Showing 129001 words to 132000 words out of 318746 words
akan al'amarin nan sai da nazo na sanar mata. Abba ko kasan dama tunda Yah Abdallah ya dawo gidannan baiyi zaman minti biyar da Momy ba. Da ya shigo ya gaidata da safe bazata sake ganinsa ba sai washe gari. Fushi yake da ita babu gaira babu dalili. Ta sakani na tambayesa amma yacemin idan na sake zuwa masa da zancen Momy sai ya ɓatamin rai. Ita kanta nace zan sanar maka abinda ke faruwa amma ta hanani, wai mu bashi lokaci kozata fahimci abinda ke damunsa”.
Jikin Abba ne yay sanyi, dan tabbas kuwa ya kula tunda Abdallah ya dawo ƙasar nan bai taɓa ganinsa zaune da Momy ba, da farko yaso tambayarta sai kuma yayi tunanin ƙila sai ya fita suke zaman. Wannan ya sakashi yin shiru duk da kuwa yasan yanda matar tashi take da ƙulafucin ƴaƴa musamman Abdallah.
Nannauyan numfashi ya sauke tare da zama yana cire hular kansa ya ajiya.....
A ɓangaren baba malam kuwa Abba na fita waya ya zaro ya shiga neman layin Abdallah. Sai dai kuma abin mamaki switch off. Ajiye wayar yayi ya maida hankali ga Hajjo da ke sharar hawaye har yanzun. Kwantar mata da hankali ya shigayi da bata haƙuri. Yace, “Inna ki kwantar da hankalinki dan ALLAH, insha ALLAHU mu dai wannan bazai kawo mana rabuwar kawuna ba. Duk inda Abdallah ya shiga kuma na tabbata zuwa dare dole ne ya dawo gida ya kwana ai, insha ALLAHU a daren nan sai ya maidasu su duka biyun”.
“Ɗan malam bazaka gane abinda nake nufi ba, amma duk yanda kake tunanin sauƙi a al'amarin nan da wahala ya kasance hakan. akwai abinda na sani wanda kai da sauran ƴan uwanka baku san da shi ba a gidan nan. Ina barin masu aikatawar ne kawai kafin ranar da zan masu bankaɗa da tonon silili a gaban kowa. Ni dai abinda zan sanar maka yanzu shine da ga Abdullahi har Nasiru ka zaunar da Zainabu ta zaɓi wanda tafi so tunda abin ya zama haka. Kokuma ta auri wani bare can a zauna lafiya. Sannan inason ka nutsu kayi tsai da hankalinka a wannan karon game da kowa a gidannan, koda baka fahimci duka abinda na fahimtaba zaka fahimci wasu daga ciki. Dan kai ne uba a gidan nan, duk da dama nauyi da girman ya rataya a wuyankane tunbayan rasuwar mahaifinku, ina kuma alfahari da yanda ka riƙe hakan, amma sai randa ƙasa ta rufe idanuna zaka sake tabbatar da girman dake bisa kanka da tarin fituntunun da ke kwance a cikin gidannan wanda ALLAH ne kawai hanasu fallasuwa saboda rahamarsa da ikonsa da kuma ƙarfin addu'ar mahaifinku da har yanzu take biye da ku. Kai dai ALLAH ya ƙara maka haƙuri da juriya kawai. Tashi kaje ka huta, ka kumayi ƙoƙarin tausar sauran ƴan uwanka akan duk ma abinda zai iya biyo baya game da wannan gagarumar fitinar da Abdullahi ya ɗaɗɗago mana”.
Kasa cewa komai baba malam yayi. Cike da ruɗanin maganganun Hajjo ya jinjina mata kansa kawai da miƙewa ya fice zuwa nasa sashen. Bai iske kowa a falon ba sai Muhammad dake karatun Al-Qur'ani na haddar da aka basu a islamiyya. Yaron bai dakata daga karatun da yakeyi ba, shima kuma bai masa magana ba ya wuce ɗakinsa.
