Showing 294001 words to 297000 words out of 318746 words

Chapter 99 - saran boye complete by Queen meenali

01 Jul 2024

41606

mutu. Kasancewar sun kira sun sanar sai ogansu ya basu umarnin maza su ɗakkosa su dawo cikin kano asibiti. Bisa wannan umarnin ya sakasu ɗakkosa suka juyo a guje.
    Kai tsaye babban asibiti suka nufa, cikin amincin ALLAH kuma akai sa'a can aka kai Addah da su Umm suma. Su baba Malam na tsaka da tashin hankalin abinda ya faru sabon labari akan haɗarin Abban Abdallah yazo musu. A take na gida dana asibitin suka sake harmutsewa.
     A yanda Yoohan yaga al'amarin ya kasance sai da yaji nadamar shigewa gaba wajen wannan bankaɗe-bankaɗe. Sai gashi da idanunsa ya ga baba malam na rusar kuka. Nu'aymah kam ai sai allurar barci ya danna mata saboda yanda ta birkice kamar dai ƙwaƙwalwar ta bata gama dawowa dai-dai ba.
      Lallai wannan ranace da waɗaɗan nan ahali bazasu taɓa mantawa da itaba a jerin tarihinsu. Sauƙinsu ma har yanzu ainahin labarin bai fita kunnuwan jama'ar gariba. Sai dai kawai ana maganar Sheikh Rudwan Hashim jibiya yayi Accident a hanyarsa ta zuwa Ktn yanzu babu jimawa. A take mutane suka shiga jera masa addu'ar ALLAH ya tashi kafaɗa, musamman ma mabiyansa.
      Zan iya ce muku yanda wannan ahali sukaga yinin wannan rana haka sukaga dare. Duk da kuwa Alhmdllh zuwa dare an tabbatar da Abban Abdallah bai rasuba. Ya dai samu karaya a kafaɗunsa duka biyu da kafafu. Sai manyan raunika da sukai masa kaca-kaca da jiki. Itako Addah barci suka sakata yi. Umm ma Alhmdllh ta farfaɗo ita da malam ƙarami. Hakama Nu'aymah ta farka.
         Sai kusan tara na dare suka bar asibitin, ba kuma a barsu sunga Abban Abdallah ba dai. Yoohan da kansa ya fiddo Nu'aymah da ga ɗakin office ɗinsa daya sakata barci. Ananah ta taimaka mata suka ƙarasa shiga mota. Baba malam yaso su Yoohan su bisu can gidan su kwana amma suka bashi haƙuri akan zasu zauna anan asibitin ne. Badan yaso ba ya barsu.

