Showing 282001 words to 285000 words out of 318746 words
Babu wanda drama ɗintasu baisa dariyaba. Sai Jay da Bily basu dara ɗinba a fili sai a zuciya. Sundaita kallonsu cike da nazarin suɓutar harsunan nasu.
Kai jay ya girgiza kawai yana katse little dake son ƙara magana. “Kunga ku aje wannan shirmen naku sai kun fita can sai kuyi, idan kunso ku sassafa kawunan naku munada likita a kusa da zai duba ku. Yanzu dai Yoohan dole a yau ɗin nan Nu'aymah ta wuce kano. Dan aikin nan banason ya shige satin nan bamu kammalashi ba. Maganar Abdallah kuwa na tabbatar jin Nu'aymah na Nigeria zaizo shima koda a ɓoyen daya saba ne. Yanzu zan baza jami'ai da zasu fara bibiyar lamarin motsin kowa na gidan idan ya fito. Shima Nasir ina buƙatar a jawomin hankalinsa yazo kano. Babu sanya a aikinmu, duk wanda mukaci karo da rashin gaskiyarsa zamu kamasane mu tuhumesa kamar Rabi. Za kuma mu maida Rabi itama dan wayarta zata taimaka mana sosai wajen zaƙulo abubuwa”.
Cike da gamsuwa kowa ya amsa masa. Duk da kuwa Yoohan dai da alama baiso yin nisa da matarsaba. Amma ya fahimci hakan zai taimakesa gameda ƙudirin papa kuma a kanta. duk da kuwa a kanon ma wasu kurayen zata tarar. amma gara can akwai jami'ai masu sanya ido a lamarinta.
________★
Koda su Aymah suka dawo gida bata ga Blessing ba. Hakama Madam Chioma da papa da alama basa gidan ma. Yara kawai suka tarar da Mama debora. Joy ta wuce makaranta, Miracle kuwa mama debora ke basu labarin wai ta haɗa kayanta ta koma gida.
Ko a jikin Yoohan. Aymah kuwa yar dariyar shaƙiyanci tayi abinta ta wuce sama cike da tunanin ina Blessing ta shiga. Ɗakinta ta nufa direct, ta fara zame kayanta zuciyarta taf damuwa akan maganar hoton nan. Agogonta data cire ne ya faɗi ƙasa. ta ɗan matsa baya tana dubawa ta tillesa da ƙafa yay ƙarƙashin gado. Abin ya bata haushi, dan harta barsa akan yayta zama sai kuma taji tanason ɗakko kayanta dan Yoohan ya batashi matsayin ƙyauta a ranar da suka cika shekara ɗaya da aure. Fita tai ta ɗakko mopping stick dan Yoohan bai shigoba har yanzu yanacan tare da mama debora. Durƙusawa tai gaban gadon batare da damuwa da cikin dake gabantaba saboda wauta. Ta kunna fitilar wayarta ta haska. Da ƙyar ta iya hango agogon ta saka mopping stick ɗinnan ta turosa a hankali. Sai da yazo dab da ita ta fahimci harda wani abu take jawowa. Hannu ta miƙa danta jawosu duka ta kasa. Dole ta sake zungurowa da iccen mofa ɗin sannan suka fito. Jikinta har rawa yake wajen fara ɗaukar envelope ɗin ta buɗe. Tai wani irin waro ido na al'ajabi da mamaki. Batama san sanda ta ƙwaƙume hoton a ƙirjiba saboda murna. Jin an taɓa ƙofar za'a buɗe tai saurin sakin hoton ƙasa, kafin Yoohan daya shigo ya ƙaraso ta tura hoton ciki yanda bazai ganiba.
Duk da ta masa alamun rashin gaskiya sai bai nuna yama fahimcetaba. Yay baya da fiɗin, “Oh ashe kina nan, bara na watsa ruwa saiki shirya kema zuwa biyar na yamma zamu wuce kano. Amma mi kikeyi ma a durƙushe anan? Bayan kinsan bake kaɗai bace?”.
Miƙewa tai tana nuna masa agogon data ɗakko. “Kaga abinda na yadda nan na ɗakko”.
