Showing 81001 words to 84000 words out of 318746 words

Chapter 28 - saran boye complete by Queen meenali

01 Jul 2024

41665

da ƙyau, kafin ya jawo stool ɗin mirror ya zauna yana tambayarsa garin yaya yaji ciwon?.
     Bai tanka masa ba, dan haka Rich ɗin ya kama ƙafar kawai ya hau ja masa. “Jesus!!!” ya faɗa da muryar nan tasa mai amo data haɗu da damuwa a yanzun. Saurin zama Momy tai a kusa da shi ta amshe filon daya damƙe ta maye gurbin filon. Caraf kuwa ya kama hannunta ya damƙe cikin nasa da masifar ƙarfi, dan har sai da ta saki ƙara itama.
     Yanda jikinsa ke rawa zufa na fito masa sai duk tausayinsa ya sake kamasu, Miracle tai saurin zama ɗaya gefensa tare da kwanciya a jikinsa tana hawaye. Sai da Rich ya tabbatar ƙafar tayi yanda ya kamata sannan ya barsa. Sai faman jera masa sorry sukeyi.
      Duk da yaji mutum kwance a jikinsa bai motsaba sai da zafin ƙafar ya daina sosai, a lokacin ƙamshin turaren Miracle dana Momy suka tabbatar masa sune nanuƙe da shi. A hankali yasa hannu ya ɗaga Miracle dake lafe a jikin nasa, kafin itama Mom da tunda ta farga da Mira take zuba mata wani kallon ƙasan ido na gargaɗi, shi dai ya zare hannunsa daga cikin nata, jan jikinsa yay baya ya haye gadon sosai batare da yace uffanba duk da sannun da suketa faman yimasa har yanzun.
         Cike da kulawa Rich ya basu shawarar ya kamata su fita abar Yoohan ɗin ya huta, dan ya kula da yanda Yoohan ya sake cika tamkar zai fashe, hakan kuma yanada nasaba da zamansu a ɗakin, dan shi ɗin shaidane akan yanda Yoohan yay mugun tsanar jin kowanne kalar motsi a kusa da shi idan har yana cikin wannan yanayin.
        Papa da ya gamsu da shawarar Rich ɗin sai ya tarkatasu suka fice duk da uwar gayyar Mom bataso hakanba ita. Bin bayansu Richard yay shima dan yana buƙatar ɗakko wani abun da yake son gwadawa Yoohan ɗin ko zai aminta wannan karon yasha.

           Yoohan na zaune yanda suka barshi idanu a lumshe Richard ya dawo ɗauke da ƙaramin tray mai ƙyau. Duk da Yoohan na jinsa bai buɗe idanu ba balle ya motsa, Rich ya jawo ƙaramin table glass dake gaban sofa zuwa gaba gadon. Trayn dake ɗauke da kwalbar barasa da kofuna biyu, sai ƙanƙara a wani bowl ya ɗaura a kai yana kallon Yoohan ɗin. “Mr-x!”. Ya faɗa yana ƙoƙarin buɗe kwalbar barasan.
      Buɗe idanu Yoohan yayi a hankali batare da ya amsama Rich ɗinba. Rich ya ɗan murmusa, dan bai damu da rashin amsawarba, barasan ya zuba rabin kofi, ya ɗiba ƙanƙara ya zuba a ciki yana murmushi. Ɗagowa yay ya miƙama Yoohan dake kallonsa ta ƙasan ido kofin.
     Ɗauke kai Yoohan yayi fuskarsa na nuna ƙarin ɓacin rai, dan yasan Rich ɗin yafi kowa sanin shi baya shan giya...........
          “X-Man! inhar bazaka yarda na maka allurar da zata taimakeka kayi barci ba to ka daure kasha wannan, na tabbatar ita zata saka ka barcin koda na awa ɗaya ne. Kai fa likitane, kasan illar wannan matsalar da yanda take maida rayuwar mai fuskantarta a ƙarshe. Idan kana tunanin ƙin shan giya ne dan karta shiga maka rayuwar aiki yanzu ai ba'akan aikin kake ba, sannan don neman lafiyarka ne”.
         Shiru kamar Yoohan bazai kulasa ba, dan har Rich ɗin ya fidda tsammanin samun kulawarma. Sai ya tsinkayi sautin tsakin Yoohan ɗin a hankali. Kallonsa Yoohan ɗin yake cikin ido da jajayen idanunsa dake a kumbure, murya a daƙile yace, “Rich! a wajenka ya kamata mutane su ƙara sanin halina akan idan nace bazanyi abuba bazan taɓa yinsa ɗinba, dan haka karka sake tunanin zansha barasa koda ba yau ba”.
        Yanda yay maganar cikin kaushin murya ya saka Rich saurin cemasa “I'm very sorry”. Batare da Yoohan ɗin ya sake cewa komai ba ya maida idanunsa ya lumshe duk da yasan barcin ba ɗaukarsa zaiyi ba.

