Showing 126001 words to 129000 words out of 318746 words
kuwa shi hakan yake buƙata tun ɗazun. A tunaninta zasu tafi ne, amma sai taga sunyi zamansu sunata hira da Umm. Kusan mintuna talatin basu da ko niyyar tafiyar, takaici ya cika Nu'aymah, dan haka kawai yau itama sai takejin zafin Adawiya akan Abdallah. Shiyyasa hirarma bata saka baki, tana lafe jikin Umm tamkar wata mage.
Basu bar sashen ba har sai da Baba malam ya shigo gidan, dama shi suke jira. Zama kuwa yay suka gaisa a ransa yana mai jin daɗin ganin yanda Adawiya ta kwantar da hankalinta. Yanda tai ƙiba ta ƙara ƙyau kawai ya isa fahimtar da mai kallonta hankalinta a kwance yake sosai. Barci ne ya sake kwashe Nu'aymah har suka bar sashen bata saniba. Koda Umm datai tunanin anan Adawiya zata kwana amma taga saɓanin hakan sai da ta tashe Nu'aymahr ma ta rakata ɗakinta saboda barcin da tayi.
Washe gari Nu'aymah ta tashi ne duk a takure. Ba komai ya jawo hakanba sai zuwan su Yah Ab da zaman Naser a gidan. Maƙalewa tayi a sashensu taƙi fita har rana. Sai da Umm ma ta takura mata ɗaukar abincin Hajjo ta kai mata sannan ta fita badan taso ba.
Tunda taga takalma birjik a ƙofar Hajjo taji kamar ta juya. Amma gudun kar Umm tai mata faɗa sai ta daure tayi sallama. Sai da aka bata izinin shiga sannan ta shiga da wata sallamar a bakinta. Duk samarin gidanne a she. Sai Rufaida da Hajjo. Nu'aymah ba wani shiri sukeyi da Rufaidah ba itama, dan ta girmesu, gata kuma da shegen son girman tsiya, shiyyasa take ganin sai dai su bita. Ita kuma Nu'aymah tsiwa.
A tare kawai tace dasu “Ina yinin ku”. batabi takan dawa-dawa ya amsa ba ta nufi Hajjo daketa binta da kallon jin daɗin ganin jikinta ya sake warwarewa.
“Hajjo barka da gida. Ga abinci inji Umm na”.
“To takwara sannu kinji, yaya jikin naki?”.
“Naji sauƙi Hajjo”.
“Alhmdllh ai haka akeso dama. Tun ɗazun nake tsumayen ganinki amma shiru. Tashi ki duba a firiji na ajiye miki fura”.
Sosai daɗi ya kanata. Cike da ɗoki ta nufi fridge ɗin hajjo ta ɗakko kofin furar tana sakema hajjo godiya. Har zata fice Naser ya kirata. Badan tasoba ta amsa tare da juyowa tana kallonsa. Ya sakar mata sassanyan murmushi tare da miƙewa ya nufo inda take tsaye. Bayare da yay magana ba yay gaba da mata alamar ta biyoshi.
Bataso hakanba, amma sai ta bisa kawai gudun kar yaga kamar ta masa wulaƙanci. Ɗaya daga rumfar bunun da aka jera guda uku a harabar gidan ya nufa. Nu'aymah ma dai na biye da shi. Kujera ya ja mata baya yace ta zauna. Nanma bata musaba tayi yanda yake buƙata. Sai da ta zauna sannan shima yaja wata ya zauna.
Yana zama Abdallah na isowa wajen kamar daga sama. Daga ita har Naser kallonsa sukai. Yayi kicin-kicin da fuska tamkar zai fasa ihu. Batare da yace dasu uffanba yaja kujerar ɗanyan gefen Nu'aymahn ya zauna suka sakata a tsakkiya.
‘Ikon ALLAH ’. Nu'aymah ta faɗa a cikin ranta tana kallonsu da mamaki.
“Alhaji lafiya kuwa?”. Naser ya faɗa a lalace yana kallon Abdallah. Murtani Yah Ab ya maida masa cike da dizgi. “Itace ta kawo haka”.
“Humm!” Naser ya faɗa yana ɗauke kansa daga garesa ya maida ga Nu'aymah da mamaki ke cigaba da nuƙurƙusarta a zuciya.
