Showing 54001 words to 57000 words out of 318746 words

Chapter 19 - saran boye complete by Queen meenali

01 Jul 2024

41600

yaran gidan marayun nan suma. Shiyasa suma yaran suna tsananin ƙaunar wannan family, su suke ɗauka danginsu da komai a rayuwa.

★★★★★

             “Wai wannan akwatin da kika lodama kaya duk na miye Nu'aymah?”. Umm data shigo ɗakin Nu'aymah ta faɗa tanabin Nu'aymahr daketa shirin kaya da kallo.
     Ɗagowa tai ta kalli Umm cike da ɗoki, “Umm yo na bikine mana, sati guda zamuyi a can”.  “To lallai, ashema kune iyayen bikin kenan?”. Dariya Nu'aymah tayi dajin zancen Umm, Umm kam daga haka bata sake cewa komaiba ta ajiye mata magungunan ta tana faɗin, “Gasu nan, saura kije kita wasa da shansu Nu'aymah, dan ALLAH ki kula da kanki, duk abinda kikasan zai zame miki matsala ki kujesa, ku kuma riƙe mutuncin kanku, na kira Baba Habi a sashenta zaku zauna kafin Hajjo ta iso gobe idan ALLAH ya kaimu, saura naji wani abu mara ƙyau na shegen tsiwanki, ALLAH saina ɓata miki rai”.
        “Umm insha ALLAH bazakiji komaiba ma”. “ALLAH yasa”. Umm ta faɗa tana juyawa ta fice daga ɗakin..

          Bayan sallar azhar su Nu'aymah sukai sallama da kowa suka wuce, Yah Abubakar ne ya kaisu. Da yake shima irinsu ne ɗan taraliya saida ya kaisu sukai shopping sannan ya wuce dasu gidan marayun.
     Ƙaton gaske ne, sannan an ƙawatashi ta ko ina babu makusa. Akwai makaranta da asibiti da duk ma abinda masu rayuwa da iyayensu suke samu. Makarantarsu ta fara tun daga noziri har zuwa sakandire. Ana koyar da boko da arabic, idan kaji yanda yaran ke larabci da turanci sai kasha mamaki da al'ajabi. Rayuwarsu suke cike da farin ciki da jin daɗi wadda ko wasu masu iyayenma basa samu. Gasu da tarbiyya abin birgewa.
     Ɓata lokacine zama bayyana muku yanda gidan marayun nan ya ginu da tsari mai ƙyau, kusa a ranku kawai ya haɗu. Dan sosai su baba malam ke samu taimakon manyan mutane dama masu mulki game da riƙe gidan. Ga kuma suma kansu masu nemane basu zauna jiran na sadakaba. Kaso mafi yawa na ɗunbin dukiyarsu yana tafiyane wajen tattalin rayuwar marayun nan da kulawa da su. Shiyyasa Alhmdllh da wahala ace sun nema abu sun rasa. Sai dai ace yau da gobe sai ALLAH, komai arziƙinka dama wani abun sai ya gagareka.
       A yanda su Nu'aymah suka sami tarba zai tabbatar maka da sanannune a gidan, kuma ba wannanne farkon zuwansu su kwanaba. Dan rigima aka shigayi musamman ga sa'anninsu, kowa na faɗin sashinsu su Nu'ayma zasu sauka. Bayan ansha taƙaddama dai kowa ya haƙura zasu zauna a sashen da amare suke, wato sashen baba habi da Umm ta faɗama Nu'aymah tun a gida.
        A yau kowa ya kalli Nu'aymah yasan tana cikin farin ciki sosai, haƙoranta sun kasa rufuwa. Tsiyarsu sukaita tsulawa uwa ba kwaɓa uba babu tsanani, dan suna son suga sunzo gidan nan, shiyyasa wani lokacin baba malam da kansa yake cewa suzo suyi weekend ɗinsu anan, dama anan duk yaran gidansu ke karatunsu tun daga noziri har zuwa sakandire, shiyyasa sukeda shaƙuwa sosai da yaran gidan marayun fiye da zaton mai tunani.

