Showing 222001 words to 225000 words out of 318746 words
ta gansu ba.
Godiya itama ta musu, ta shigo tabar Yoohan na ƙarasa magana da su. Bayan su Dr Liam sun wuce, Osin ya shige masaukinsu wai zaiyi toilet🤧. Solomon ma dai tafiya yayi can nasa masaukin inda suka fara zama da Yoohan. Hakan ya bama Yoohan da Richard damar kasancewa su kaɗai. Maganace a bakin Rich sosai gameda firar papa da Dr Mateo da yaji, sai dai baisan ta yadda zai tunkari Yoohan ɗinba kai tsaye tunda Papa mahaifinsa ne.
Ajiyar zuciya Yoohan dake ɗan nazarinsa yayi, “Rich kamar akwai magana a bakin nan naka tun kafin ka wuce kwanaki. Sai dai bansan miyasa ka gaza yiba. Duk da nasan dai bazai wuce akan komawata musulmi ba. Na yarda da kai Rich, dan baka taɓa cimin amana ba a tsahon shekaru goma sha shida da mukasan juna. Dan haka zan faɗa maka sirrin komawata mai salla a yanzu koda kuwa bazaka fahimceni ba”.
Batare da ya jira amsar Richard ba ya shiga bashi labarin tun farkon haɗuwarsu da su Nu'aymah a ƙofar Orphanage. Fasa masa glass ɗin mota da tayi da tilasta musu shiga cikin Orphanage akan yaron da suka bige. Fara mu'amularsa da su baba malam har zuwa musulintarsa da aurensa da ita. Babu abinda Yoohan ya ɓoyema Rich. Sosai tsantsar mamaki da firgici ya bayyana ga Richard. Wani irin rauni da ƙwaɗayin shiga musulinci ya ringa kutse cikin ɓargon jikinsa da zuciya. Sai dai baice komaiba akan hakan sai magana akan ƙullin da akaima Aymah na maganar ciki.
Ya janye hannunsa da ga dafe kan da yayi yana duban Yoohan da ke kallon wani waje da ban. “Ka yafemin Yoohan”.
Juyowa Yoohan yayi yana dubansa. Cikin ɗan lumshe idanu yace, “Akan mi? Ni bakamin laifin komaiba ai”.
“Niko na maka laifi X-man. Dan na zargeka akan abinda ba haka yake ba. Sannan na zargi in-lows ɗinka suma. Da ga yau na maka alƙawarin tayaka wannan yaƙin, zan taimakeka wajen cikama iyayenta alƙawarin daka ɗauka na bayyanar gaskiyar maganar cikin da suke zargin ta zubar”.
Kallonsa Yoohan yake cike da so da ƙauna. Ya riƙo hannun Rich cikin nasa yana faɗin, “Nagode sosai Rich, kai ɗin na dabanne a gareni koda bakina bai furtaba”.
“Ba nine na daban a garekaba Yoohan, kai ne na daban a gareni. Dan kamin abubuwa da yawa da ni kaina bansan hanyar da zan iya saka maka ba. Indai ni ɗin ɗan halak ne dolene na kasance a cikin yaƙin nan daka ɗauki alƙawarin yi. Sai dai zan baka shawara ɗaya zuwa biyu”.
Numfashi Yoohan ya furzar da lumshe idanu ya buɗe akan Rich. “Ina jinka”.
“Ka ajiye maganar ƙanƙantar matarka ka fara nuna mata ɗunbin soyayyar da kake mata. Waddama bata kaita shekaruba tana ɗaukar namiji balle ita dana fahimci tanada wayo sosai. Kaifa likitane, kasan sirrin mace duk da kuwa karatun likitancinka ba'a kansu kayisa ba. Amma na sanka da bincike, ta wannan hanyarne kawai kaima kanka zaka fahimci gaskiya ko akasin abinda Doctors ɗin suka faɗa a wancan karon, tare da naka gwajin, sai ka bita a sannu yanda kake buƙata.........”
“Amma Rich.......”