“Ki kulafa, dan na fahimci har yanzu wautanki na nan”.
Baki ta kumbura da iska batare datace masa komaiba. Shima sai ya juya abinsa ya fice kawai ya barta batare daya sake maganaba. Sai dai bai rufe ƙofaba. Da wannan damar ya samu zarafin laɓewa kozaiga mitakeyi. Aiko tana ganin ya fita ta sake duƙawa ta ɗakko hoton tana ambaton ‘Alhmdllh ya ALLAH. Da banga hoton nanba da bazan taɓa yafema duk wanda ya ɗaukesaba. Dolene nasan wacece wannan mai kama da mijina ɗin insha ALLAHU’.
Dukkan maganganun Aymah a cikin kunnen Yoohan ne. Hakan yasa zancen tsaya masa a rai tare da son jin ganin hoton nan shima. Yayi kamar zai dawo sai kuma ya fasa. Akan idonsa ta maida hoton a Wadrobe. Tafiya yay ɗakinsa tunda yaga inda ta ajiye. Sai dai kamar tasan yana kallonta. Yana barin wajen ta ɗauke hoton ta sakashi a ƴar jikkar data haɗa kayan tafiya kano wai dan kar wani ya sake shigo ya sace mata. Tana shiga wanka Yoohan ya dawo duba hoton. Sai dai kuma komai kama da shi bai ganima. sai ma kamashi da Aymah taso yi ALLAH dai ya taimakesa ya gudu.
Haka suka kammala shirin wucewa kano mamakin atsabibancin Aymah na damun Yoohan, shi ganima yake ta gansa shiyyasa ta canjama hoton waje.
Itako Aymah ranta fal baƙin cikin rashin ganin Blessing da Yoohan yasa tabar gidan har sai sun wuce dan bayason ta sanamar Nu'aymah abinda ya faru tsakaninsa da Momynsa.
*_KANO TA DABO_*
Ƙarfe bakwai dai-dai jirgin su Aymah ya sauka a kano. Batare da sanin kowa daga ahalintaba har su baba malam. Sai da Yoohan yasa suka fara biyawa sukai shopping na tsarabar da zata kaimusu sannan suka wuce gidan.
Ganin Aymah da Yoohan ya saka mai gadi buɗe musu gate mai taxi ya shiga har ciki. Nu'aymah zata fita da kwakwazo Yoohan ya riƙota yana girgiza mata kai. “Please kibi a hankali, a ganinama ba gara ki shige babu wanda ya san da zuwanki ba da safe sai kiyi musu surprise”.
Baki ta ɗan tura gaba. Sai kuma tai saurin sakin dariya da cewa, “Yes Yah Yoohan kayi gaskiya kuma”.
Murmushi yay mata da bata sumba a gefen kumatu. Daga haka suka fito a motar. Gidan shiru kowa yana a sashensa, hakan yasa Yoohan taya maigadi kaima Aymah kayanta bakin ƙofa. Sannan ya turata ciki ya sulale ya koma taxi ɗin suka fice. Dan hotel yake son guduwa kafin baba malam su fito massallaci su ritsashi.
Umm na zaune a bedroom tana karatu da jiran lokacin sallar isha'i sai ji kawai tai an rungumeta. A firgice ta juyo dan harga ALLAH ta tsorata. Ta waro idanu sabida mamakin ganin wadda batayi zatoba.
“Nu'aymah wai kece da gaske?”.
Kukan murnar ganin Umm ɗinta ta saki tana faɗin, “Nice Ummna, I miss you so much”.
Rungumeta Umm tayi da ƙyau a jikinta itama ƙwalla na cika mata idanu. Kai ɗa dabanne gaskiya. Sanin ba ita kaɗai bace yasa Umm tadata daga durƙuson da tayi a ƙasa ta zaunar da ita a bakin gado. Gaba ɗaya Aymah sai kuma taji kunyar Umm ta mamayeta, sai ta duƙar da kai ƙasa tana ƙara lulluɓe cikinta da gyale. Dariya abin ya bama Umm sosai. Sai dai bataiba. Saima tambayarta tai ina mijin nata?.