“Kayi haƙuri ka bamu waje magana nakeson yi da ita Abdallah”.
“Wannan isar ce kuma baka yiba. Duk abinda zaka faɗa mata inhar kasan ba mara ƙyau bane ka faɗa a gabana mana”.
“Mtsoww! Ai kasan baka isa sakani yin abinda banyi niyya ba. Nu'aymah tashi muje can...”
Batayi niyyar binsaba a yanzu. Tayi niyyar kawai tabar musu wajen. Sai dai tana yunƙurawa zata miƙe Abdallah ya daka mata tsawa. “Koma ki zauna kona mareki!!”. Ya faɗa yana ɗaga hannun tamkar zai maketa.
Ɓata fuska sosai tayi tamkar zata fasa kuka. Dan ita kam sun sakata a tsaka mai wuya.
A fusace Naser yace, “Abdallah karka bari nakai bango da kai, wai shin ina ruwanka dani ne? Naga dai Nu'aymahr nan ba matarka bace balle kace zakama mutane iko. Idan ada kayi ikon saboda akwai alƙawarin aure a tsakaninku yanzu saika tuna babu wannan. Ita ɗin allura ce cikin ruwa mai rabo ka ɗauka........”
“Nine mai rabon kuma insha ALLAHU!!, dan haka ka kama kanka karka bari a jimu da kai Naseer”.
“Hhhhhh! Abin dariya. Sannu Abdallah ubana mai bani umarni. ai ka sani kayi sake tun a farkon dama, a yanzu kuma ta suɓuce maka har avada. A da canma dan ba'a bata dama bane akaso mata auren dole da kai, amma sai UBANGIJI yay dubeta ya hana hakan.....”
“Naser!!!”
Abdallah ya kirashi cikin ƙaraji da fusata tare da dunƙule hannu tamkar zai kai masa naushi. Ƴar zabura baya Naser yayi kamar irin yaji tsoro ɗin nan. Sai kuma ya kwashe da dariya ya kuma ɗaure fuska duk a lokaci ɗaya. “Oh to ko dukan nawa zakayi ne?!”.
Bai gama rufe baki ba kuwa Abdallah ya kai masa naushi. Da sauri Naser ya duƙe naushin yabi iska. Ya sake kai masa wani Baba malam da ke bayansu shi dasu Abbah ya daka musu tsawa.
“Kai!! wane irin shashanci ne haka kukema mutane a cikin gida da hankalinku?. Ko kunya bakujiba kuka zauna faɗa a gaban ƙaramar ƙanwarku, wannan ai rashin hankaline da sakarci”.
Duk ƙasa sukai da kawunansu kowa na huci. Abban su Adawiya yace, “Ku wuce muje ciki. Kema Nu'aymah shige”.
Sum-sum ta wuce tana danne dariyar dake cinta a rai tun fara rigimar yayun nata. Tana shiga falonsu kuwa ta fashe da dariya. Da sauri Umm da Rabi dake a kitchen suna aiki duk suka leƙo.
“K lafiyarki kuwa kike wannan dariyar ta rashin hankali?”.
Hannu Nu'aymah tasa da sauri ta danne bakinta, da ƙyar ta haɗiye dariyar tata sannan ta kalle su. “Wlhy Umm su Yah Ab ne suka bani dariya”.
Batare da Umm ta tsaya jin ba'asi ba tai tsaki ta koma kitchen. Rabi kam sai ta nufota tana tambayarta wai miya faru?. Da sauri Nu'aymah ta haɗe fuska tare da zuba mata harara tabar wajen. Itama Rabin da harara ta raka Nu'aymahn, a ranta kuwa faɗi take, ‘Zaki gane shayi ruwa ne yarinya, shegiya mai kama da ƴaƴan aljanu’.