Komai tsaf a gyare kamar yanda ya saba zuwa ya iske, ga ƙamshi mai daɗi. A ɗaya daga kujerun ya zube hankalinsa har yanzu baya tare da shi. Dan ransa da zuciyarsa cike suke da tarin ruɗanin kalaman mahaifiyar tasu. Shi kansa yasan akwai abubuwan dake kwance a gidan nan ƙwarai da gaske. Waɗanda da yawansu shi da iyalinsa sun cutu matuƙa a cikinsu. Koma yace suna kan cutuwa. Ya kumayi imani da ALLAH babu wani baƙon ido daga waje da zasuce yana aikata su, dolene mai aikatawar a cikin zuri'arsu yake. Yasha yin tunanin tsananta bincike, amma sai zuciyarsa ta gargaɗe sa da yin haƙuri, sannan yana mai tsananin jin tsoron wanda sakamakon ɓarnar zata tabbata a garesa. A ganinsa gara kawai a cigaba da tafiya a lulluɓen dan UBANGIJI mai ji ne kuma mai ganine akan kowa da komai..........
Taɓa shin da akayi ne ya saka tunaninsa katsewa. Duban Umm da tun ɗazun take masa magana yay. Fuskarta cike da damuwa tace, “Malam lafiya kuwa? Wane irin zurfafa tunanine haka? lna fatan dai lafiya ko?”.
“Humm! Jannat lafiyar nan da dauƙi”.
Saurin zama tayi hannunta riƙe da kofin data zuba masa ruwa tana faɗin, “Miya faru?”.
Ruwan ya fara karɓa ya sha, ta sake ƙara masa ya shanye sannan ya ajiye kofin ya labarta mata duk abinda ya faru, harma da zancen da Hajjo tai masa.
Duk da itama ta jima da ji a ranta duk abinda Hajjo ke zargi a kwaishi a gidan hakan bai hanata jin tashin hankali ba. Ita kanta tanason sanin mai aikata musu SARAN ƁOYE a lokuta da dama. Sai dai tsoron wanda zata gani yana aikatawar ke sakata sama ranta haƙuri da barin komai hannun UBANGIJI.
★★★★
A yau dai har dare Abdallah bai dawo gidanba duk jiran da su baba malam sukai zaman yi masa. Dole suka haƙura suka kwanta al'amarin nacin ransu da zuciya.
Washe gari bayan fitowa sallar asuba baba malam da sauran ƴan uwansa suka hallara gaba ɗaya a sashen mahaifiyarsu. Bayan sun gaisheta suka sake haɗuwa gaba ɗaya wajen bata haƙuri akan abinda Abdallah yayi, suka kuma tabbatar mata insha ALLAH zasu dai-daita komai ba sai yayi tsamari ba.
Batace da su komaiba dai, sai dai ta musu addu'ar nasara da nemawa Abdallah dama sauran yaran shiriya gaba ɗaya.
A wannan yinin maganar sakin ta shiga kunnen kowa dake a gidan ciki harda Addah da yaranta dake can suna shan biki. Aiko ba ƙaramin rikita musu lissafi Adawiya tayi ba. Dole babu shiri suka tattaro suka nufo kano zuciyar kowa babu daɗi.
Tunda saƙon saki ya isa kunnen Yusrah kuwa sai wani tarin farin ciki ya kamata. Bama tasan lokacin data shiga dirga tsalle akan gadon ɗakinsu ba. Kafin ta sakko da sauri ta shiga bayi ta ɗauro alwala. Salla tayi raka'a biyu na godiya ga ALLAH daya kawo ƙarewar wannan aure da ko tarewa batayi ba a cikinsa. Dama tunda su Adawiya suka diro ƙasar bata da wani sukuni. Shiyyasa ta koma yinin makarantar Tahfiz ɗin gidansu dan kawai ta gujema ganinsa. Hakan kuwa akayi, dan tunda suka iso sau biyu ta haɗu da shi. Ɗaya da daddare ya shigo sashensu wajen Abba. Na biyu kuma a sashen hajjo taje kai mata abinci. Duka a haɗuwar tasu gaisuwa ce kawai ta shiga tsakaninsu. Yanda baya sakar mata fuska itama bata shiga sabgarsa sam, dan baya wani nuna alamar akwai ko ɗigon haƙƙinta daya rataya a kansa ma. Hakan kuma bai dameta ba, to gashi cikin amincin ALLAH komai ya zama yanda taketa fata a kullum. Ba ƙaramin azumi da ƙiyamullaili tayi ba akan auren nan a cikin watannin nan. Dan ita kaɗai tasan dalilin rashin son auren.