     Washe gari Nanah tace suma gasunan zuwa ita dasu Suhailat, hakan yasa bayan sallar la'asar ana tsaka da musu ƙunshi dan ranar itace suka saka ranar ƙunshin, Nanah ta kira wayar Yusrah ta sanar musu gasu a bakin titi suzo su shiga dasu dan baza'a barsu su shigaba kai tsaye.
        Nu'aymah da Yusrah da biyu cikin ƴammatan gidan suka fita shigowa da su Nanah dansu ƙunshinsu harya bushe sun wanke, Nu'aymah ce kawai bata wanke nata ba amma ya bushe. da ƴar tafiya tsakanin gate da gidajen yaran, amma haka suka taka a ƙasa suna hira har suka iso. suna a gab da fitane suka haɗu da yaran gidan maza da bazasu gaza shekaru sha biyu ba kusan su bakwai wai wajen ball suka tilla ƙwallon waje ta katanga shine zasu zagaya ɗakkowa. Security ɗaya ne tare dasu zai rakasu. A tare suka fita dasu Nu'aymah da zasuje tarbar su Nanah.
       Gidan marayun yana akan babban titine, shiyyasa sam ba'a barin yaran fitowa ko ina su kaɗai koda hakan ta kama sai da security.
     
        Dariya Nu'aymah tai ganin su Nanah acan ɗayan tsallaken basu tsallakoba, tasan Nanah matsoraciyace akan tsallaka titi dama, shiyyasa yanzuma abun ya bata dariya data tuna. Su Yusrah ma dariya suka sanya famhimtar dariyar Nu'aymah da sukayi. Bayan sun kalla ɓangare biyu na titin babu mota suka sa kai zasu tsallaka. Da sauri security ɗin daya rako yaran nan yasa hannu ya fisgo Nu'aymah dake ƙarshen tafiya saboda tahowar wasu motoci guda uku a jere cikin masifaffen gudu.
        Ta juya zataima security ɗin masifar taɓatan da yayi dukda tasan hakan na halinsu bane sukaji razananniyar ƙarar ɗaya daga cikin yaran wanda motar farko ta kwashesa yana ƙoƙarin ɗakko gyalen Nu'aymah daya zame ya faɗi lokacin da security ɗin nan ke ƙoƙarin maidota baya.
         “Ƙuuuuuwww!!!” motocin suka bada sautin taka birki a tare, yayinda mai napep dake bayansu ya bugi motar ƙarshe shima.
      A tare su Nu'aymah suka fasa ƙara da rumtse idanu kunnuwansu a toshe da hannayensu, sai da sukaji tsitt sannan suka bubbuɗe ido dan son ganin yaya akayi.
       “Innalillahi.... Suka shiga ambata kusan a tare saboda hango yaron a kwance ƙasa cikin jini. Sunma manta a titi suke, suka tafi da gudu kansa suka rufu masa. Sunkai mintuna uku akan yaron nan suna kuka da jujjuyashi amma ko mutum ɗaya bai fito daga motocin nan uku ba balle kai tunanin sunsan ma abinda suka aikata. Cikin tsananin fushi da zafin zuciyar gado Nu'aymah ta rarumi wani dutse dake a gefen titin ta nufi motar tsakkiya dake a saitinta, wadda kuma tafi kowacce haɗuwa da ƙyau ta buga dutsen jikin glass ɗin.
      Ko gezau glass ɗin baiyiba, dan haka ta koma na gaba wanda tasan insha ALLAH zata dace ta sake bugawa da iya ƙarfinta. Aiko a take ya shiga tsatstsagewa. Ta sake ɗagawa zata buga aka riƙe mata hannu. Fisge hannun nata tai ƙoƙarin yi ta kasa, dan haka ta juyo bakinta cike da tsiwa.
      Ido huɗu tayi da manyan garada masu suffar ƴan dambe cikin baƙaƙen suit da glasess zagaye da ita su shidda, daka gansu kaga cikakkun marasa imani dan babu alamar sunsan ma minene dariya a rayuwarsu, babu tantama kuma zasu iya halaka mutum batare da sunji koda ɗar ba.
        A mamakinsu sai gani sukai ta ɗaga dutsen ta bugama wanda ya riƙe mata hannu a goshi. Saurin sakinta yay ya dafe goshinsa daya fashe a take ya fara zubda jini.
        Kusan a tare suka fiddo bindigu suka nunata da shi. Duk da Nu'aymah tasan zasu iya harbin nata ta mutu kuma, amma sam cikin idanunta babu tsoronsu, saima masifa dake cinta. Haka take ita sam batasan tsoroba. Idan kaga tsoro ga Nu'aymah to duhu ne ko tsawa, ko allura.
       Ɗasss! Ɗasssss!! Ɗassssss!!!
Sukaji sautin buga yatsu a bayansu. Gani tai duk sunja baya daga kusa da ita amma basu sauke bindugunba, sundai risinar da kawunansu ƙasa na alamar girmamawa ga koma wanene mai buga yatsun.
        Kamar bazata juyaba sai zuciyarta ta bata shawarar juyawa taga wane shahararran ƙwallan mara imanine da mutuncine shiɗin...........✍

