Showing 159001 words to 162000 words out of 318746 words
Ashe faɗan da Abdallah da Naser suka tafka ne a daren shekaran jiya daya bama kowa tsoro yajawo su baba malam canja shawara akan zaɓin Nu'aymah. Ananah da hajjo sukai dogon nazari da shawarar canja komai. Dan yanda abubuwan ke nan canja salo tabbas zumincinsu zai iya girgiza akan matsalar Naseer da Abdallah. Dan haka suka kira su baba malam a wannan daren tare da Abban Naseer daya iso suka tattauna. Abban Nasir shine ya bada shawarar hana Abdallah da Nasir gaba ɗaya. Ya kuma bada shawarar aurama Yoohan kamar yanda ya bukata dan a samu zaman lafiya. Hakan zai kawo masalahar Abdallah ya maida matansa. Nasir kuma yaje ya auri wata.
Kowa yayi na'am da wannan tunani na Abban Naser. Babu ɓata lokaci ko jinkiri suka kira Yoohan suka sanar masa. Yoohan kuma bai ɓata lokaci ba wajen sanarma papa. Sai dai yayi matuƙar mamakin ganin yanda Papa ya bashi goyon baya babu wani ja inja ko ƙalubalantar lamarin, ya kuma gargaɗesa karya sanarma Momynsa (Madam Chioma😸) shi zai sanar mata.
A wannan daren papa ya bada akai masa invitation na layin waya aka turama duk wanda yake da buƙatar gani a wajen ɗaurin auren ɗan nasa. Washe gari kuma ya ƙarasa dukan kai kawo da yake buƙata tare da bincikar duk yanda al'adar auren hausawa yake. Duk abinda ake buƙata sai da papa ya saya aka shiryasu a mota.
Anan kuwa kano su Abdallah basusan wace wainar ake toyawa ba. Kowannensu dai ya ɗauki alwashi akan ɗan uwansa tsakanin shi da Nasir. Hakan yasa sukaje ɗaurin auren kamar kowa cikin kwalliya ta musamman. Sai dai kuma ganin Yoohan da tawagar ƴan uwansa da abokai ya basu matuƙar mamaki. Gashi waje ya ƙure balle su tambayi iyayen nasu. Basu fita daga ruɗanin ganin Yoohan ba aka fara ɗaurin auren. An fara ɗaura na Kubrah da angonta Al-ameen yuseef durɓi, sai Hajarah da angonta Dawood Sulaiman Rano. Naseer na jiran yaji shi da Nu'aymah sai yaji Zainab Sooraj Hashim jibiya da Yahya Goshpower”.
Turƙashi zance ya girma. Ba Nasir kawaiba ne a ruɗani, Abdallah kansa hajijiya yaji tana ɗibarsa. Hakan yasa Omar dake kusa da shi ya taimaka masa suka fito daga cikin hayaniyar ya kaisa mota. Shima acan Nasir sai Ahmad ne ya kamashi ya fito da shi. Sun koma sanarma su baba malam, Abdallah ya tada motar da Omar ya sakashi ciki ya bar wajen batare da kowa ya sani ba. Nasir kam da ƙafa ya bar wajen shima a birkice.
Daga wannan tafiyar ne har yanzu babu wanda yasan ina suke. Su baba malam sunyi neman a waya harsun gaji. Dan duk wayoyinsu a kashe suke. Halin da suka ahigo suka iske Nu'aymah a gidane ya sakasu yin shiru da zancen rashin su Abdallah ga kowa. Duk da kuwa Hajjo nata tambayarsu bataga Abdallah da Nasir ba.
WASHE GARI..........✍
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 44
*_IDAN kaji ƙi gudu sai in sa gudu bai shigo wajen ba. Ƴan uwa abokan tafiya, gafa magani A GONAR YARO. domin tabbas idan kaji gangami akwai labari_*.