Duk wannan ruguɗai da akeyi Nu'aymah batasan anai ba ita kam, dan Umm da baba malam babu wanda ya sanar mata. Sashen Hajjo kuma yanzu ba wani shigarsa takeba sosai saboda takurawar Nasir da Abdallah da suka maida sashen hajjo wajen zamansu. Ta gwammaci taita zama a sashensu, idan Muhammad na gidan susha shirmensu, idan kuma ya fita makaranta tayi kallo idan akwai wuta ko su zauna hira da Umm. Wani lokacin kuma tai barcinta dan Doctor ya ce ta dinga yawan barci, shiyyasa ma ya saka mata maganin barci a magungunanta.
Yauma tana a ɗaki tasha barcin rana har su Adawiya suka dawo bata saniba. Ta fito wanka tai sallar la'asar, shiri ta farayi da ƙudirin zuwa islamiyya yau dan tanajinta Alhmdllh. Tana tsaka da saka kaya ta jiyo kururuwar kuka kamar muryar Adawiya kuma. Saurin ƙarasa saka kayan tayi ta fito, a mamakinta duk ma sai ta iske ƴan gidan a tsakar gida kowa ya fito an rufu kan Adawiya. Gabantane ya faɗi da tunanin ko Accident sukayi a hanya. Da sauri ta shiga bin kowa da kallo sai taga kowa ma yana nan, harsu Aunty Aysha ma basu wuce gidajensu ba nan sukayo.
Kallon Jafar dake kusa da ita tayi tace, “Jafar miya faru wai?”.
“Aunty Nu'aymah ban saniba nima. Kawai dai naga Aunty Adawiya na kuka tana cewa wai indai aka rabata da Yah Ab zata mutu”.
Kafesa da kallo Nu'aymah tai tana son fassara kalaman nasa amma sunƙi fassaruwa. Dubanta ta kai ga Umm dake lallaɓa Adawiya taje sashensu amma taƙi, hakan ya sake tabbatar mata da lallai ba lafiya ba kuwa. Baba malam daya shigo gidan yanzunne ya dakama Adawiya tsawa. Jiki na rawa ta miƙe tsaye.
“Wane irin rashin hankaline wannan tun daga wajen gate anajin muryarki, tona mana asiri zakiyi da shirme ko mi?. To wlhy bara kuji bama ita ba duk wanda na sakejin bakinsa a wannan maganar saina ɓata masa rai, naga dai Abdallahn a ƙarƙashin ikonmu yake shima, dolene kuma yabi abinda mukeso inhar yana buƙatar gamawa da rayuwarsa lafiya. Kowa ya shige ciki”.
Jan ƙafa kowa ya shigayi zuwa sashensa. Kubrah ta kama hannun Adawiya suka shige tare. Inda suka bar Addah da bata fitaba nan suka isketa zaune. Babu wanda taima magana a cikinsu har suka zazzauna kowa na ƙannun magana. Batace musu komaiba dai har lokacin, saima jingina da tai da kujera ta lumshe idanu.
Nu'aymah suna shiga sashensu ta shiga tambayar Umm abinda ke faruwa. Dan ita harga ALLAH bata fahimci komaiba dai har yanzun. A taƙaice Umm ta faɗa mata, sai ko ta zabura a matuƙar razane. “Ya salam. Umm Yah Ab kuwa yana da hankali?! Wannan ai gogama mutane sharri ne da zai ce saboda ni ya aikata saki ga matansa”.
“Wannan sakaki a cikin da yayi shine ya sake tada mana hankali muma Nu'aymah. Dan zai iya zama wata fitina daban wadda ba'asan iyakar inda zata tsaya ba a gidan nan. Yanzu dai Abbanku ya gano inda yake, ya kuma bashi daga nan zuwa kwana uku idan bai dawo gida ba zai haɗu da ɓacin rai mai tsanani daga garesu”.