Nidai nama rufe idona bazan gansa ɗinba😎🚶🏻.

Yau dai ga dogon page nan ku more harda na jiya na haɗa muku. Saura kuma naji wata tace bai isheta ba😚😏😣🚶🏻🚶🏻🚶🏻


__________________________________
_____________________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________
  
                
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
  
          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.

*_Typing📲_*

No. 12

________________________
*ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE*

       *_KAJI shahararrun kuma mandiyoyin ƴan ƙwalisar kawo kayan kitchen masu tafiya dai-dai da zamani. Idan nace nadaban ina nufin suɗin nadabanne wajen kaya ƴan gaske dake ƙawata kitchen ɗin amarya harma dana uwargida ƴar ƙwalisa. Ka siya ka tabbatar ka saya ɗin ko a gaban tsaranka sai ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE. sunan kayansu sa kishiya cin bashi🤣, dan tana ƙyalla ido taga kitchen ɗinki tsarin amerikawa tuni zata fara ƙwafa da tunanin zuwa gidan delu dillaliliya mai saida kwanika. Sai dai kuma kama da wane akace bata wane, dan haka ku maza ku garzaya ZEESMART KITCHEN UTENSILS AND MORE. domin samun naku kuma. Suna kawo kaya daga ƙasashen ƙetare akan farashi mai sauƙi da rahusa. Suna order ɗin products kamarsu, dukan kayan kitchen na zamani, bedsheets, shoes dade sauransu, products ɗinsu pre-order ne dake zuwa akan lokaci batare da mai kaya ya ƙosa da jira ba ko samun matsala. Zaku iya samunsu a Number waya kamar haka ko Location nasu. Phone number: 08102393622. Location Gombe. Amma Zasu iya turawa kowani gari dake a lungu da saƙo na ƙasarnan. Sayen nagari maida kuɗi gida. Ku garzaya kar ayi babu ku. Da ƙyar nasha yafi da ƙyar aka kamani inji masu iya magana😉😘😘😍😋._*

___________________

................Sai da ya kammala ƙalular shirinsa cikin kayan barci wando 3quarter da riga Armless sannan ya zura slippers masu taushi ya fita. Kusan su shidda ya iske a falon kowa da hidimar da yakeyi. Wasu kallo wasu danna waya wasu surutu.
     Da sauri Miracle ta ɗauki remote ta rage ƙarar television ɗin dan tasan ya tsani hakan. Shikam baimabi takan kowaba ya nufi d/table. Kafin ya ƙarasa Miracle ta rigashi isa, yana ɗaura hannunsa saman kujera zai jata baya ta ɗora nata akan nashi. A take fuskarsa ta sake tsukewa, ya ɗago fararen idanunsa ya zuba mata wani banzan kallo. Maimakon ta janye hannun saita kashe masa ido ɗaya tana murzawa a hankali. Kallon hannun yayi cike da tsantsar fushi. Duk da tsoronsa dana yanayinsa a yanzu ke ratsata bata fasaba, saima karta zaƙo-zaƙon faratan ta ta farayi tana matsawa da hannunta gaba akan nashin cike da salon iskanci.
          Ita da kujerar ya haɗa ya wancakalar gefe, kafin takai ƙasa ya bita da halbi, sai gata ƙasa wanwar. Ƙarar data firgita kowa a gidan ta ƙwalla tana faman ihu kamar wadda aka yanka. Dukansu kanta sukayo, yayinda Yoohan ya sake ɗaga hannu zai ƙwaɗa mata mari Gebrail ƙaninsa yay saurin riƙesa, fisgewa yay yayi ƙwallo da kujerar kusa da shi ta dining ɗin ya juya fuuu kamar wani kumurci ya nufi sama. Da sauri Mom data fito daga wani ƙofa yanzu saboda jiyo ihun Mira ta shiga ƙwala masa kira da turanci. “Yoohan! Yoohan!! Yi hakuri zo kaci abinci”.
      Baiko waiwayeba balle tai tunanin samun amsa. Da gudu ta bisa tana haɗa steps ɗin da bibbiyu. Kafin ta ƙarasa har ya tura ƙofar ya maida ya rufe. Bugawa Mom ta shigayi tana kiransa cike da lallashi “Yoohan! yi haƙuri kaji, kar kayi fushi zo kaci abinci Please”. Duk da yaransu take maganar, amma yaƙi buɗe mata. Shi tunima yabar jikin ƙofar harya shige bedroom ɗinsa.
        Zuciyarsa cike da matsanancin ƙunci ya faɗa saman gadonsa ya kwanta a rufda ciki. Ji yake gaba ɗaya duniyar ta masa masifar ɗaci, yaja filo ya danne kansa da shi da ƙarfi.