*_Ina masu wahala kullum cikin neman maganin sanyi (imfection) amma babu biyan buƙata. Kinyi na asibiti har kin gaji babu canji, na gargajiyarma taɓawa kike babu wani ƙyaƙyƙyawan sakamakon. Tofa kakarku ta yanke saƙa. Domin kuwa ga dama a tafin hannunku. Munada maganin NI'IMA, maganin GYARAN HIPS (mai gida bye bye😉). Muna da maganin BOOBS (mai gida welcome🙈). Maganin BASIR mai hana sakewar zama. Duk ku garzayo domin samunsu akan farashi mai sauƙi da rahusa, ga kuma inganci domin an samosu ne daga tsaftatacciyar hanya mai nagarta._*👇🏻
*AISHA S BAYERO TRADITIONAL MEDICINE AND HERBAL RESEARCH CENTER...*
_KUNJI SUNAN KO? CENTER CE TA MAGUNGUNAN GARGAJIA, WANDA DUK WANI DAMUWA DAKE DAMUNKA IDAN HAR KAZO WAJEN S BAYERO TA KARE DA YARDAR ALLAH.. KADAN DAGA MAGUNGUNANTA SUN KUNSHI:_
_MAGANIN SANYI_
_MAGANIN NI'IMA SET_
_MAGANIN NANKARWA_
_MAGANIN KIBA BABBA DA KARAMI_
_MAGANIN HIPS_
_MAGANIN GYARAN NONO_
_MAGANIN RAGE KIBA_
_MAGANIN SAKA FEELING_
_MAGANIN CIDA KWAI_
_ZUMA YAR ASALI_
_MAGANIN BASIR KOWANNE IRI_
_HODAR NI’IMA_
_MAGANIN MALLAKA_
_GUMBAR NONON RAK’UMI_
_GUMBAR MADARA_
_TURAREN FARIN JINI_
_KAZA MARA KWAI_
_TURAREN MALLAKA 3 STEP_
_HAD’IN MATAR MINISTER 1_
_KAZA ME KWAI_
_STEP 2:_
_TURAREN MALLAKA ME KWALBA_
_ME KUNAMA DAN MATSI_
_TURAREN GOSHI_
_TURAREN QIRJI_
_TAUWADAR MATA_
_MEMORY_
_KAHON MALLAKA_
_YAJIN MAZA_
_TEA DIN MAZA_
_DAMBUN MATSI_
_MAN AYU_
_MAN DAMO PURE_
_KWALLIN IDONKA IDONA_
_GARIN SHA DAKA ME KYAU_
_KUBEWAR MATA_
_DUKA WADANNAN INGATTUN MAGUNGUNA NA GARGAJIYA HAJ AISHA NA DASU GANGARIYA.. HERBAL MAGUNGUNA NE MASU KYAU DA INGANCI.. TAFIYAYYU NA KASAR CHAD. CHADIAN HERBAL MEDICINE AND RESEARCH CENTER.. KYAU, INGANCI.. RAHUSA... SAI MAGUNGUNAN *AISHA S BAYERO TRADITIONAL MED AND HERBAL RESEARCH CENTER....*_
_NUMBER WAYAR WHATSAPP: 08121491609 KO KIRA TA NUMBER 08145873617._
_ADIRESHI: KUNTAU KARSHEN KWALTA KAN A KARASA YAN TIFA, DAIyDAI GADON KAYA CEMENT.._
Sai kunzo😘😘🤝🏻
_________________________
No. 44
..........WASHE GARI normal Nu'aymah ta tashi kamar yanda kowa yay fata. Sai dai rashin ƙarfin jiki da damuwar maganar auren da ta sake tabbatar an ɗaura mata shi. Dan bayan baba malam ya dawo daga massallaci zaunar da ita yay ya ringa mata nasiha mai ratsa jiki da ɓargo. Tun tana hawayen zuci, harta koma na zahiri. Hawaye suka dinga kwarara mata daga ido suna sauka saman fuska.
Fuskar baba malam ɗauke da murmushi ya kai hannu ya share mata hayen. Ya kamo hannayenta duka cikin nashi yana sake kwantar mata da hankali. “Kukan ya isa haka kinji mamana. Duk abinda kikaga ya shigo cikin rayuwarki saɓanin tunaninki ki ɗauka hakan shine mafi alkairi a gareki. Idan kuma har kika rasa abinda ke shine burinki da fatanki, ki saka a ranki UBANGIJI bai baki shi bane saboda ba naki bane, hanakin kuma shine yafi alkairi. Akwai abubuwa da yawa dana san suna damunki a cikin rai. Amma inason ki ɗaukesu ki watsar da su acan nesa, ki kuma manta da su ki shafe babinsu a tunaninki. Dan jiyanki ta wuce, kina cikin yau ɗinki ne. Kinga yafi kamata ki maida hankali wajen hangen gobenki. ALLAH yay miki albarka. Ya yaye miki damuwarki. Ya share hawayenki. Yay riƙo da hannunki. Yay miki jagora a gobenki da jibinki”.
“Amin Abbah na gode, ALLAH ya ƙara maka lafiya da tsahon rai”.