Oho Nu'aymah batasan tanai ba. Dan tuni ta shige ɗakinta. Sai dai itama a ranta tana matuƙar mamakin munafunci irin na Rabi. amma sam Umm ta kasa fahimtar akwai wani abu a zuciyar Rabi, dan ita ta jima da fahimtar hakan, harma a ranta tana zargi Rabin da ɗaukar sirrin Umm tana fitarwa. Dan akwai ranar data taɓa ganinta bayan ɗakinsu tare da wanda bata fahimci namiji ne ko mace ba suna magana. Sai dai kafin ta zagaya taga wanene ta iske sunbar wajen Rabin ma harta shigo ciki. Tun daga lokacin ta saka mata kahon zuƙa. Taso fahimtar da Umm amma saita hauta da faɗa akan batason wannan halin banzar, dan Rabi a haife ta haifi Nu'aymah harma wanda ya fita. Kuma tun Nu'aymah na ƙarama suke tare ita bata taɓa ganin wani abu mara ƙyau daga gareta ba.
Tsaki tayi kawai da kauda zancen Rabi a ranta ta koma tuno su Abdallah. Haka kawai takejin al'amarin nasu na sakata nishaɗi. Ba sai an faɗa ba kowa yasan tana tsananin son Abdallah, ƙaddara ce kawai ta shiga tsakanin al'amarinsu. Amma a yau sai kawai yanda Naser yay sai shima ya birgeta. Har takeji zata iya aurensa duk da zuciyarta bawai tana sonsa bane ba. Amma tunda ta haƙura da Yah Ab zata iya maye gurbinsa da Naser ɗin. Sai dai fa tasan lallai akwai ƙura a cikin faruwar hakan kuma.
★★★
A ɓangaren su Abdallah kuwa faɗa sosai su Baba malam sukai musu akan abinda suka aikata. Dan a gabansu mafi yawan rigimar ta faru shiyyasa basu bi takan jin yanda akai ba. Sai da baba malam ya tabbatar jikinsu yayi sanyi sannan ya ɗora musu da nasiha kuma, ya kuma sakasu bama juna haƙuri sannan suka sallamesu.
Suna fitowa kowanne ya wurgama ɗan uwansa harara da jan tsaki.............✍
Kuyi manage Please, inada baƙi😒🚶🏻.
_____________________________
ZAFAFA BIYAR 2021
_______________________
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[5/22, 10:26 PM] +234 809 502 2953: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 34
............Abu kamar wasa sai ga ƙaramar magana na neman zama babba. Dan kuwa dai rikici sosai ke wakana a tsakanin Abdallah da Naser akan Nu'aymah. Amma sai suka canja taku yanda iyayensu bazasu fahimta ba. A duk sanda Naseer yasa aka kira masa Nu'aymah sai Abdallah yazo ya tsare. Hakama duk lokacin da Abdallah ya buƙaci ganawa da Nu'aymah sai Naser yazo ya hana hakan ta hanyar zama tsakaninsu kamar yanda Abdallahn keyi.
Hajjo da mafi yawan rigimar a sashenta akeyi tana kallonsu amma tai kunnen uwar shegu da su kamar bata ganiba. Wani lokacinma da biyu take sakawa a nemo mata Nu'aymah ta zauna a sashenta dan tasan nanne wajen zaman su Naser ɗin musamman da daddare.
Duk kuma wannan abun dake faruwa Adawiya bata nan, dan kwanansu biyu da zuwa sukai tafiya biki ita dasu Hajarah dangin kakarsu maman su Addah. Da Addah ta ƙarrafa ayi tafiyar da Nu'aymah ma. Sai dai yanayin jikinta yasa Hajjo hanawa. Shiyyasa suka tafi su uku harda Kubrah sai Addahn da sauran ƴaƴanta na ma'auri.
Da farko rikicin nasu Naser nishaɗi yake saka Nu'aymah, amma ganin al'amarin na sake ɗaukar zafi sai hankalinta ya fara tashi. Dan neman birkita mata tunani sukeyi har takan rasa wanene yafi cancanta ta mallakama kan nata?.
Al'amarin bai sake tada hankalin kowaba a gidan sai randa Hajjo take cema Abdallah dama ya haƙura ya barma Naser Nu'aymah. Tunda shi a yanzu gashi yana auren su Yusrah. A fusace yace, “Indai su Yusrah ne zasu masa katanga da mallakar Nu'aymah to lallai zai rusa katangar”.
Babu wanda ya ɗauki furucin nasa da muhimmanci a lokacin da yayisa. Sai dai ga mamakinsu bayan sallar isha'i sai gashi da zungureriyar takarda har guda biyu yazo ya dire gaban hajjo.