      A falo kam Mom data sakko a ranta a ƙuntace ta ƙarasa inda Mira ke faman kuka har yanzu, cikin faɗa tace, “Miracle bance ki fita hanyar Yoohan bane? Kin riga da kinsan halinsa baya son wannan banzan halayar amma ke kam bazaki kama kankiba. Ki cigaba, wataran idan ya karyaki ko ya miki mugun dukan da za'a gaza ganeki zaki kiyayesa ai”. Batare da ta saurari amsa daga Mira ba ta wuce ɗakinta cikin fushi itama, dan a rayuwarta ta mugun tsanar ganin an ɓatama Yoohan rai a gidan. Tana masifar son yaronta fiye da sauran ƴaƴanta.
          Kuka Mira ta sake ɓarkewa da shi iya ƙarfinta su Joy na lallashinta, da ƙyar suka iya ɗagata dan tanada jiki sosai bawai siririya bace, sannan a shekaru sai dai suyi sa'anni ma da Gebrail ƙanin Yoohan ɗin.
      Da taimakon su Joy Miracle taje ɗakinta, sai da suka kwantar da ita a gado Gebrail ya kalleta shima cike da takaicinta. “Mira idan baki fita hanyar Brother ba na tabbatar shine zai maidaki gurguwa kafin ki koma gidanku, nasha faɗa miki shifa a rayuwarsa yanda ya tsani shan giya haka ya tsani harka da mata. Wanda yay kashi biyu cikin ukun rayuwarsa a turai matan can basu sakashi ya iskance ba ta yaya kike tunanin ke ƙaramar ƙwaruwar Najeriya zata iya sakashi aikatawa? Ƙilama dakin kama kankine zai soki kamar yanda kikai fata, amma a haka ina tabbatar miki tsanarki yake ƙarayi dan baya ɗaukar lamarin ta fuskar soyayya, idan kinji shawarata sai ki kiyaye”. Yana gama faɗa ya juya yay ficewarsa, kafin duk suma sauran su fito a barta daga ita sai Joy da take kusan sa'arta itama. Dan twins ne ita da Gebrail ɗin. Hawayenta ta share tana danna ƙafarta data buge, da yarensu tace, “Joy wai miyasa Brother ɗinku bashi da kirki?, gashi duk iskancin da wulaƙancin da yakema mutane su Mom sai sudinga goya masa baya basa son ɓacin ransa, kamar sunajin tsoronsa ma......” da sauri Joy ta rufema Miracle baki da hannu tana girgiza mata kai, sai da ta tabbatar tayi shiru kafin ta saketa, ƙofa ta nufa da sauri ta leƙa, ganin babu kowa saita maida ta rufe sannan ta dawo wajen Miracle ɗin. Daf da ita ta zauna cikin magana raɗa-raɗa tace, “Ni kaina na daɗe inason yin maganarnan da Wani Mira, kinga dai su Mom duk su suka haifemu, amma idan kika lura sunfi son Brother Yoohan, ko yaya suka gansa a damuwa sai kiga sun rikice, sannan duk abinda yakeso shi ake masa. Kiga dai yanda kike sonsa yana wulaƙantaki a gidan nan amma basu taɓa nuna masa rashin dai-dai akan hakan ba. Kowafa tsoronsa yakeji anan gidan har Mom ɗin”. Mira dake sauraren Joy kamar mai ɗaukar karatu tace, “Yayi kuɗi ne shiyyasa ai”. Kai Joy ta girgiza mata da faɗin, “Sam ba haka bane Mira, ki tuna tuntuni suke masa wannan gatan na fitar hankali, makaranta saida ya zaɓa ya darje mai mugun tsada a ƙasar waje, har sai da ya cika burinsa na zama babban likitan da yakema duniya aiki bama Najeriya kaɗaiba, amma kina gani ni da Gebrail a 9ja muka fara karatunmu, sai yanzune da shi yace zai fita damu sannanfa suka yarda”. “Hakane Joy. to ammafa kinsan Yoohan yanada bala'in ƙwaƙwalwa, dan sister Divine tace min sanda suna primary yafi kowa hazaƙa da ƙoƙari a ajinsu, yanzu za'a karanta masa yanzu zai ɗaukesa a kai. Ni yanda ya tsaya yay karatun ya birgeni, dan masu irin shegen kaifin ƙwaƙwalwar nan tasa basu da yawa a cikin mutane, zakiga kuma mafi yawansu sunfi yarda su zama mugaye fiye da mutanen kirki, balleshi daya tashi ɗan gata ma. Amma kigafa shi a ma tsarinsa baya shan komai har giya da ba komaiba, baya neman mata, abinda kawai ya sani a rayuwarsa shine aikinsa da Family ɗinsa. Gaskiya ina masifar son gayen nan Joy, komai nashi yana birgeni”.
        Dariya Joy tayi sosai, ta wani juya idanunta cike da yanga, “Ai bake kaɗaiba Mira, koni da yake Brother ɗina sonsa nakeyi, haka ƴammata da yawa suke haukacewa a kansa, shiko babu wacca ta ishesa koda kallo ma, Mom tace tunda suke da shi bai taɓa ce musu ga budurwarsa ba. Ke nifa da ƙanwa zata iya auren yayanta da Brother Yoohan zan aura fa”. Baki Mira ta taɓe cike da kishi ta ɗauke kanta batare data bama Joy amsaba.
     Joy data fahimci kishi Mira keyi saita kwashe da dariya ta miƙe, amma ita tasan har cikin ranta son Brother ɗinta take da gaske. Kuma harga ALLAH tana kishin ganinsa da wata mace har Mira ɗin, dan yau sosai taji daɗin mazgar da yayma Miracle.

