Showing 102001 words to 105000 words out of 116554 words
yace "next friday xaki min bayanin ma'anar kunyar nn da kika ji idan an kawo min ke gidana" kwace kanta tayi da gudu ta fice daga dakin ta nufi na su, kwata kwata bata san me ke faruwa gidan ba, taga dae ana ta siye siyen kayan abinci, ta kuma ji wae Anty Safiya ta fita Dubai siyayya, kusan kullum kuma sae sauran Aunties dinta sun tafi kasuwa amma bata san me xa ayi ba kuma bata tambaya ba, bbu wanda ya gaya mata kuma, dakinsu ta shiga taga wasu ubansun lace kusan kala takwas duk iri daya red da ratsin silver da ash a jiki, da gani anko ne, snn ga atamfofi ma duk iri daya biyu kadae ne daban, juyawa tayi cike da son sanin me ke faruwa gidan nasu ta fita ta nufi dakin Mami, xaune ta sameta ita da aminiyarta Hajiya fatee suna xuba turarurrukan wuta masu ddin kamshi cikin lafiyayyun kwalaben da aka yi domin su, suka amsa sallamarta, ta karaso kusa da Maminta ta xauna, a hnkli tace "Mami me xa ayi naga ana siyo kaya, Mami ta daga kai tana kallonta kafin tayi murmushi tace "Je ki tambayi yayanki" ta dan yi shiru kafin tace "Me xance masa?" Mami tace "Tambayar da kika min xa ki masa mana" bnda dariya bbu abinda hajiya fatee ke yi, bata kuma cewa komae ba ta mike a hnkli ta fita daga dakin ta koma nasu, Mami tayi murmushi ta ci gaba da abinda take, Hajiya Fatee tace "Allah sarki". Afeefah na kwance dakinsu don ta ki komawa gun yayanmu su Anty baby suka dawo, sun yi Mamakin ganinta a dakin don bacci kadae ke shigo da ita da daddare gaba daya dakin yayanmu take yini duk kayanta ma suna can, gashi kuma sun ga motarsa alaman yana gida, to ko bae nn ma bata shigowa cikinsu, ta mike xaune da sauri tace " Anty wae me xa ayi a gidanmu?"
🌸👩🏻 'Ya mace kyautar Allah👩🏻🌸
By Ashmaad
97____98
Kallonta Aunties din nata suka shiga yi, lkci days duk suka sa dariya Anty Baby ta ajiye ledojin hannunta ta xauna gefenta tace "Je tambayi yayanmu" shiru tayi tana kallonsu kafin ta sunkuyar da kai, Anty sadiya da Jiddah suka dinga dariya, Kmr munafuka ta mike xata bar dakin Anty baby ta kamo hannunta ta xaunar da ita tana murmushi tace "biki xa ayi," xaro ido tayi tana kallon su Jiddah tace "Bikin wa kuma?" Anty baby tace "Bikin ki da yayanki" shiru tayi kmr warce aka dasa a gun tana kallon yayar tata ko kifta ido bata yi, lkci daya tayi apprending abinda Anty baby tace ta fada jikinta ta boye fuska, banda dariya bbu abinda yayyin nata ke yi. Tun daga wnn rana Afeefah ta fara wasar 'Yar buya da yayanmu, duk inda xa su hadu bata bi da taji motsin sa xata shige bayi ta kulle, ya lura da hkn ya daina xuwa inda take ma gaba daya, shi kansa kunyar nata yake ynxu, gyara ssae wata kawar Mami 'Yar nijar ta shiga yi mata sanin auren ta na biyu knn, gyaran da ba a cika son ayi ma budurwa ba ma, kuma ita a tunaninta ae ba budurwar bace ita din, bbu wanda bae yi Mamakin Afeefah a gidan ba ganin ko kadan bata daga hankalinta ba, barin Mami, sae dae kusan duk kunyan 'yan gidan take ynxu, gashi tayi sanyi ko magana bata so, abinci ma sae Mami tayi da gske da ita take ci, ana sauran kwana uku biki Anty Safiya ta dawo shake da lafiyayyun kayan lefen da taje Dubai ta yo na akwatuna saiti uku da kits, kuma a ranan 'yan kaduna suka iso gidan