“Amin mamana nima na gode. Kije ki kwanta ki sake hutawa kinji. Sai dai ki zama cikin shiri dan zuwa jibi idan ALLAH ya kaimu kema za a miƙaki gidan mijinki”.
Kanta kawai ta ɗaga masa. kamar zata tambayesa waye mijin nata sai kuma tayi shiru. Ɗago idanunta dake jajur tai ta kallesa. Muryarta na rawa tace, “Abba dan ALLAH ka yafemin dukan abinda kake ganin na maka a sanina ko saɓanin haka. Sannan wlhy kaji na rantse ban aikata abinda likitocin nan suka tabbatar ba. Abinda ke a cikin hotunan nan kuma ya farune bisa ƙaddara........”
Duk abinda ya faru a waɗan nan ranakun biyu sai da Nu'aymah ta sanarma baba malam. hatta da farkon haɗuwarta da Yoohan. Sosai baba malam ya gamsu da dukan bayaninta. Dan duk abinda Yoohan ya faɗa shine ta maimaita. Inda sukai saɓani kawai shine ita tana ganin da gangan ya aikata mata. Shi kuma ya sanar dasu baba malam duk akan taimakonta zata faɗi komai ya faru. Ya san Nu'aymah tun tana yarinyarta da wahala kaji tamaka ƙarya akan abu. Koda kuwa za'a daketa idan tai laifi aka tambayeta saita faɗa.
“Na yarda da ke Mamana. Insha ALLAHU kuma zamu ƙara sanin gaskiyar daga ina zancen ya fito. Dan wasu kalaman mijinki akan maganarnan suna nan tsaye bisa ƙwalwata ina musu fashin baƙi a hankali. Kuma lallai da gaske na fara ganin haske a ciki”.
“Abba na gode daka fahimceni”. Ta faɗa tana kuka da dariya lokaci ɗaya. Shima Murmushin ya keyi cike da tausayinta. Daga haka suka fara cin abincin da Umm ta shirya masa na breakfast shi da ita. Tana bashi a baki shima yana bata abin sha'awa.
Janyewa inuwar dake jikin windown tayi, baba malam da sai yanzu ya farga yay tsai yana kallon jikin Window ɗin cike da mamaki da al'ajabi. Sai dai kuma a zahiri ya maida hankalinsa ga Aymah ne. Daga can wani gefe na zuciyarsa yace, ‘Taya zakai zargin an muku laɓe ne bayan gidan cike yake da baƙi. Maybe wanine ke wani abu a wajen dai’. Ɗari bisa ɗari ya gamsu da hakan har cikin ransa. dan haka ya sake maida hankalinsa ga ɗiyarsa da tausayinta ke cike taf da ransa.
Bayan baba malam ya shirya ya fita Nu'aymah ta koma sashen Umm. Ƙannen Umm ɗin da yayunta duk suna nan. Breakfast ma sukeyi. Sai wasu daga ƴan uwan Adda da suma anan suka kwana. Cike da jin daɗin ganinta ras duk suke kallonta. Ta risini ta gaidasu. Daga haka ta fito sashen hajjo. Nanma sunyi farin cikin ganin ta tashi lafiya kamar ba ita ba. Gaishe da baƙin dake a sashen tayi sannan ta shige bedroom ɗin hajjo. Acan tai wankanta tsaf, Yusrah data shigo taje ta amso mata kaya. Bayan ta shirya tare da Yusrahn suka fito. Hakan yayi dai-dai da shigowar Adawiya falon hannunta ɗauke da bokiti ruwan goro.
Tunda sukazo ƙasar wannan shine gani na uku da Aymah tai mata. Adawiyan duk ta rame, tayi duhu kamar ba itace sukazo tayi ɗam da ita kamar zata fashe ba dan ƙyau. Ɗauke kanta tayi tamkar bataga Aymah da Yusrah ɗinba. Ta ƙarasa gaban Ananah ta ajiye bokitin tana faɗin, “Ananah gashi inji Addah na ƴan katsina ne da zasu wuce yau”.
“To. To masha ALLAH, ALLAH ya sanya alkairi yasa albarka. Kice mata angode ALLAH yayi albarka”.
“Amin” ta faɗa tana ƙoƙarin gitta su Nu'aymah zata fice. Murmushi Aymah tayi, tare da cewa, “Adawiya an tashi lafiya?”. Da mamaki Adawiya ta juyo ta kalli Nu'aymah. Kamar bazata amsaba sai kuma tace, “Alhmdllh”. Daga haka ta fice abinta.