🤣Joy kedai muguwace to.

______________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________
  
                 Wannan littafi SARAN ƁOYE na kuɗine, yana ɗaya daga zafafa biyar, idan kana buƙata kaima waɗanan numbers ɗin magana ka biya kuɗinsa naira 300 kacal dan girman ALLAH. Karka karanta idan baka biyaba, karka kuma yaɗa dan ALLAH idan ka gani😀🤝🏼.

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

_______________________

               A tsarin gidan dolene duk safiyar duniya ka fito babban falo inda suke taruwa su duka har ma'aikatan gidan suyi addu'oinsu. Yoohan ne dama sai ya gadama randa ta raya masa yake fitowa idan har ya kwana a gida, dan yafi ganema yayi tasa a ɗaki shi kaɗai baisan hayaniya, garama idan Papa ya takura masa.
      Yauma kamar kullum duk sun hallara, har ƙananan yaran duk an tasosu, Papa da yay tafiya ne kawai babu sai Yoohan da kowa yasan yau bazai fitoba tunda jiya da haushin Miracle ya kwanta. Amma duk da haka sai da Mom taje ta buga masa ƙofa.
      Yana jinta sarai, dan tashinsa kenan yana zaune a kan gadonsa ido a rufe yana addu'ar shima. amma yay mata banza, sai da ta gaji dan kanta ta haƙura. Sauka yay a gadon fuskar nan kamar kullum a cinkushe, amma hakan bai hana ƙyawunsa da ALLAH ya azurtasa dashi bayyana ba (damma babu hasken bautar UBANGIJI a cikinsa Yoohan daya zarce hakan ga mai kallo😭).
        Slippers ya zura ya nufi toilet, ya kusa mintuna goma a ciki sannan ya fito, da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login