“Ai gara yazo ya kwance wannan ƙullin da yay min nikam, a dalilin mi zai sakani tsakkiya, a barni da abinda ya damenima nikam ya isheni Umm”. Tai maganar tana fashewa da kuka.
Tausayinta ne ya kama Umm sosai, ta ruƙo hannunta ta sakata jikinta tana lallashi............✍
😩 Yah Ab ya zaka mana haka ne?🤦🏻♀️🙆🏻♀️
_____________________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[5/24, 12:25 PM] +234 806 269 3623: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
Ina fatan ansha weekend lafiya? ☺️🤝🏻😘
No. 35
.............Kamar da wasa sai ga Abdallah ya shanye kwanaki ukun da baba malam ya bashi babu shi babu mai kama da shi. Ran baba malam da sauran ƴan uwansa ya sake ɓaci matuƙa, amma duk sunta ƙoƙarin dannewa. Dan hatta Hajjo ranta a ƙololuwar ɓace yake.
Hankalin Nu'aymah ne ya sake ta shi. Dan koba komai har yanzu tana son Yah Ab, bazata so bari ya cigaba da munana a idon iyayensu ba akan shima son da yake mata. Tunda duk abinda yake aikatawa na laifi a garesu a kanta ne.
Kuka sosai Nu'aymah tasha akan wannan al'amari. Musamman ma da itama tai kiransa da wayar Umm amma yaƙi ya ɗaga tun a ranar.
Yau ma wayar ta sake ɗakkowa ta Umm ta kirasa, sai dai bai ɗaga ɗin ba. Haƙura tayi da kiran, sai dai kuma bayan kamar awa guda kamar an tsikareta ta sake zuwa ta aro wayar again. Test massege ta tura masa, bakinta cike da addu'ar ALLAH yasa ya duba.
Bayan kamar mintuna biyar kuwa sai ga reply ɗinsa. Jikinta har rawa yake wajen ɗauka ta duba.
*_“Zan iya amsar gayyatarki akan dalili guda ɗaya, idan kin amince da shi ko yanzu zan iya dawowa gida na fuskanci iyayenmu”._*
_Dalilin kawai ki amince a ɗaura mana aure ranar bikin su Kubrah._
Wani irin mugun bugawa ƙirjin Nu'aymah yayi, tai mugun waro manyan idanunta waje hawaye masu zafi na rige-rigen fitowa. A fili cike da karyewar zuciya ta furta, ‘Anya kuwa Yah Ab bai fara shaye-shaye ba jama'a? Na shiga uku ni Zainab, wane irin tsaka mai wuya bawon ALLAHn nan yake ƙoƙarin jefani a gidan nan?’.
Kuka sosai ta kuma sha fiyema dana ɗazun, dan sai da taji kanta ya fara sara mata sannan ta haƙura. Har bayan anyi sallar isha'i bata fitaba ta cigaba da zama a ɗaki. Wayar Umm ma da Muhammad ya shigo aran littafinta na *Ahdhari* ta bashi ya kai mata. Yunwa ce ta fara takura mata, dole ta miƙe ta shiga bayi, wanka tayo ta fito, tai shirin cikin wando da riga na barci masu taushi. Tanajin yunwa amma bata jin cin abincin kuma, sha'awar shan lipton ne yazo mata a rai. Dan haka ta miƙe ta ɗauka hula ta saka a kanta sannan ta fito.
A falo sukaci karo da Rabi ɗauke da ƙaramin jug da alama ma ɗakinta zata. Baki Rabin ta washe ta na faɗin, “A'a uwar ɗakina kin tashi ashe? Kamar kinsan kuwa zoɓon nan zan kai miki dama ko zaki ɗansha dan na sanki da son zoɓo”.
Ɗan lumshe idanu Nu'aymah tayi ta buɗe akan rabin tana ɓata fuska kaɗan. “No bar zoɓon nan ma dai baba Rabi. Idan ban takura miki ba dan ALLAH haɗamin lipton kaina ciwo yake min”.