Yusrah tace, “Humm ALLAH ya ƙyauta. Wlhy lamarin Adawiya har mamaki yake bani Aymah. Ita yanzu dai abinda take nunawa ta raba zuminci damu. Nifa tunda sukazo ƙasarnan batamin magana. Idan na mata kuma saita amsani kamar wata kashi. Koda yake kema da kuka shaƙu da ita fiye da kowa tana ɗaga miki hanci bare mu”.
Murmushi kawai Aymah tayi, amma batace komaiba. Daga Ananah har hajjo duk suna jinsu suma. Amma sai sukai kamar basujinba.
An ƙarasa gudanar da shagalin biki yau. Zuwa bayan azhar sukaje gidan amare akai buɗan kai. duk baƙi masu tafiya daga can suka kama gabansu. Sai ɗai ɗai kune suka dawo nan gidan waɗanda su sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu. Nu'aymah dai tana gida bataje ko inaba. Cikin ranta kam fal damuwa dason sanin wanene ita aka ɗaura mata aure da shi?. Anya kuwa Naser ne datai fata? A ganinta idan shine yaci ace ta gansa ai. Amma tunda ta tashi daga Naseer har Abdallah bataga kowa ba a cikinsu. Kuma duk sauran samarin gidan ta gansu.
_________★★★★_________
*_FCT ABUJA_*
A birnin tarayya kam taƙaddama ake bugawa sosai tsakanin Yoohan da kakanninsa. Harma da wasu a cikin ƴan uwansa da suke nuna borensu akan auro Nu'aymah da yayi. Hayaniyarsu da haukarsu duk bata damesa ba. Yamayi kunnen uwar shegu da su tamkar baiji akan mi sukeyi ba. Babban tashin hankalinsa da damuwarsa kawai halin da Momynsa ke a ciki.
Dan tun daren jiya jininta ya hau sama sosai saida ya danna mata allurar barci, har kuma yanzun bata farka ba saboda mai ƙarfi sosai yay mata. Su Richard ne kawai da suma suka so tasashi gaba da magana akan auren yay azamar taka musu burki. Dukansu sunsan halinsa, idan rashin mutuncinne da buyagi duk ya fisu iyawa. Sannan suma ɗin kowanne allazi da nasa amanu ai. Kuma babu wanda sirrinsa ba'a tafin hanunsa yake ba. Haƙuri suka bashi akan masa katsalandan ɗin da sukayi. Suka kuma nuna masa zasu basa goyen baya tunda yana son matarsa.
Uffan baice da su ba daga haka. Su kuma duk suka tashi suka fice suka barsa. Fita sukai daga gidan duka, sai da sukasha gulmarsu iya iyawa a waje kafin su tattauna akan shagalin biki da suke son shirya masa tunda auren nasa yazo musu da salo na daban ba irin nasu ba.
A cikin gida ma bayan su mama Debora sun turza sun turza akan Yoohan ɗin sunga babu mafita sai suka sakko dan kansu akan zasu amince da auren, sai dai da sharaɗin duk sun dawo da zama gidan papa. dolene kuma Nu'aymah ta zauna itama a gidan Yoohan bazai kaita ko ina ba.
Sai dai a mamakinsu sai sukaga Yoohan yayi murmushi tare da lumshe idanunsa ya buɗe a kansu. Sai da yay musu kallon tsaf na wasu mintuna kafin ya miƙe cike da basarwa yace, “Na amince”. A ransa kuwa dariya ya tafi yana musu, dan yasan indai nu'aymah ce sun sami dai-dai dasu.
Kusan duk a tare sukai wata irin zabura. Dan sam sun zata zaice bai yardaba su kuma su sake tada wani billin. Sai gashi sunga saɓanin tunaninsu. Kafin su gama dawowa hayyacinsu ya dawo falon ɗauke da takarda. A tebirin dake tsakkiyar falon ya ajiyeta. Ya bisu da kallo fuska a murtuke yana faɗin, “Wannan takarda ce ta agreement tsakanina da ku. Zaku cigaba da zama a gidan nan, matata ma zata zauna. Sai dai da sharaɗin duk randa na kama wani da laifin mata koda maganar banza a cikinku ko cikin yaranku sai mutum yabar gidan nan koda ace kuwa cikin su Gebrail ne. Itama kuma na muku alƙawarin bazata shiga rayuwarku ba bayan mutuntawa da girmamaku”.