     Haka suka cigaba da zama a cikin ɗakin shiru, Richard da ya sha barasar da Yoohan yaƙi sha har ya fara barci a gefen sa, shiko idanunsa biyu amma suna a lumshe. Lokaci-lokaci hawaye kan ziraro masa ta gefen ido. Yana sauraren yanda Momy da Papa keta faman zaryar leƙowa ɗakin, sai dai ɗauka suke ko Rich ɗin yaci nasara yasha giyar barci ya ɗaukesa, shiyyasa hankakinsu yaɗan kwanta suketa faman jin daɗin yanda duk shigowar da sukeyi suna samun Yoohan ɗinne a kwance.
  
       Wajen misalin goma na dare Yoohan ya gaji da kwanciyar, tashi yay ya sauka daga gadon yana bin Rich dake barcinsa hankali kwance da kallo, bayi ya shiga ya watso ruwa. Bai jimaba ya fito sanye da bathrobe. a bakin gadon ya zauna tare da jingina da fuskar gadon. Ya kai hannu zai kashe fitilar gefen gadon idanunsa suka sauka akan farar envelope, cak ya tsaya yana kallon rubutun jiki, janyewa yay kamar zai share, sai kuma yasa hannu ya ɗauka tare da buɗewa ya zaro takardar dake a ciki.
     Rubutun bashi da wani yawa sosai, amma a tsare yake gwanin sha'awa, sannan yanda aka tsara kalaman cikin rubutun da harshen turanci sunyi matuƙar jan hankalinsa har yana ɗan lumshe ido. Sai da ya maimaita takardar sau biyu sannan ya ninketa ya maida cikin envelope ɗin ya jawo drawer ya ajiyeta yana juya abinda ta ƙunsa a cikin ransa.......

________________________
        *_SAUDIA_*

       Duk da fushi da zuciyarsa keyi ga duk zuri'ar gidan tasu hakan bai hanashin jin ɗokin zuwan hajjo da Ahmad ba, dan baisan harda Nu'aymah a tafiyarba. shiri yay tsaf ya wuce airport domin tarbosu batare da ya saurari Adawiya da tace zata bishi ba, dan tana wanka ma ya siɗaɗe ya fice daga gidan.