da wasu daga 'yan uwan Mami, dangin Abba dama tuni suka iso, gidan ya cika ssae da mutane, ko ta ina Shirye Shirye ake, occasions uku su Anty Safiya suka shirya, mothers eve, kamu, sae dinner, shima da kyar yayan nasu ya yrda don ya ce baya so, ran da xa a sa Afeefah a lalle tana dakin Mami kwance sun dawo daga saloon da su Anty Jiddah, Fadila ta shigo dakin rike da envelope ta karasa kusa da Afeefah, Mami ta bi ta da kallo tace "Meye wnn" k'asa cewa komae fadila tayi, sae da Mami ta maimaita tambayar snn ta isa gun Mami ta duka k'asa tace "Dr Aliyu ne yace in ba Anty Zainab" mikewa xaune Afeefah tayi da sauri tana kallonsu, Mami tayi shiru tana kallon fadila kafin tace "Ina kika ga Aliyun?" Fadila ta sunkuyar da kai tace "A waya ya kira ni" Mami ta sauke ajiyar xuciya tace "Kai mata" mikewa tayi ta karasa gun Afeefah ta mika mata, a sanyaye ta karba ta bude envelope din ta fito da abun ciki, kudi a rafe ta gani da wata farar takarda, hawaye ya kawo idonta da kyar ta warware takardan ta shiga duba content dinsa, rubutunsa me kyau taga kmr hka a takardan "Ina taya ki murnar bikin ki Zainab, Allah sanya Alkhairi, ya bada xaman lfya da xuri'a dayyaba, ya bada hkurin xama da juna, congratulations Afeefah, Happy married life in advance." Hawaye ne ke sakko mata ssae, ta ajiye takardan tayi kwanciyarta duk jikinta yyi sanyi. Yayyinta na shigowa aka nuna masu kudin suka yi murna ssae da yi masa fatan alkhairi, Anty Sadiya ce ta kirga ta ga dubu hamsin ne, Mami tace "Allah ya saka da Alkhairi" Da yammacin ranan aka yi kamu, tayi kkrin ganin ta saki ranta, tayi kyau ba kadan ba cikin tsadadden less maroon da ratsin silvern da ke jikinta, light make up wata kwararriyan make up artist tayi mata, aka yi komae lfya cikin burgewa, Karfe bakwae saura ta shiga gida ita da su ilham da Aneesah, ko wannensu da sabon ciki jikinsa, wayarta ta dauka bayan ta shiga daki ta kwanta ta nemi nmbr Dr Shariff ta tura masa text kmr hka, "Nagode Dr Aliyu, Allah saka da alkhairi ya baka mace ta gari, ina kuma rokon gafarar ka, ka yafe min plss, nasan na xalunce ka amma ka yafe min ba don halina ba, nasan kai din me hkuri ne," tana kuka ta tura masa text din, daga hka ta rufe ido kmr me bacci. Karfe tara da kusan rabi tana kwance dakin Adnaan ita kadae don bata son hayaniyan gidan, Rahmah ta shigo ta xauna gefenta tace "Anty Zainab yayanmu na kiran ki wae" shiru tayi bata ce komae ba, don rabonta da shi kwana biyar Yau, Rahmah ta mike ta nufi kofa xata fita cikin sanyin murya tace "Yana ina?" Rahmah ta juyo tana kallonta tace "Yana cikin motarsa a waje" Hijab dinta ta jawo a hnkli ta sa ta fita dakin, sae da ta fara sanar da Mami snn ta fita gidan ta kama hanyar gate. Nesa da motar ta tsaya, ya jima yana kallonta kafin ya bude motar ya fito ya karaso inda take ya rungume hannunsa yana kallonta, kin dago kanta tayi har sae da ya kira sunanta cikin sanyin murya, da kyar ta iya cewa "Um" ba tare da ta dago ba still don wani kunyarsa take ji ba kadan ba, murmushi yyi yace "Shknn tunda baxa ki kalleni ba" a hnkli ta dago kai ta kallesa, suna hada ido ta rufe fuskarta da tafin hannunta da sauri, dariya yyi yace "ynxu kuma kunyan yayan naki kike princess" kin cewa komae tayi sae juya masa