Kan Aymah a ƙasa tace waje ta barsa ita dai suna kwaso kaya shi da maigadi. Jin haka yasa Umm fita ta leƙa. Sai dai babu Yoohan babu dalilinsa sai maigadi kawai dake shigo da kayan ɗan barandar falonsu. Shine ke sanar mata Yoohan ɗin ya juya tare da mai taxi akan da safe zai dawo insha ALLAH.
Kai kawai Umm ta girgiza ta koma ciki, inda ta iske Aymah ta fito daga toilet da alama fitsari tayo. Cike da kulawa tace, “Kinji mijin naki ya tafi wai zai dawo da safe. Dama kunyi dashi hakan?”.
“A'a wlhy Umm, ni kawai yace na shigo zaije massallaci ne”. Tai maganar cikin ɓata fuska. Murmushi kawai Umm tayi ita dai, tace, “To kiyi wanka kawai sai na samo miki abinda zakici ke tunda shi ya gudu. Cike da kunyar Umm ɗin data aro ta yafama kanta ta amsa da to. Daga haka ta koma toilet ɗin danyin wanka.
Babu wanda Umm ta sanarma da zuwan Nu'aymah a gidan sai hajjo. Sai ko Muhammad daya dawo massalaci ya ganta a bazata. Baba malam ma sai da ya sallami ɗalibansa ya shigo yaci karo da ita a falo zaune ita da Hajjo da Umm da Muhammad dake liƙe da ita.
Tuni Nu'aymah ta manta da kunya, ta miƙe da sassarfa ta nufi Abbanta dake kallonta cike da kewa da so da ƙaunarta. Gabanta tai niyyar durƙusawa ya riƙota yana faɗin, “A'a mamana keda ke fama da kanki. Irin wannan zuwa haka na bazata”.
Hannunta yaja ya maida a kujera sannan shima ya zauna. Kanta a ƙasa ta shiga gaisheshi cike da kewa. Shiko yana amsawa da kulawa. Abakin Umm yaji cewar Yoohan ya gudu. Dariya kawai yayi dan ya fahimci kunya Yoohan ɗin keji da alama.
Haka sukayi murnarsu su huɗu kawai. Ganin dare ya farayi Hajjo taje sashenta danta kwanta. Aymah kuwa a ɗakin Umm zata kwana tare da Umm ɗinta data bar baba malam shi kaɗai.
Aiko maimakon barci sai suka buɗe sabon babin hira ita da Umm ɗin, sai da suka kusan kai asuba sannan barcin ya kwashi Aymah, daga nan itama Umm tayi.
__________★
Washe gari kam a bazata kowa yaga Nu'aymah a gidan. Kafin kace mi sun rikice da murna da hayaniya. Tun Aymah na ƙunshe-ƙunshen ciki harta saki jikinta ta shige cikin ƴan uwanta anashan shafta. Zuwa tashin hantsi kuwa sai ga Hajarah tazo gidan, dan ita dama tasan da zuwan nata. Rungume juna sukai cike da farin ciki. Yanda suka nuna ɗin har mamaki ya bama kowa. Dan gaba ɗaya salon shaƙuwar Adawiya da Nu'aymah ne ya koma kan Hajarah a yanzu.
A ranar da yamma suma ƴan Abuja suka iso. Ganin Nu'aymah kuma ya matuƙar basu mamaki dansu da suke Abujan ko a labari basusan da zuwan nataba. Har Momy ma sai da ta kasa haƙuri tai complain ɗin cewar Yoohan bai ƙyautaba. Suna matsayin iyayen Nu'aymah amma yazo da ita har Abuja bai fara kaita canba sai dai suzo su ganta anan tsulum.
Daga karshe dai Yoohan ɗinne da yazo gidan ya kare kansa akan wannan tuhuma. Dan Aymah bata iya cewa komaiba tunda itama tunanin zuwa can ɗin baizo mataba. Zumuɗinta kawai azo kano.
Ya bama su baba malam haƙuri akan rashin tsayawarsa jiya. Acewarsa aikin gaggawa ne ya samesa shiyyasa bai tsayaba. Duk sun masa uziri akan haka. Sannan suka ɗora da godiya akan hidimarsa ga gidan marayunsu daketa ƙara nunkuwa a koda yaushe. Akan bikin nanma kawai da za'ai ba ƙaramin hidima yayiba.