       Cikin sa'a kuwa yana isa airport ɗin jirginsu Nu'aymah na taɓa ƙasa. Lumshe idanu tayi tana karanto addu'oi da fatan cika alƙawarin da taima iyayenta akan kama kanta batare da wata fitina ta ɓullo ba. Hajjo na lura da duk motsinta, amma sai batace da ita komaiba har sukabi ayarin masu fita. Sanye take cikin wando blue na jeans da farar rigar fakistan da tsahonta yake har gwiwar ta, an ma rigar ado da blue ɗin duwatsu manya da ƙanana, sai farin veil da ta naɗa a kanta wanda ya sake fidda ƙuruciyarta da ƙyawun da ALLAH ya bata. Farar ƙafarta da kalar wandon ya haska tana sanye cikin blue ɗin takalmi da yay masifar mata ƙyau dan bata da babbar ƙafa sam. Sai ƙaramar jakarta itama dai blue ɗince.
     Kallon agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunta tai lokacin da suke ƙoƙarin sakkowa daga jirgin, ta ɗan yamutse fuska tana sauke hannun a hankali da kai dubanta can ɗan nesa dasu. Wani irin bugawa ƙirjinta yayi saboda hango Abdallah dake tsaye jikin motarsa sanye cikin ƙananun kaya da sukai masa ƙyau, ya ƙara ƙiba da ƙwarjini a idanun mai kallo kamar ba azumi ake ba. A take wata kasala ta saukar mata, tafiyarta ta sake raunana fiye da farko. Dan sai da Hajjo ta kama hannunta ta ida sauka da ita ma.
      Abdallah da ya yunƙuro saboda hango Ahmad dake a gabansu da yay yaja ya tsaya cak lokacin da idanunsa suka sauka akan Nu'aymah da bai zato ko tsammaanin gani ba.. Wata irin hajijiya-hajijiya ya faraji tana neman ɗibarsa a wajen, ya kasa motsi balle ɗauke ido daga kallonta har suka ƙaraso inda yake.
    Hajjo datai tamkar bataga halin da suka shiga ba ta mangare masa ƙeya tana faɗin, “Kurwata kur dan gidanku”. Firgigit yay da sauke nannauyan ajiyar zuciya, sai dai ya kasa ɗauke idanun nasa daga kan Nu'aymah da ta ɗauke kanta gefe tamkarma batasan da zamansa ba a wajen. Hannu yakai ya shafa inda Hajjo ta tallaresa kafin ya janye idanunsa da ƙyar ya maida kan hajjon data wani ƙyaɓe fusaka tana zuba masa harara.
      “Yanzu dan ALLAH daga zuwanki mina miki zaki tallemin kai?”. Ya faɗa yana ɓata fuska da kallon Hajjon. Watsar dashi tai taƙi magana, saima hannun Nu'aymah data kamo suna shirin barin wajen.
    Dariya Ahmad yayi, ya matsa ya rungume Abdallah, “Oh Yaya kaifa kai da Hajjo sai a slow, manta da batunta kayi tani da ƙanwarmu kawai”. Murmushi Abdallah yay tare da rungume Ahmad ɗin shima. Kafin su saki juna kowanne fuskarsa da murmushi jin daɗi. Abdallah ya sake kai dubansa ga Nu'aymah sannan ya kalli Ahmad.
     Kai Ahmad ya ɗan jinjina yana murmushi, amma baice komaiba sai ƙyafta idanu da yayma Abdallahn. Ab ya kaɗa kansa kawai da nunama Ahmad hanya alamar suje to.

         Nu'aymah da Hajjo na baya, yayinda Ab da Ahmad ke gaba. Hajjo ce kawai ke magana a motar Ahmad na tayata, dan mafi yawan maganar tata duk tsiya takema Abdallah, shi kuma Ahmad ɗin na karesa.
      Abdallah kam rabin hankalin na'a tuƙi ne rabi akan Nu'aymah da a yanzuma ta ɗauke kanta tamkar bata gansa ba. A haka suka iso madaidaicin gidan nasa mai ƙyau da tsari. Sai da ya faka motar inda ta dace kafin su fita shi da Ahmad, Ahmad ya buɗe na Hajjo, ya taimaka mata ta fito, Nu'aymah kuma ta buɗe da kanta ta fito tana kallon gidan dama anguwar gaba ɗaya, a baɗini kuwa zuciyarta har wani zallo take saboda ganin Yah Ab ɗinta, duk yanda tai tunanin zata daure sai ganinsa ya canja dukan ƙudirin nata lokaci guda. Sai dai kamar yanda ya fiske itama haka tai ƙoƙarin fiskewar.