“Karkace komai Mr X. Wai shin kai baka tunanin shekarunka ƙaruwa suke ba raguwa ba? Ya kamata kasan sirrin dake cikin wannan tafiyar. Ko dai baka da lafiya ne Yoohan?”.
Harararsa Yoohan ɗin yayi kawai ya kauda kansa. Rich ya kwashe da dariya yana faɗin, “Kai ɗinne kana abu kamar dutsi oga. Ga dama ka samu a hannu amma kana son kasa damawa. Idan da kace kana ƙyanƙyami da gudun matan waje wannan dai matarkace ai ko.......”
“To naji mai shegen surutun tsiya. Muje shawara ta gaba”. Yoohan ya faɗa yana talle ƙeyar Rich.
Shafa ƙeyar Rich yayi da faɗin, “Mugu, ashe dai kanaso. Shawara ta ta biyu itace karku koma Nigeria da ita yanzu har sai na binciko maka duk yanda komai ya kasance”.
“Taya zaka binciko abinda baka saniba. Sannan wannan abun nasu yayi kama dana family, kai da ma ko sakin jiki ka kasayi da Uncle ɗin kanata faman jin haushinsa”.
Murmushi Rich dake kallonsa ya keyi, a ransa kuwa yanason hana Yoohan komawa Nigeria da Aymah ne saboda abinda ya jiyo a wajen papa a wannan komawar da yayi gida. Saboda hirar papa da Dr Mateo ta kasa barin ransa tun wancan karon. A wannan zuwan koda suka koma dasu baba malam a abuja ya sauka shi. Anan ya ɗanbi diddigin papa shine ya sakejin kwangilar kashe Aymah da ya bada ayi masa saboda wai ya ganta a cctv ta shigar masa ɗaki. Duk da basusan mitayiba a ciki saboda cctv ɗin iyakarta parlornsa ne, (Tab, kenan randa Aymah taje ɗakin papa. Ya salam🤦🏻♀️) Abinda yasa suka gaza gane mitayi su basuga komai a hannuntaba. To amma shi papa ya tabbatar ta ga sirrinsa shiyyasa yake buƙatar a kauda masa ita kafin bakinta ya faɗama wani. duk da yana zargin ta faɗama baba malam, yaso kuma ƙyaleta yabi a hankali harya gano abinda tayo a ranar amma su Uncle Mike sukaita tunzurashi aka ya kasheta kawai, shine ya bama Dr Mateo kwangilar kasheta a wajen aiki batare da an zargesaba, dan Yoohan ya sanar masa a inda za'ai aikin da masu tayasa. shine aikin ya gagara kuma.
Wannan abu da Richard yajine ya sakashi zaunar dasu G-boy akan su haɗa kuɗi su saka Yoohan zaman Honeymoon a Austria. Sai dai su basu san dalilinsa nayin hakanba dan bai fito fili ya faɗa musu ba........
Taɓashin da Yoohan yayine ya sakashi dawowa hayyacinsa. Ya sauke numfashi, cikin son kauda tambayar mi yake tunani da Yoohan yay masa yace, “Yoohan ka bani dama. Zanyi bincike nane iyakar likitocin da suka gwadata. Sai kuma ƴar aikin da kace an kawo muku tunda kace ka saka mata abin ɗaukar magana a ɗakin da kuka ajiyeta”.
“Okay Rich, sai dai banason ka saka kanka a haɗari Please”.
“Karka damu kamin addu'a kawai. Kuma ai tare zamuyi aikin ma da kai”.
Murmushi Yoohan ɗin yay masa suka rungume juna cike da so da ƙauna. Daga haka Rich ya korashi wai yaje madam na jiransa shima zaije yay video call da tashi dan gobe ma wajenta ya nufa, tare zasu wuce 9ja daga can..........✍🏻
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[6/22, 2:04 PM] +234 806 216 7027: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 59
..............Sosai yanzu ta nutsu ta ƙarema lungu da saƙo na ɗakin kallo, dan an kashe waɗancan fitulun ansa ainahin fitilu da suka ƙarama ƙawata ɗakin. Lallai duniya budurwar wawa. Idan bakayi wasa ba irin waɗanan abubuwan tuni suke shagaltar da kai ma ga bautar ALLAH. Shiyyasa wasu mutanenmu dasun samu irin wannan damar sai kaga addininma an fara walagigi da shi. Zama tayi tana jiran shigowarsa dan taji wai yayama za'ayi? taga ɗaki daya ne. Nashi ne nan ko nata?. Dan kuwa dai ba yarda zatai su zauna a ɗaki ɗaya ba ehe.