Washe gari baƙi suka fara cika gidan, ƴan katsina, ƴan lagos da sauransu, kowa kuwa yana sake yaba yanda Aymah ta ƙara girma da canjawa a cikin shekara ɗaya kacal. Gashi daga gani ansan ta samu lafiya yanzu. Sai dai fatan ALLAH ya sa ta sauka lafiya kuma.
Da yamma sukaje can orphanage akai walima, anan ta haɗu da sauran yayunta su Kubrah. Tayi mamakin ganin yanda Aunty Kubrah ɗin dukta lalace. Harta kasa haƙuri ta tambayi aunty Hajarah.
Cike da damuwa Hajarah tace, “Humm Aymah ke dai ALLAH ya ƙyauta, zaman natane babu daɗi daga ita har mijin da kishiyar. Kwanaki ai kusan watanta biyu a Lagos wajen Abbah Musbahu. Sunyi faɗa ya daketa shine taje can”.
Kasa magana aymah tayi saboda damuwa. Kodai babu komai Kubrah ƴar uwartace duk da a yauma ta nuna har yanzu ba sonta takeba.
Duk wannan hidima da akeyi kuwa su Aymah zagaye suke da yaran Jay ta ko ina. Motsin kowa akan idonsu yake faruwa. Tun daga orphanage har cikin gidansu.
Washe gari juma'a aka ɗaura auren amare ashirin da takwas maza da mata. Kowa ya kalli su baba malam yasan suna cikin farin ciki. Sai dai ai fatan ALLAH ya basu ladan hidimarsu ga marayun ALLAH babu gajiyawa.
An miƙa amare ɗakunansu, daga haka baƙi suka fara raguwa sai na jiki kawai aka bari. Kamar yanda Jay ya samu tattaunawa da baba malam a ranar ɗaurin aure a yau suka yanke hukunci bisa shirinsu. Duk da kuwa da ƙyar baba malam ɗin ya yarda da buƙatar Yoohan, Jay, Omar ɗin. Dan basu ɓoye masa komaiba game da shirin nasu gudun kar a samu matsala.
Tun a yammacin ranar baba malam ya fara takalar Umm da batun mallakama Nu'aymah wasu kaddarorinsa dan yasan lallai mai musu laɓe na tare da su saboda tuna Nu'aymah tazo garin ya fahimci mai laɓen ya ƙara ƙaimi wajen yimusu. Ta riga tasan shirinsu, itama sai ta biye masa. Sai dai zancen bai tsahoba suka barshi akan zasu ƙarasa da safe dan lokaci baba malam nada uziri..........✍
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[7/6, 9:38 AM] +234 913 412 2711: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 73
.............A yau kam su Nu'aymah da duk wanda yasan da wannan shirin sun tashi a shirye tsaf bisa yaƙinin tarkon da suka ɗana ya ɗanu. Kasancewar sanyi da akeyi duk sauran jama'ar gidan da ƴan biki suna can a sassan gidan a maƙale, duk da madai ƴan bikin da suka rage duk na jikine babu bare. Babu kowa a tsakar gidan sai yaran Jay dake ɓoɓɓoye.
Yau kam Jay ya shiga har falon baba malam tare da lauyan malam mahaifin su baba malam a zuwan zasu tattauna akan kaddaririn baba malam ɗin. Acan kuma ta waje little bee ce da wasu jami'a a harabar gidan a mabanbanta wajaje duk da Jay yasan akwai camaras ɗin da Afrah ta saka masa a wancan zaman. Yafi buƙatar gani ga ido ga kowa kafin ya bankaɗa sirrikan dake a cctv ɗin. An kira Aymah da Yoohan falon, sai su Abban Abdallah da hajjo data san komai itama. Sai Omar da yazo matsayin lauyan Nu'aymah shima.
Bayan buɗe taro da addu'a baba malam ya fara da nasiha a garesu duk dai a cikin salon tarkonsu, dan a zahiri fa babu wani maganar mallakama Nu'aymah kaddarorinsa da yakeyi. Shirine kawai irin nasu Jay.