         Abdallah ne a gaba lokacin da zasu shiga gidan, Ahmad da Hajjo biye da shi, sai Nu'aymah a ƙarshe tana karanto duk addu'ar da tazo mata a baki domin samun sassauci daga abinda takeji akan ganin Abdallahn.
        Falon tsaf yake ko ina a gyare, ga ƙamshi mai daɗi yana tashi da sanyin ac. Sallamar Abdallahn da karaɗin Hajjo ya saka Adawiya data cika da haushin tafiyar Abdallah batare da ta saniba ta fito. Sam idanunta basu kai a kan Nu'aymah ba, dan haka ta daka tsalle cike da ihun murna ta ɗane Hajjo, saurin riƙota Ahmad yayi yana faɗin, “Ke malama karki ƙarasata ki jamin tsiya wajen su Baba malam”. Sakin Hajjon tai tana dariya ta juyo ta rungume Ahmad ɗin shima tana tsale.
          “Wannan matar taka bata da man kai sam Yah Abdallah ”. Ahmad ya faɗa yana janye Adawiya daga jikinsa. Murmushi yaƙe Abdallah yayi yana kama hannun Hajjo ya zaunar a kujera. Hakan yay dai-dai da ɗagowar Adawiya zataima hajjo magana idanunta suka faɗa akan Nu'aymah dake tsaye gefe tana kallonsu.
      “What?!!!!” Adawiya ta faɗa da sauri tana waro idanu waje, a take ta sarƙe da yawu kuwa ta hau tari.
       Karan farko Nu'aymah ta saki wani lallausan murmushi da har ya bayyana fararen haƙoranta waje, ta taho da wani irin ɗoki ta rungume Adawiya dake tari tamkar zata amayo harshenta.
     Dakatawa Abdallah da Ahmad da suka miƙe saboda ƙwarewar Adawiyar sukai. Nu'aymah ta ƙanƙame Adawiya jikinta tana matso ƙwallar da suka taru mata a ido akan dalili biyu. Ganin Abdallah, da kuma kewar Adawiyan.
      Da wani irin sauri Adawiya tasa hannu biyu ta tura Nu'aymah, jikinta na wani irin rawar tashin hankali............✍

🤔Tofa, hajiya Adawiya yaya dai?🤗🚶🏻.


Barka da juma'a😍😘😍🤗


_______________________________

ZAFAFA BIYAR 2021

Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
  
          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.


*_INA MASU NEMAN INDA ZASU SAMU INGANTATTUN:_*
*_HERBALS APHRODISIAC NA GARGAJIYA BANA HADIN BATURE BA MAI SIDE EFFECT..?_*

*_TO KU SAURARA KUJI, DOMIN NESA TAZO KUSA.._*

*_ZEE HERBALS APHRODISIAC!_*
*_ZEE HERBALS APHRODISIAC!!_*
*_ZEE HERBALS APHRODISIAC!!!_*

*_MUNZO MUKU DA INGATTTUN KAYAYYAKI WANDA ZASU GYARA CIKI DA WAJE_*
   *_MUNADA SUPPLEMENT MASU GYARAN JIKI DANA FATA, WANDA ZASA SAKI KIYI SHEKI FATAR KI TAYI LAUSHI. TAYI LUWAI! LUWAI! TAMKAR TA JARIRAI_*
    *_AKWAI SUPPLEMENT NA KAYAN MATA WANDA ZASU GYARA KI, KIJI KI TAMKAR BUDURWA, SUPPLEMENTS DINMU BASU DA SIDE EFFECT, DOMIN AN HADO SU NE DAGA INGATTATTUN ITATUWA, WATO NATURAL PRODUCTS NE ACIKI._*
       *_KAI BA ANAN KADAI MUKA TSAYA BA, MUNA DA INGATTUN KAYAYYAKIN MATA WANDA KESA KISHIYA KWAFA, WANDA DUK INDA SARAUNIYA TAKAI KIN WUCE, WANDA ZASU TSATSO MIKI MARTABAR KI DA KIMAR KI_*.