Tayi kusan zaman mintuna goma sha biyar sannan ya shigo ɗauke da ƙyaututtukan dasu Dr Sophia Suka bata. Yi tai kamar batasan ya shigoba. Shima kallo ɗaya yay mata ya ɗauke kansa. Sai da ya ajiye kayan hannun nasa sannan ya nufo inda take. Zama yay a kujerar dake kallon tata ya zaro wayarsa dake ring ya sa a kunne fuska ɗauke da murmushi. Sun kwashe tsahon mintuna a haka yana waya tana satar kallonsa harya kammala.
Kallonta yay ta kauda fuskarta gefe. ‘Yarinyar nan rigimanta yawane dasu' ya ayyana a ransa yana lumshe idanu da buɗewa a kanta. Ganin bazatayi manar daya fahimci takeson yiba sai ya mike ya shiga toilet ɗin ɗakin bayan ya ciri kayan barci a cikin kayansa da Solomon ya kawo ya ajiye rigar a saman gado ya ɗauki wandon kawai.
Duk da Aymah najin sanda ya shiga bayin ta kasa ɗagowa. Haka ta cigaba da zama zuciyarta na tattaro mata abubuwa masu ɗunbin yawa a kansa, ga ɗokin son komawa gida da takeyi, dan wulaƙanci yau ma gaba ɗaya bai kira mata Baba malam ba kamar yanda ya saba.
Duk daɗewar da yay a bayin a yanda ya barta haka yazo ya isketa. Da alama ma dai barci ta fara. Gaban kujerar ya matsa yana mai tsane sumar kansa ta gefe-gefe dan ba jiƙata yayi ba. Leƙa fuskarta yayi, hakan yasa ruwan da bai gama tsanewa ba a jikinsa ya ɗisar mata a gefen fuska.
Motsawa tai tare da buɗe idonta dan da gaske barci ta fara. Suna haɗa ido tai saurin jan gyalen jallabiyarta ta rufe fuska. “Oh God! Dama babyn nan mai bakin tsiwa tanada kunya ashe?. Tom tashi kije kiyi wanka”.
Bata iya ta motsa ɗin ba sai da taji motsin barinsa wajen. Ta gabanta ya zagayo inda Wadrobe ɗin ɗakin take. Tabi bayansa dake raɓar ruwan wanka da kallo, dan dogon wandone kawai a jikinsa babu riga, sai towel ɗin dake a hannunsa ƙarami. harya buɗe Wadrobe ɗin da akwatin kayansa ke a ciki, harma da nata kayan a haɗe da batasan da zamansu ba idonta a kansa. Ajiyar zuciya taɗan sauke da mikewa ta nufi bayin dan tana buƙatar yin wankan da ruwa mai ɗumi ko zataji daɗin jikinta, taga alamar kuma guy ɗin nan ba kunyace da shi ba. Kaɗanma daga aikinsa yace a gabanta zai Shirya. Bara tai wankan sannan tazo taji yanda zasuyi akan zaman ɗaki.