baya da tayi, yace "uhm xaki gaya min ma'anar kunyan nn jibi" juyawa ta yi da gudu ta shige gida, yyi murmushi ya koma gun motarsa ya shiga ya bar anguwar. Washegari thursday aka yi mothers day, gidan ya cika makil da kawayen Mami da abokan arxiki, Mami tayi Mamakin ganin Mahaifiyar Dr Shariff, ta tarbe ta da kyau sae dae da kunya kuma, a ranan ta bada nata gudunmawan bikin na bedsheet me tsada da turarrukan wuta da na ruwa, Mami ta dinga mata gdya tana cewa Allah bar xumunci, tambayar Afeefah Hajiya Hajaran ta dinga yi, hkn yasa Mami ta lallaba Afeefah da kyar ta yrda ta fito don gaidata cike da kunya da nauyinta, da yamma misalin bakwae aka tafi dinner, Afeefah tayi kyau har ta gaji don wani ubansun lace ne jikinta sea green da head pepper red, an mata make up da ya kara fito da ainahin kyanta, shi ko yayanmu sanye yake da tsadadden shadda fara kal da ya amshi farar fatansa, yasa babban riga, waow ina ma fanz xa su gan sa a wnn rana nasan sae sun yi fall din masa, yayyin Afeefah da kanninta duk lace ja da ratsin ash da silver suka sa, guri ya cika da 'yan uwa da abokan arxiki da suka xo taya murna, can na hango 'yan Khaleesat Haiydar Novels da suka xo taya su farin ciki a gefe daya sae ciye ciye ake baki har kunne suna yaba kyan amarya da ango, ko wannensu ya cakare cikin nasu ankon na net lace sky blue da milk colour da ratsin silver a can filin rawa na hango su Hajiya Jamila, Fati Jaji, Rukayya M inuwa, Maryam Liman, Zainab sani daura, Maryam N Abubakar sae tikar rawa suke bakin rae cikin dangin Amarya, na rike Haba ina kallon ikon Allah, to ko wa ya gaya masu venue din dinnern??? can rumfar da Amarya Zainab da angonta yayanmu ke xaune na hango su Ummee Ibrahim, Shafa'atu Ibrahim Usman, Zaynab lawal da Ummi Salma sae likin 'yan dubu dai dai suke ma amarya da ango baki har kunne, a can wani gefe na hall din na hango 'yan partyn Dr Shariff sae wani tabe baki ake kar dae wae ace basu xo ba duk da nasan ganin kwakwaf suka xo yi ba wae taya murna ba, da alama bbu abinda ya burgesu wajen don ko abinci naga sun ki ta6awa, su Halima Muhammad ne, Ibrahim Sadiya, Humairah ibrahim yusuf, Beaulin Bilmoh, Nafeesat A Muhd, da sauransu duk sun tsuke baki cikin ankon wata atamfar leda 'yan duba daya daya da suka yi, su Zahra baba alkali da Asiya Usman da Maryam Adam muhd kam dama ko shigowa hall din naga basu yi ba, daga waje suka tsaya ana yatsine fuska ana taunar cingam wae nn jiran ganin ko Afeefah xata yi fuck up a taron suke, sae addu'a Allah sa hkn ya faru su ke don a cewarsu ba kai gare ta ba, sae ta iya saka kuka a gun, hka dae aka watse taro lfya bbu mishkila. Lol
Washegari ana sakkowa juma'ah aka daura auren Barrister Aliyu Mahmoud, da Zainab Mahmoud Umar a kan sadaki dubu dari biyu, daurin auren da ya samu halartar jama'a da dama daga garurruwa daban daban, kayataccen walima aka yi ranan a gidansu ango da amarya, Karfe biyar aka fara shirin tafiya da amarya gidan mijinta, bata wani daga hankalinta ba sae dae tayi kuka ssae yayin da iyayenta maxa ke mata nasiha, su Momy ma suka daura da nasu da yayyinta mata, nn yayyinta da kawayen Mami da 'yan uwan Abba suka rakata gidan m[truncated by WhatsApp]
🌸👩🏻 'Ya mace kyautar Allah👩🏻🌸
By Ashmaad
99.......