Da sauri Rabi tace, “Ah wlhy babu wani takura uwar masu gida. Kinga zauna bani mintuna biyar kacal, barama nai miki amfani da ganyen shayin baba malam, ina dai kina so ko?”.
Kai kawai Nu'aymah ta gyaɗa mata dan surutunta ya isheta. A ƙasan ranta kuma tana mamakin yanda Rabin ta amsa dafa mata shayin ɗin babu ko musu balle sukai ga faɗan da suka sabayi kullum.
Ɗakin Umm Nu'aymah ta nufa kafin Rabi ta kammala, sai dai ta iske tana wanka dan haka ta fito akan idan ta gama zata koma. Fitowarta dai-dai da fitowar Rabi da ga kitchen ɗauke da kofin shayi dake ta turiri. Sai da tai mata godiya sannan take tambayarta ko baba malam ya shigo?.
“A'a bai shigoba, dan naji Muhammad na faɗin kamar yayi baƙi ne ma”.
“Okay”.
Kawai Nu'aymah ta faɗa tare da ɗaukar kofin ruwan zafin ta kai bakinta tana ƙoƙarin kunna television da hannunta na haggu.
Sosai shayi yayma Nu'aymah daɗi, harta shanye wanda Rabi ta zuba mata itama ta sake zuba sauran wanda ya rage a butar shayin. Tana cikin shan wanda ta zuba ɗinne Umm ta fito...
“Oh dama kin tashi?”.
“Eh, nama shiga ɗakin na tarar kina wanka. Umm kaina ke min ciwo ALLAH”.
Cike da kulawa Umm dake dubanta tace, “Ba dole kanki yay ciwoba Nu'aymah, kukan da kikayine ai. Halan ma da kika tafi ɗakin ba barcin kikayi ba?”.
“Umm barcin nefa bai zoba. Amma yanzu naɗan fara ji, sai dai zan jira Abba ya shigo sannan naje na kwanta”.
“Wayasan sanda zai shigo, ki tashi kije ki kwanta banason sakarci. Miyasa ke wai sam baƙya tattalin lafiyarkine? Kin fison kullum ki ganmu hankali a tashe”.
“Kiyi haƙuri Umm ba haka baneba wlhy, dama dan yau duk bamu haɗu da Abba bane shiyyasa. Amma bara nasan insha ALLAHU da safe zamu haɗu. Sai da safe”.
“Ki tabbatar kinyi addu'a kafin ki kwanta”.
“To Umm”.
Nu'aymah ta faɗa tana nufar ɗakinta badan taso hakanba. Kamar jira tana kwanciya sai barci mai nauyi ya kwasheta batare da ko addu'ar da Umm ta gargaɗeta yi ba tayi ɗin.
★★
Sai wajen sha ɗaya baba malam ya shigo gidan. Koda ya tambayi Nu'aymah Umm ta sanar masa ta kwanta sai ya nufi ɗakinta. Yayi sallama kusan sau uku babu amsa, dan haka ya juyo falo yana faɗin, “Nayi magana shiru, inaga tayi barci ma”.
“Dama tace barci takeji, amma tsabar fitina wai zata zauna jiranka dan yau duk bata gankaba”.
Murmushi kawai baba malam yayi, amma baice komaiba.
Kusan ƙarfe sha biyu saura Nu'aymah ta farka da wani Masifaffen ciwon ciki. Juye-juye ta shigayi a kan gadon tana kiran sunan Umm. Tun abin na mata sama-sama harya fara fin ƙarfin tunaninta. Yunƙurawa tai da ƙyar ta tashi zaune tana ambaton ‘Innalillahi.....’ da ƙyar ta iya sakkowa da ga saman gadon. Sai dai yanda ƙafafunta da mararta suka riƙe sam bazata iya takawa ba.
Ƙasa ta durƙushe hannunta ɗaya riƙe da cikinta, ɗayan kuma ta dafe gado da shi tana matse idanu da cije baki. Cikin azabar data isheta ta fara ƙwalla kiran sunan Umm da baba malam tana roƙon suzo su taimaketa zata mutu. Yanda zufa ta jiƙeta