Lallai indai da ranka kallo baya ƙare maka ba. Dan toilet ɗin kansa ma wata aljannar duniyace. Tsabar ɗaurema ƙarya ƙugu harda television a ciki. Baki ta taɓe tana faɗin, ‘Kunga aljanu ai sun samu nayi. Kayi tsirara ga tv ana nunawa ai al-amari sai wanda kuma ido ya gani’. Da wannan mitar ta shiga wajen wankan na glass shima dake a mulmule. Wankanta tayi, sai da ta gama ne kuma tunanin kaya yazo mata a rai. Kanta ta dafe cike da damuwa tana faɗin ‘Oh Stupid me. Miya shiga kaina ne?’. Fitowa tai gaban ƙaton mirror ɗin da aka shirya towels a wani ɗan drawern glass shima. Fatanta ta samu bathrobe. Cikin sa'a kuwa tana ɗaga ta farko sai taga rigace. Ajiyar zuciya ta sauke ta warwareta ta saka. Tako wuce mata gwiwa, hakan ya sata jin daɗi ta ɗaure igiyar sannan ta naɗa ƙaramin towel a kanta dan duk ta jiƙa gaban goshin da ƙeyar. Kayanta data cire da nasa daya ajiye ta jefa cikin washing machine ɗin ta wanke. Ta sakasu wajen busarwa ma ta busar sannan ta ninke abunta ta fito dasu a hannu duk da harga ALLAH tanajin nauyin fitar saboda Yoohan. Amma da yake bawani jikinta bane a waje sai ta fuske akan zata ɗakko kaya ta dawo toilet ɗinne ta saka.
Zaune ta iskesa a bakin gado yana danna tab. Yana sanye da kayan barci farare ƙal. Baiji fitowarta ba saboda a hankali take tafiya da sanɗa, ita wayonta wai karya ganta. Sai ko akai rashin sa'a tana zuwa saitinsa ya ɗago ido ya kalleta. Cak ta tsaya tana cika baki da iska kamar zata fasa kuka. “Ni dai banason kallo”. Tai maganar da alama dai an ƙure mata gudu ne.
Idanunsa ya lumshe yana sake buɗesu a kanta. Baki ta kuma cunawa gaba ta juya masa baya.
A hankali yace, “Silly girl!”. Yana maida kansa ga tab ɗin.
Cike da munafurci Aymah taɗan karkato ta kallesa. ganin ya maida kansa ga tab taci gaba da tafiyarta kai tsaye yanzun. Bayansa taje ta tsaya ta ɗayan ɓangaren gadon. Kamar zatai kuka tace, “Banda kayan sakawa ni fa”.
Batare daya juyo ya kalleta ba yace, “Tom aro zan baki ne?”.
“Hu'um. Ƙato da kai tayaya kayanka zasumin. Kana kallon kanka kuwa a mirror? Sai kace ɗan dambe”.
‘Yarinyar nan ko’ ya faɗa cikin ransa yana juyowa ya kalleta. Saurin juya masa baya tayi dan itafa batason kallon. Shima ya fahimci kunya takeji, hakan ya sakashi yin murmushi. Wannan ɗabi'ar ta kunya tana abu na farko da yaren hausawa ke burgesa da shi. Ko abu ke damunsu sukazo gabansa matsayin likita sunta ƙunshe-ƙunshe kenan.
Miƙewa yay ya zagayo inda take. Ganinsa kawai tayi a gabanta. Hakkanne ya sakata zabura tai baya kamar wanda tai gamo da abun tsoro. Tai saurin sake juya masa baya a daburce.
Hannayensa duka biyu ya tura cikin aljihun wandon kayan barcinsa yana faɗin, “Uhyim! Tom nama fasa bada aron kayan. Garama ki lallaɓani fa, koki kwana da bathrobe. idan kuma kinaso juyo ki kalleni”.
Ji Nu'aymah tai kamar ta fasa ihu dan takaici, gashi harga ALLAH tana buƙatar aron kayan kuma da gaske. Dan bazata iya kwana da rigar wanka ba. Juyowa tayi a hankali idanunta a ƙasa ta kasa kallonsa. Yanda ta koma kamar wata munafuka ne ya bashi dariya. amma sai ya gimtse kayarsa baiyiba. Takowa yay gabanta ya tsaya gab. Yasa hannu a karɓi kayansu dake a hannunta tare da ɗora na damar a haɓarta ya ɗago fuskarta. Tsaf ta runtse idanunta kuwa. Baiyi magana ba, sai kallonta kawai da ya keyi musamman bakinta da arayuwa yake bala'i-bala'in ɗaukar masa hankali. Kodan shine yafi masa tsiwa oho. “Je gasu can a Wadrobe ki ɗauka badan halinkiba dai”.
Batare data buɗe idanunba ta motsa laɓɓanta kaɗan tace, “Thanks you”.
