƙance sai na ji baƙinciki."
"Ki yi haƙuri Habi, tun da dai hannunka ba ya ruɓewa ka yanke shi ka jefar." Zancen Inna Kulu kenan cikin tausasa murya a ƙoƙarin ta na tausar Ummata, daga mugun fushin da ta shiga tana ta feso hayaƙin maganganu masu nuni da zallar ɓacin ran da ta shiga, sannan kuma masu kama da yi mini baki a fakaice.
"To ke Kulu sau nawa mutum ya sa aka cire masa hannun aka jefar? Ai sai dai idan ba ta kama ba. Don haka ta tashi ta koma gidan mijinta yanzu tun muna shaida juna. Idan kuma zaman gidan take so ni zan bar mata gidan ta zauna, amma ba za mu jeru ni da ita ba"

"Ba za ta zauna gidan nan ba, sai dai ta koma gidan Alhaji Ali tun da daman can shi yake ɗaure mata ƙugu tana iskanci."
Maganar Kawu Sale kenan da na tsinkayo muryar shi a sama alamun shi ma ya ɗauki zafi da ni.
Hawayena na share sannan na miƙe ina gyara zaman mayafin da ke jikina, na rataya jakar hannuna, na ja ta kayana na fito ɗakin.
Ƙofar fita gidan na nufa ina sharɓen kuka ba tare da na ce da su ƙanzil ba, "Wallahi muddin kika fita gidan nan a yanzu sai na tsine miki albarka, matuƙar ba gidan Mukhtar za ki koma ki rungumi 'ya'yanki ba."
Turus na yi babu shiri na ja na tsaya, domin a raina babu zancen komawa gidan Mukhtar har abada. Inna Kulu ta zo har inda nake ta karɓi jakata tare da riƙo hannuna muka koma ɗakinta.
Nasiha ta fara yi mini cikin kwantar da murya, tana ƙoƙarin fahimtar da ni muhimmancin yi wa Umma biyayya, da gudun lalacewar tarbiyyar 'ya'yana da take yi. Wanda abu ne a bayyane ko ni na sani Mukhtar ba zai iya ɗora su a kan tarbiyyar da na ba su ba. Domin zai iya dawo da hannun agogo baya kamar yadda na sha yaƙi da shi a kansu, kafin komai ya daidaita ya daina mayar mini da 'ya'ya kishiyoyi. Saboda duk wani aikin da ya dace mata ta yi wa mijinta idan aka cire kwanciyar aure, to shi yake saka su ba tare da ni ya damu da ni balle ya ce na yi masa. A kan haka mun yi faɗa ya fi a ƙirga da ƙyar na samu ya daina, saboda ƙaƙƙarfar iyakar da na yi masa da yarana.
Da wannan tunatarwar Inna Kulu ta samu kaina na rage kukan da nake yi, saboda matuƙar na ce zan tsallake na watsar masa da su, to babu makawa sai ya dawo da bara bana. Idan kuma hakan ta faru to babu amfanin nema wa kaina 'yanci bayan na wargaza tarbiyyar yarana.
"A ce.. ya kawo.. su idan.. na... tashi mu koma.. tare da su..."
Maganar da na faɗa kenan cikin ajiyar zuciya da shesshekar kuka. Domin jikina ya yi sanyi ƙalau musamman da na tuno lokacin da ya rufe su a ɗaki suna kuka, ba tare da ya damu da rarrashin su ba balle ya nuna musu tausayi irin na Uba.
"Tun da sassafe yau ya kira Ummarki yana sanar da ita ba ki kwana gidan ba, shi ma bai san ba ki nan ba har sai da ya zo yi miki ina kwana sannan ya gano ba ki gidan."
Murmushin takaici na yi sannan na ce, "Idan har da gaske ya san ban kwana gidan ba, to dole ne a ce yana sane na fita ko kuma a kan idon shi. Idan kuma har bai san ba na gidan ba har sai da ya zo yi mini ina kwana kamar yadda ya ce. To bai da masaniyar lokacin da na fita balle ya san gidan na kwana ko ba gidan ba. Abu na ƙarshe kuma ni rabon ina kwana ta haɗa ni da shi; na yi masa ko shi ya yi mini an fi shekara uku ko huɗu. Domin ko sallar asubu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login