A gefe kuwa idanun su Yoohan gaba ɗaya na'a Windows ɗin falon a kaikaice. Baba malam kuwa na cikin nasiha sai ga abinda suke jira ya bayyana. Kallon juna sukai shi da Jay dasu Yoohan sukayi murmushi. Daga haka ya cigaba da bayaninsa hankali kwance.
Acan waje kuwa su Little bee na mammaƙale a maɓoyarsu sai ga mutum sanye cikin dogon hijjab har ƙasa da niƙab ya fito daga tacan bayan gidan yanda babu mai iya fahimtar daga ainahin sashen da aka fito. Basu da tabbacin mace ce ko namiji, dan komai an rufe ba'a gani.
A yanda mai laɓe ke tafiya da dabaru zaka san cewar lallai an ƙware, sannan aikine da akeyi tunba yanzuba. Cikin salon iya aiki Little bee taima abokan aikinta wani salo da yatsun hannunsa suka bada ɗass!! Sau ɗaya. A take duk suka ƙara shiryawa dan suma dai suna biye da mai laɓe akan idanunsu.
Sai da suka tabbatar mai laɓe ya isa dai-dai sashen Malam marigayi alamar dai ɗan gidanne, tunda har ansan a ina su baba malam zasuyu taron nasu aiko sai wanda yasan gidan. Kamar yanda mai laɓe ya saba a koda yaushe ya isa jikin Window. Wani siririn abu ya saƙa a tsakanin glasess ɗin Window ɗin da alama na ɗaukar magana ne. Dan yana gama turashi ya kai hannu ya taɓa kunnensa alamar tabbatar da daidaitar komai. Ƙaramin tsaki akaja jin Nasihar da baba malam ya fara dan ba ita ake buƙataba a yanzu. Jin baba malam zai fara jawabinsa mai laɓe ya ƙara nutsuwa da maida hankalinsa ga window ɗin domin saurare..
Da wannan damar su Little bee sukasamu isowa wajen cike da ƙwarewar aiki suka toshe gaba da baya na ɗan siririn lungun bayan ɗakin malam marigayi. Ƙarar saƙon daya shigo wayar Little bee daga Jay ne ya fargar da mai laɓe ya juyo da sauri. Sai kawai ganinsa yayi zagaye da mutanen da baisan ta ina suka ɓullo ba.
Tashin hankali ba'a saka maka rana. Wannan shine ɓoyayyar kalma a zuciya da bakin mai laɓe duk da bai fito ya furta manaba a zahiri. Dan kuwa dai gabas da yamma kudu da arewa babu wajen guduwa. Katanga a bangon gabas. Ginin sashen malam a bangon yamma. Little bee da jami'ai uku a bangon kudu duk sun nunasa/ta da bindiga. Dawood da jami'ai uku shima a bangon arewa duk sun nunata/sa da bindiga nanma.
Wannan itace kwana casa'in da tara ta barawo ɗaya tak ta mai kaya. Little bee ta ciwo wayarta da hannu ɗaya a aljihu ɗayan kuma riƙe da bindigar data nuna mai laɓe. Kiran Jay tayi a waya. Yana ɗagawa tace, “Sir! Aikinmu ya kammala zaku iya fitowa”.
“Woow!” Jay ya faɗa yana miƙewa idonsa akan su baba Malam. Takawa yay jikin windown da yake hango inuwoyinsu ya zuge gilas ɗin tare da net. Abinda mai laɓe ya saƙala ya faɗo. duƙawa yay ya ɗauka yana jujjuya shi a hannunsa kafin ya kalli su baba malam da suma duk shi suke kallo.
“Malam zama ya ƙare ai, suspect ɗinmu yazo hannu zamu iya zagayawa”.
Harga ALLAH sai da gaban baba malam da Umm ya faɗi. Hakama Aymah duk sai taji tsoro kuma. Su Abba Musbahu da basusan mi akeyiba suka shiga kallonsu da tuhuma. Ko a jikin Yoohan da Umar. Dan sunema farkon ficewa a falon.
Baba malam dake kallon su Abban Abdallah yace, “Kuyi haƙuri wannan itace kawai mafita