Karfe tara saura duk aka watse aka bar Zainab daga ita sae halinta bayan ta ci kukanta har ta gode Allah, can karshen gadonta da aka shimfide da bedsheet me ubansun laushi da kyau na milky colour ta takure kanta, wnn karan ma ba karamin bajinta iyayen nata suka yi mata a furnitures din dakinta ba, kmr ba baxawara ba a cewar wasu mutanen da suka xo ganin daki, har ta fara bacci daga xaunen da take taji shigowar mota gidan, gabanta ya fadi ba kadan ba, tana jin shigowarsa gidan ya hauro sama, ya kusa minti uku biyu tsaye corridorn dakunan kafin ya tura kofar dakinta a hnkli, da sauri ta cusa kanta cikin pillow bayan ta lullube fuskarta da mayafin jikinta, sanye yake da shadda milk colour sae kyalli yake, yyi tsaye nn bakin kofar yana kallonta kafin ya karaso cikin dakin kmr me counting steps dinsa ya xauna gefenta yana kallonta ya dago ta a hnkli, ta fashe masa da kuka tana nonnokewa taki barin ya ga fuskarta, lumshe ido yyi ya rungumeta tsam jikinsa cikin sanyin murya yace "Zainab!" Kin cewa komae tayi hkn yasa ya manna mata lips dinsa a wuyanta, ae tuni ta bude ido da sauri don sae da tsigar jikinta ya tashi, muryarta na rawa tace "Yayanmu!" Ya bude idanuwansa shi ma yana kallonta har lkcn yana rungume da ita, cikin wata kasalalliyar murya yace "Ina son ki Zainab, ina son ki! son da ban taba yi ma wata 'ya mace ba, kece macen da na fara so a rayuwata tun baki san kanki ba, bbu wata bayan ke Zainab, kin xame min jinin jikina, i just can't stop loving yhu har karshen rayuwata" hawaye ne ke bin kuncinta tana gyada masa kai, a hnkli ya sassauta rikon da yyi mata ya dago kanta yana kallan lips dinta ya shiga share hawayen fuskarta ta lumshe idonta, cikin sanyayyan muryarsa yace "Kina jin yunwa koh?" Bude ido tayi ta Girgixa masa kai yace "Sure?" A hnkli ta gyada masa kai cikin sarkewar murya tace "Bacci xan yi" yyi shiru yana kallonta kafin yace "Toh xaki yi wanka?" Sunkuyar da kanta tayi, ya mike ya nufi bayin dakin, ba a dau lkci ba ya fito dauke da bathrobe ya xauna gefenta ya ajiye snn ya cire mata mayafin jikinta, ya cire mata dankunne da sarka da bracelets din hannunta ya dauki bathrobe din ya mika mata yace "gashi ki cire kayanki kije kiyi wankan princess" mikewa tayi ta bata fuska tace "Toh ka fita in cire kayan" murmushi yyi yace "Ok" snn ya mike ya fita daga dakin, ta cire atamfar English din jikinta ta saka bathrobe din ta nufi bayi. Bakinta ta wanke tayi wanka ta fito, ta gama shafe shafenta knn ta sa kayan baccinta pink colour me tsantsi riga da dogon wando, tana kkrin tura gashinta cikin net ya shigo dakin sanye da jallabiya baki, k'asa ci gaba da abinda take tayi don da sauri take ta kwanta ta shige bargo, Karasowa yyi inda take ya karbi hular ya sa mata a hnkli snn ya dagota, ta rufe ido da sauri, murmushi yyi ya hadeta da jikinsa yace "ynxu kunya ta kike koh princess? Oya muje ki gaya min ma'anar kunyar kafin in cire maki" bae jira cewarta ba ya nufi kan gado tana jikinsa ya xaunar da ita, cikin lallausan muryarsa yace "Ina jin ki" kukan shagwaba ta saki tace "Ni bacci nake ji fa yayanmu" shiru yyi yana kallonta ta boye fuskarta kirjinsa da sauri tana shigewa jikinsa, lkci daya mood dinsa ya canxa, a hnkli ya janyeta jikinsa yace "Je ki kwanta" mikewa xaune tayi tana kallonsa xata yi magana ta ga ya mike ba tare da ya kalleta ba yace "Gudnyt" daga hka ya fice daga dakin ta bi sa da kallo jikinta yyi sanyi. Bangarensa ya nufa ya fada kan gado wani kishi ya ji ya lullubesa. Afeefah kam kwanciyar ta tayi ta shige bargo sae dae hawayen da take ta kkrin dannewa sae da ya xubo idonta, daga nn ta fara kuka a hnkli. Washegari tana xaune kan darduma don ko tashinta tayi sllh bae yi ba ya shigo dakin, ya xauna gefen gado yana kallonta, ba tare da ta kallesa ba tace "Ina kwana?" Saukowa k'asa yyi ya xauna gefen ta cikin sanyin murya yace "Lfya lau Princess, kin tashi lfya" ta sunkuyar da kai bata ce komae ba, shi ma bae kuma ce mata komae ba ya mike ya nufi kofa, ta bi sa da kallo har ya fita. Mikewa tayi jiki ba kwari ta fada kan gado ta runtse ido, to me tayi masa yake fushi da ita. Takwas saura ta ji an danna bell downstairs, tana ji ya fito daga dakinsa ya sauka k'asa, bayan minti biyar aka bude kofar dakinta Sadiya da Jiddah suka shigo, mikewa xaune tayi da sauri, duk suka sakar mata murmushi ta mayar masa kafin ta gaishesu, Jiddah tace "yayanmu yace ki sakko ki yi breakfast, Amaryar yayanmu" ba tare da ta kallesu ba tana murmushi tace "Toh" Sadiya tace "Mu xa mu koma" da sauri tace "Ynxu?" Jiddah tace "Kinga ko wanka ba mu yi ba anjima xa mu dawo" a sanyaye tace masu toh, kafin ta mike tsaye suka fita dakin gaba daya, sallama suka yi ma yayanmu dake xaune falo, snn ta rakasu bakin kofa ta daga masu hannu, juyawa tayi ta nufi sama ya kirata, ta tsaya kafin ta juyo tana kallonsa yace "Breakfast" a hnkli ta tako har cikin falon. Ta xauna k'asa gefensa ya sauko ya shiga hada mata tea, ya dibar mata farfesu da kayan soye soyen dake wani kula daban, a tare suka yi break din sae dae ita turawa kawae take bata da appetite, lkci lkci ta kan d'aga kai ta kallesa, har suka gama, ta kwashe kwanukan da cups ta kai kitchen, bata fito ba sae da ta tsaftace kitchen din, snn ta fito rike da sweeper da mop, ajiye wayar hannunsa yyi ya Mike yace "Let me sweep sae ke kiyi mopping din baxa ki iya ba ke kadai," mika masa sweepern tayi, duk inda ya share ta goge har suka gama ta xube kan kujera wae ta gaji, yyi murmushi yace "Dama nasan xa ki gaji din ae, a gidan tsohon mijin ki wa ke maki aikin" turo baki tayi tace "Bana yi" yace "Ba kya me?" Tace "Aikin" bae daina kallonta ba yace "Wa ke yi toh?" Tace "bbu wanda ke yi," yace "Hka kike barin gidan" ganin ynda ya tsare ta da ido yasa ta mike da sauri tace "Ni wanka xanyi yayanmu" daga hka ta nufi stairs ta haura sama da sauri ya bi ta da kallo, ta gama cire kayan baccin jikinta knn daga ita sae undies ta dauki bathrobe xata sa ya shigo dakin, k'ara ta saki a gigice ta durkushe gun tana kare kirjinta, shi kansa ya rikice ba kadan