Sakar mata fuska yayi ya matsa. Da sauri tabar wajen dan gaba ɗaya idan ya tsaya kusa da ita koya zauna jinta take a matuƙar takure, duk sai yay mata kwarjini. Tana buɗe akwatinsa dake a Wadrobe ɗin yana isowa wajen. A bayanta ya tsaya gab tare da zura hannunsa duk biyu ya ɗora akan nata dake ɗaga murfin trolly ɗin data buɗe. Jitai numfashinta na fita da ƙyar lokacin da ƙirjinsa ya mannu da bayanta duk da akwai kaya a jikin nasu. Taɗan rintse ido zuciyarta na harbawa. Kansa ya ɗora gefen kafaɗarta ya ajiye kayansu daya amsa a wajenta yana magana a hankali. “Ashe kin iya wanki?”. Kasa bashi amsa tayi, dan harga ALLAH ta matuƙar takuruwa. Shima fahimtar hakan da yayine sanadin numfashinta da yaji yana seizing ya sakashi sakar mata kiss a wuya yaja baya. Kaɗan ya hana fitsari zuboma Aymah. Ta sauke ajiyar zuciya da ƙyar sannan ta buɗe idanunta dake tara ƙwalla. Ɗaga kayan ta farayi ko zataga wanda zai ɗan mata, sai taga kayanta har kala huɗu ashema a ciki. juyowa tai taɗan kallesa da masa ƙaramar harara. Baisan tanayi ba, dan ya juya mata baya ne zai zauna a inda ya taso a bakin gado. Ƙunƙuni taitayi tana ciro kayan. Gaba ɗayansu ma kala huɗu ne. Na barci biyu, dogayen riguna biyu, sauran duk nasane suma dai basufi guda biyar ba, Sai kayan ciki datai fatan ALLAH dai yasa bashine da kansa ya ɗakko mata su ba. Dan wlhy daya gama da rayuwarta kam. Ɗaukar waɗanda zata saka tayi ta maida sauran. Ta haɗo harda wayarta data gani a ciki da Charger. Ta gabansa tazo ta wuce bayi, acan ta canjo kayan ta yafo mayafin jallabiyar data wanke dan dashi ta koma. Kayan bama wani kamata sukayiba, kuma basu fidda mata jikiba. Sai dai wandon iyakarsa gwiwar ta. Sannan hannun rigarma bawani babba bane can sosai. Amma bai mata yanda zataji kunya ba. A kwance ta samesa yanzun, idanunsa a lumshe suke amma batasan duk yana kallonta ba. Wajen Wadrobe ɗin ta koma, ta ɗauki turarensa data gani har biyu saman akwatin ta hau fesawa. Daga haka ta dawo wajen gadon tana kallonsa fuska a tsuke.
“Wai bazaka tafi ɗakinka ba ne?”. Tai maganar a hankali kamar maijin tsoro. Sarai ya jita, amma sai yay shiru abunsa kamar yayi barci. Idanuntane suka cika da ƙwalla. Dan gaskiya ita dai bazata iya kwana da shi a ɗaki ɗaya ba. Ta ɗan ɗaga murya fiye da ɗazun tace, “Kaji! Dan ALLAH kaje ɗakinka. Kokuma ni naje can sai na kwana”.
Idanunsa ya buɗe a kanta. Yace, “Ohooo! Silly girl. Nan gidanki ne ma ashe ko? Dahar sai kin zaɓi ɗakin barci?”.
“To amma ai kasan mu biyu ne sai ka kama ɗaki biyu”. Tai maganar da iya gaskiyarta. Fahimtar da yay yarintar tatace ta motsa ya sakashi gyara kwanciyarsa yana faɗin, “Wasa nake miki ga key ɗin ɗakinki anan zoki ɗauka”. Ya nuna mata bedside ɗin. Da iya yarda ta nufo wajen kuwa ita zata ɗauki key. Tana ɗora hannunta saman handle ɗin drawer ɗin kuwa ya riƙesa caraf.
Bata ankaraba sai jinta tai a jikinsa ya fisgota ta faɗo. Duk da