Kallonsa tayi fuska a yatsine. “Kai wannan takardun kuma na miye ka ajiyemin kamar wani ɗan saƙon kotu?”. Fuska a turɓune yace, “Hajjo sakamakon katangar da kika tabbatar min zata shiga tsakanina da Nu'aymah ne a ciki. Kinga yanzu sai ki daina min baki ko”.
Sam hajjo bata fahimci zancen nasa ba, amma sai ta saka Omar dake zaune tare da ita ya duba mata. Ɗaukar ɗaya yay yana murmushin diramar kakar tasu da yayansu. Da sauri ya fesar da ruwan da ya ke sha yana faɗin, “What!?” saboda abinda yaci karo da shi a rubuce.
A rikice hajjo tace, “Miya faru Umaru?”. Jikin Omar na ɓari ya ajiye kofin ruwan tare da ɗaukar ɗayarma ya buɗe. Nanma dai abinda ke cikin ta farkon ce a ta biyu, ai baima san lokacin daya furta, “Hajjo wlhy Yah Abdallah ya haukace! ko kuma ya fara shaye-shaye ku bincika!. Hajjo sakin Yusrah da Adawiya fa ya yi.....”
“Saki kuma?!!” Hajjo ta faɗa itama tana miƙewa zumbur.
“Wlhy kuwa Hajjo gashi a rubuce saki ɗai-ɗai”.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un. Abdullahi!!. A wlhy gaskiyarka kuwa Umaru Abdullahi ya haukace. Ni Zainabu na shiga uku. Kaga kiramin ɗan malam duk inda yake yazo gida”.
Ɗan jimm Omar yayi alamar tunani, sai kuma ya dubi Hajjo da ranta ke a matuƙar ɓace. Cikin lallashi yace, “Amma Hajjo inaga kamar dai kiyi haƙuri har ya dawo gida. Kinga yanzu bamusan wane uziri yake kan yiba, kiran da za'ai masa zai iya dagula masa tunani, amma idan kince a kirasan dai sai na kirasa ɗin”.
“Hakane Umaru! Kaima kayi maganar hankali, amma lallai sai na saɓama Abdullahi fiye da zato a gidan nan. Wane irin wawancine wannan? Ashe hankalin da ake ganinsa da shi da girma bashi da shi ɗin?”.
“Kiyi haƙuri Hajjo, ALLAH ya huci zuciyarki. Ni kaina ban taɓa zaton hakan daga garesa ba. Kinga wannan ai tushen ɓata zuminci ne, idan iyayen namu basu kai zuciya nesa ba sai kiga al'amarin ya kawo ɓacin rai. Sannan su kansu yaran an saka wani abu a zuciyarsu gurɓataccen. Dan zasu iya tsanar Nu'aymahr da yace dominta yayi, hakan kuma bashi da amfani”.
Ƙwafa kawai hajjo tayi ranta da zuciyarta na ƙara mata suya da ɗaci. Omar dai yayta lallashinta har sai da yaga ta ɗan kwantar da hankalinta sannan ya fice cike da jimami. Sashensu ya nufa, yaje ya faɗama Momy duk abinda ya faru.
Sosai itama ta rikice hankalinta ya tashi. Dan ta tabbata Abbansu dama wasu a mutanen gidan bazata fita da ga zarginsu ba, musamman ma da akasan taso ya auri ɗiyar ƙanwarta. Waya ta ɗauka ta shiga neman Abdallah. Sai dai harta tsinke bai ɗagaba. Bata gajiya ba wajen cigaba da jera masa kira, amma yaƙi ya ɗaga.
Hajjo, Omar, Momy sun yi yinin yau ne cikin tashin hankali da damuwar ɓarnar da Abdallah ya tafka. Duk da sun ƙagara Baba malam ya dawo gidan ransu cike yake da fargabar sakamakon da zai biyo baya kuma.