Cike da wani mamakin suke kallonsa. Zasuyi magana papa yay saurin faɗin, “Wannan tsarin na John yayi dai-dai. Dan shine zai kawo mana masalaha da kwanciyar hankali a zuri'ar mu. Mukuma sake tabbatar da kowannenmu nada ƴancin aikata abinda bai saɓamana ba”.
Babu wanda ya iya sake cewa komai. Sai singing ɗin da Yoohan ya fara yi ya basu suma duk sukayi. Ɗaya ya ɗauka ya basu ɗaya. Ɗayan copy ɗin kuma da aka saka cikin frame ya nufi bangon falon daga kusurwar d/table ya kafesa jikin ginshiƙin wajen daya zama kwalliya.
Wannan abu da Yoohan ɗin yayi ya kuma girgiza su matuƙa. Gashi babu damar magana dan ya tsuke fuskar fiye da ɗazun.
Wannan takardar Agreement itace ta zama makullun rufe bakin duk wanda keda ƙarfin faɗa a ji a family ɗin su Yoohan. Sai ma zaman shirya biki sukai dan nuna bajintarsu ga gudan jininsu tamkar yanda akema kowa.
Shi dai Yoohan bai tanka kowa a cikinsu ba akan shirin bikin, ranarma yini yayi a asibiti shi da Richard. Basu dawo ba sai dare. Gajiyar da sukayi ce ta sakasu ko zaman hira basuyi ba Yoohan ya shige sashensa. yau ma tsabar wulaƙanci hana su Rich shiga yayi. da sukai magana yace shi yanzu yayi aure baya buƙatar su a sashensa. Suje can su ƙarata a sashen baƙi suyita loda kwalaben barasarsu.
Aiko sun hayayyaƙo masa tamkar zasu cinyesa. Ya fice yana murmushi bayan ya musu gwalo.
______★★★_______
*_KANO_*
A kano kam tunda garin ALLAH ya waye yau da shirye-shiryen tahowar su Nu'aymah aka tashi. Dan zasu taho abuja gidan su Abdallah. washe gari sai a miƙata ɗakin mijinta daga nan gidan. Saboda ma baba malam baya buƙatar ayi wata gayya jirgi zasu biyo.
Jin abuja zasu wuto yasa Nu'aymah fara tunanin ko dai yah Ab aka ɗaura mata aure da shi? Ko burinsu na mallakar juna ya tabbata ne? To amma idan har hakane mizaisa a ringa ɓoye mata?. Har yanzu babu wanda ya sanar mata wanene mijinta. sai dai kowa na zaunar da ita yay mata nasiha dai-dai gwargwadon saninsa. Haka ne yasa yau taci kuka harta godema UBANGIJI. Mai ƙunshi ma da Addah tasa aka kawo da ƙyar Aymah ta yarda akai mata. Hakama da za'a kaita gyaran jiki sai da baba malan ya saka baki wajen lallashinta sannan ta amince. Ai ko sai gata tayi ɗas tamkar ka saceta ga gudu. ƴar ramar da tayi saita sake ƙara fiddo mata da ƙyawunta da haskenta. Sai dai a kallo ɗaya kaɗai ya isa ka tausaya mata duk tayo laushi kamar ba Nu'aymah tsiwa ba. Duk ta zama shiru-shiru, ta kuma nanema Umm taƙi barinta sukuni.
Lokacin da aka idar da sallar la'asar Ananah tazo har sashensu tajata dan taje a kimtsata tunda jirgin 5:30pm zasu bi saita saka musu sabon rikici. Babu wanda bai lallasheta ba amma taƙi tai shiru. Sai da baba malam ya fito yay mata jan ido da nuna mata ɓacin ransa sannan. Aiko tana kuka tana sharɓar hawaye. Koda ta fito ma sai Aunty Kulu yayar Naser ce tai mata kwalliya ka ɗan dukda kuwa ba wai gidan su Yoohan ɗin zata sauka kai tsaye ba.
Tsaf ta sakata ta shirya cikin atamfa lass ƴar ubansu, ɗinkin zani da riga. Kasancewar atamfar baƙa ce da kwalliyar golden sai tai bala'in zama mata a jiki tamkar ka saceta ka gudu.
Iyayenta sun sake taruwa a kanta sun mata nasiha da gargaɗi mai faɗi akan rayuwar da zata fuskanta ta aure mai cike da ƙalubale. Dan aure ibadane. Ita kuma ibada a koda yaushe tana a cike ne da jarabawa kala-kala. Daga haka aka miƙata wajen Umm tai mata sallama. Ba Umm da Nu'aymah kawaiba, hatta duk wanda ke a wajen sai