*_AKWAI INGATTATTUN MAGUNGUNA, NA CUTUTTUKAN DA SUKA SHAFI DAN ADAM DAMA JINNU.. KAI DAMA WANDA BAMU AMBATA BA.. ZEE HERBALS APHRODISIAC (MASARAUTAR INGATTATTUN MAGUNGUNA KENAN)_*
     *_KYAU, ARHA, INGANCI, RAHUSA... SAI ZEE HERBALS APHRODISIAC_*
   *_MANHAJOJIN MU NA SOCIAL MEDIA: KAMAR INSTAGRAM DA WHATSAPP DAMA NAMBAR TARHON MU: DOMIN SHIIGA KUGA IRIN KAYAYYAKIN MU TUNTUBE MU TA_*

_INSTAGRAM LINK DIN MU:_
www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac

_WHATSAPP LINK DIN MU:_
https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz

_NAMBAR TARHON MU_
08169380189

*_KARKA BARI A BAKA LABARI GWARA KA BAYAR.. KIZO A DAMA DAKE YAR UWA, KI ZAMO DAYA DAGA CIKIN KASAITATTUN MATA MASU AJI.. MUNA GARIN KATSINA, SANNAN KAYAN MU MUNA BADA SU AKAN FARASHIN SAYA ‘DAI DAI KO SARI.. MUNA TURA KAYANMU A KO’INA A FADIN NAJERIYA._*