Sai bayan sallar la'asar baba malam da Abban Abdallah suka dawo gidan. Dan dama tare suka fita. Sunje wani ƙauyene akan maganar wata katafariyar gona da zasu saya. Sunason gyarata su maidata gidan gona a zuba dabbobi kala-kala na kiwo a ciki. Wannan ma ne dalilin da yasa har yanzu shi da Abba Musbahu basu koma ba. Suna son sai komai ya kammala sannan su ɗauka iyalansu su koma inda suka fito sai kuma biki.
Kamar yanda al'adarsu take ta fara shiga sashen mahaifiyarsu yau ma hakan suna fitowa daga mota can suka nufa. Yanda suke tafe suna firarsu kowanne fuska ɗauke da fara'a dolene su matuƙar burgeka. Dan a kallo ɗaya zaka fahimci ɗunbin shaƙuwa da ƙaunar juna dake a tsakaninsu.
Sai da sukai sallama Hajjo da ke zaune cikin ɓacin rai har yanzu ta amsa musu da basu izinin sannan suka shiga. Kallo ɗaya sukai mata suka fahimci tana cikin damuwa. Kusan da sassarfa duk suka ƙarasa gareta kowanne na tambayarta tana lafiya?.
Batai magana ba, sai wajen zama data nuna musu. Sai dai maimakon su zauna a kujerun sai suka zauna ƙasa tamkar yanda suka saba. Gaisheta sukayi, sannan suka sake jero mata tambayoyi akan yanayin nata.
Ƙwallar da suka cika mata idanu tasa bakin ɗan kwalinta ta share. Hakan sai ya sake tada musu hankali.
“Inna dan ALLAH ki faɗa mana minene ke damunki? Mune mukai muki laifi? Ko matan mu? Kokuwa a cikin yaran nan ne wani yay miki wani abu?”.
Sake share hawayen data matso tayi da cewar, “Ni babu abinda kukai min ɗan malam, Abdullahi ne kawai keson watsa mana gida”.
Hankali a tashe baba malam da Abban su Abdallah suka kalli juna. Cikin ƙarfin hali baba malam yace, “Innah mi Abdallahn ya aikata?”.
Takardun da Abdallah ya rubuta ta ɗakko ta miƙa musu. Amsa sukayi kowanne ya buɗe guda ɗaya gabansa na faɗuwa. A tare suka ɗago a razane suka kalli juna da ambaton sunan ALLAH. Baba malam har yana tsallaken kalma wajen faɗin, “Innah shi Abdallah ɗinne ya rubuta wannan takardar?”.
“Shine ɗan malam, shine da kansa ya rubutasu ya kuma kawo mani. Wai dan kawai jiya na bashi shawarar cewar yay haƙuri ya barma Nasiru Zainabu tunda shi yanzu yana da matansa har biyu. Shine fa yau ya kawomin takardar sakinsu Adawiya wai gashinan ya rushe katangar dana ce masa tana tsakaninsa da Zainabu”.
Abba da ya gaza cewa komai tun ɗazun yace, “Innalillahi..., wai inna kina nufin su duka biyun ya saka?”.
“Eh mana Lurwanu, baga takardun nan ba duka biyu na baku”.
Da sauri baba malam ya amshi ta hannun Abba, shima ya karɓa ta hannunsa. Da gaske kuwa su duka biyun ya saki. A take tsananin ɓacin rai ya sake bayyana a kan fuskokinsu. Abba ya miƙe a fusace zai fice. Kiransa baba malam ya shigayi amma ina zuciyar gadon ta motsa. Dan haƙuri kawai ya bashi batare da ya juyoba ya fice.
Momy na zaune cikin damuwa da fargabar jiran dawowar mijinta Abba ya shiga. Jiki a sanyaye ta dubesa dan ko sallama baiyi ba
Takardun guda biyu ya watsa mata a jiki. “Da saninki ɗanki yay wannan aika-aikar ko?”.
Gaban Momy na faɗuwa ta ɗauki takardun ta karanta, hawayen da taketa faman dannewa tun ɗazun suka zubo mata a saman kumatu. “Wlhy Abban Abdallah ban sani ba. Nima ina zaune Omar yazo yake sanarmin. na kirashi yafi sau hamsin amma ya ƙi ɗagamin waya ma, kai........”
Baki ya buɗe zai daka mata tsawa Omar da ya shigo basu sani ba yace, “Abba wlhy babu ruwan Momy, hasalima batasan komaiba