__________________________________






No. 21

.................“Adawiya!!” hajjo ta faɗa a ɗan tsawace. Yayinda Ahmad da Abdallah ma sukai wani zallon mamakin abinda Adawiya tayi suma.
     Kallonsu tai a firgice idanunta na tara ƙwallar takaici da jin zafin ganin abinda batai zato ko tsammani ba. Ta buɗe baki zatai magana a zafafe sai kuma ta tuna abinda ta nema mantawa. Saurin sauke numfashi tayi tana fashewa da kuka, tare da juyawa ta kalli Nu'aymah dake tsaye dafe da kujerar data taimaketa ta hanata faɗuwa lokacin da Adawiyar ta turata.
       “Nayi fushi wlhy Aymah, yanzu dama dake za'azo amma kikaƙi sanarmin saboda ke yanzu kinma daina sona?”. Adawiya ta faɗa cike da makirci da waskewa.
     Ajiyar zuciya Abdallah da Ahmad suka sauke, dan duk zatonsu Adawiya da gaske da faɗa tayi abinda tayi. Hajjo dai bata motsa ba, amma ta kafesu da kallo su duka huɗun tana nazarin kowa.
     Jin abinda Adawiya tace ne ya saka Nu'aymah sakin murmushi, dan tsaf ta fahimci Adawiya canja hanya tayi, inkuwa hakane ai itama tanada wayonta, dan wani abun ma sai dai ta koyama Adawiyar duk da kuwa ta girmeta da wasu wattani. Sake tahowa tai da ɗan gudunta ta rungume Adawiya tana faɗin, “Afuwan habibiya, surprise nai niyyar miki shiyyasa na hana kowa faɗa miki”.
        Leɓe Adawiya ta cije dan ta juyama su Hajjo bayane, itama cike da ɗacin zuciya ta rungume Nu'aymahn tana magana cikin kuka, “ALLAH saina hukunta ki tunda kika sani kuka”. Nu'aymah tai dariya hawaye na sakko mata itama, ta ɗago Adawiyan daga jikinta tana durƙusawa gabanta da riƙe kunnuwanta, “Afuwan hassanata, kaina bisa wuya Please”.
    Karan farko Adawiya ta saki dariya, itama sai ta durƙusa kamar yanda tayi sunama juna kallon ido cikin ido, Nu'aymah murmushi takeyi, Adawiya kam ta haɗe fuska ganin su hajjo basa ganinta. “Kin haƙura kenan?” Nu'aymah ta faɗa tana wani ɗage ma Adawiyar gira ɗaya da sakin mata lallausan murmushin da yay mata tsaye a maƙoshi.
      Kasa magana Adawiya dake mata kallon tsantsar takaici da haushi tayi, sai kawai ta rungumeta a jikinta tana gyaɗa kai........
       Gyaran Murya Yah Ahmad yay yana faɗin, “Kunga malamai ya isheku haka, ku barmu mu ƙarasa ƴar yunwar azuminmu da sauran yawu a baki dan ALLAH, idan akasha ruwa komaima sai kuyi zamu tayaku da sulhu”.
         “Faɗa musu dai”. Abdallah ya faɗa a wani irin yanayi yana komawa kusa da hajjo ya zauna. Ƙaramar dariya Hajjo tayi kawai tana ɗauke kanta, sai kuma ta kalli Abdallah tana faɗin, “Kaga Audillahi kaini ɗakina na huta kaji, bazan iya luguden laɓɓa ba da azumina a baki”.
        Fuskarsa ƙawace da murmushi ya miƙe tare da taimakama hajjon itama ta tashi. Har ɗakin da zata zauna ya rakata, tana zama Nu'aymah na shigowa itama. Duk kallonta sukai shi da Hajjon, ta ajiye jakarta tana zama a kujerar dake a ɗakin ƙwaya ɗaya tal, batare data kalli Abdallah ba tace, “Yah Ab! Ina yini?”. Kallonta yay a karon farko suka haɗa ido, sai ta ɗauke nata gefe tana komawa jikin kujerar ta jingina.
    “Kunzo lafiya?”. Ya amsa mata shima cike da basarwa, dan haka kawai yanzu yakejin zafin abinda ta aikata a ranar ɗaurin aurensu. Ƙin sake tanka masa tayi, hajjo kuwa tamayi kamar bata a ɗakin.
      Ƙofa ya nufa dan kai Ahmad nasa masaukin yana faɗin, “Ki taso ki koma ɗakin Adawiya, ita hajjo sai ta zauna anan...”. Kafinma ya rufe baki cikin sauri tace, “A'a zan zauna anan tare da Hajjon”.
     Da ga Hajjo har Abdallah kallonta sukai, amma saita ɗauke kanta tana ɓata fuska danma kar Hajjon tace dole sai taje. Shima har zai sake magana sai kuma ya fasa ya fita kawai.

     “Miyasa bazakije can ɗinba? Bayan ƴar uwarki na cike da ɗokin ganinki?”. Hajjo ta faɗa bayan ficewar Abdallah.
        Nu'aymah dake ƙoƙarin cire kayan jikinta tace, “Babu komai Hajjo, nafison kawai na zauna da ke kodan himma akan ibadar da mukazoyi, sannan nifa ma ittiqafin zan shiga insha ALLAH”.
      Murmusawa Hajjo tayi kawai tana ɗauke kanta batare da ta sake cema Nu'aymah komai ba, itama Nu'aymahn sai ta shige bayi abinta batare data jira amsar hajjon ba.

★★★
    
        “Kuturun ubancan kayyasa! Yanzu wane algungumine mai wannan shirya tafiyar a gidanmu?”. Adawiya daketa faman zagaye ɗakinta ita kaɗai ta faɗa tana cizar laɓe kamar zata hudashi. Ganin babu mai bata amsa ta rarumo waya ta fara neman maman Aaida. Bugu biyu kuwa ta ɗaga. Harta fara tsokanarta Adawiyan ta katseta da faɗin, “Maman Aaida yanzu ba lokacin wasa bane, ko kinsan sister ɗin nan nawa da zata auri Yah Ab da, ta biyo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login