       Yoohan na ganin motocinsu sun gama wucewa ya sauke ajiyar zuciya mai kauri, A ɗaya daga kujerun dake a waje ya zauna hannayensa duka dafe da kansa. Sai yanzu komai ke dawo masa a ƙwaƙwalwa tamkar almara. Dan ɗazun su Addah na bayani ne little na fassara musu shi da Umar, duk da shi yana ɗan jin hausarma kaɗan-kaɗan yanzun.
      Kusa da shi Umar yazo ya zauna shima yana sauke nasa ajiyar zuciyar. Yoohan bai motsaba balle ya kallesa. Shima sai bai damuba ya fara magana a hankali. “Haka mafi yawancin mutanen da suka samu ɗaukaka suke. Sai kaga na nesa da su na matuƙar sonsu da begen kasancewa da su. Amma waɗanda ke tare da su mafi yawancinsu ba son gaskiya suke musu ba. Ƙaso ɗaya bisa uku a ciki zaka samu suna musu ƙauna ta tsakani da ALLAH. Kaso biyun kuwa sai kaga suna raɓe da sune bisa wannan ɗaukakar da ALLAH yay musu. A zahiri kuwa su zugasu da nunama duniya babu kamarsu, a baɗini sune masu musu SARAN ƁOYE. lallai waɗanan mutanen masu zagon ƙasa suna ɗaya daga cikin jarabawar masu mafi yawan ɗaukaka”.
      Ajiyar zuciya Yoohan ya sake saukewa. Ya ɗago ya dubi Umar a karon farko, idanunsa sunyi jajur. Ga barci ga yunwa ga gajiya. Shi kansa Umar ɗin a galabaice ya ke. “Zancenka haka yake Umar, bazan ɓoye makaba al'amarin mutanen nan ya sake saka tsoro a zuciyata gaba ɗaya, nasake jin tsoron halin mutum da ayyukansa. Wannan wane irin bushewar zuciya ne haka? Su da ya kamata su zauna suyita godema ALLAH bisa ni'imar da yay musu ta rayuwa, su dinga ibada sai suka zama masu butulcewa ta hanyar cutar da wanda shi ya kusan ƙare tasa rayuwarne a ƙyautata tasu da ta ƴaƴansu. Umar wai miyasa ɗan adam keda manta alkairi da yawan butulci ne?. Miyasa ɗan adam yafi yarda da biyayya wa huɗubar shaiɗan akan dokar ALLAH ne?. Miyasa ɗan adam yafi yarda ya zama mai samu bamai sadaukarwa ba?  Miyasa mafi yawan mutane sunfi sha'awar cutar da wanda suka ƙyautata musu amma sunajin tsoron mai munanasu?. Ko addu'a mutum zaiyi, sai kaji yace ALLAH ka tsareni daga sharrin masu sharri. To miyasa bama addu'ar ALLAH ya karemu da aikata sharri ga masu ƙyautata mana ne?”.
       “Wannan shine halin ɗan adam ɗin da ake faɗa Dude, munada son kanmu, duk kuma mutum mai son kasa zakaga shine kullum a cikin wahalar nema da faɗuwa. Dan bazai taɓa doguwar nasara ba. Daya samu take kufece masa. Amma saboda bushewar zuciya gobe ma sai ya koma sake neman sa'a. Kowane addini akwai na banza akwai na gari. Irin waɗan nan mutanen suke ja ana zagin addinin islama bayan shi kuma addinine mai koyar da ƙyawawan ɗabi'u. Ko shekara banyi da shiga musilinci ba, amma wlhy Yoohan na fahimci babu wani addini dake gogayya da shi akan koyar da ƙyaƙyƙyawar rayuwa. Komai musilinci ya haɗa. Amma ka duba su da keda ilimin sani a tsahon shekaru sunfi zaɓar su saɓama ALLAH bisa son zukatansu”.
     Sosai zukatansu Yoohan suka ƙara rauni da wannan al'amari. Imani da tsoron ALLAH ya sake shigarsu a zuciya da ɓargo. Suma kansu dai a wannan dare sunyi barci ne kawai badan jin daɗi ba.

*_WASHE GARI_*

        Washe gari aka bama su baba malam damar shiga su duba Abban Abdallah. A lallai duniya abin tsoro. Bawa daina cikama rayuwa baki kai ba komai bane. Duk damar da kaga ka samu a rayuwa da ga rahamar ALLAH ne. Amma wlhy idan yaso ko ƙyaftawar ido baka isa gittawa ba. A jiya iyanzu shine zaune tare da ƴan uwa da iyalansa. Amma yau gashi babu ko ƙyan gani a fuska saboda tsabar jigata da rayuwarsa tayi. Ita kanta Addah jikin nata babu daɗi.
    Duk wanda ya shiga duba Abban Abdallah sai kaga ya fito da kuka. Hakan yasa dama Yoohan bai bar Nu'aymah a wajenba. Suna zuwa ma ya jata wai tazo suje wajen awo. Bata fahimci wayo yake mataba ta bishi. Sai ya kaita office yasa aka kawo mata abinci. Duk da tace masa ta ƙoshi, dan basu fitoba sai da Umm ta bata abinci ya dage sai taci. Dole taci kaɗan dan ya barta. Sauran kuma ta bashi dan ta fahimci shima yana buƙatar a tsaresa yaci abincin.
        
     Zuwa ranar dai dukan ahalin gidan sunsan halin da ake ciki, ƴaƴan Addah dake aure da ƙannen Abdallah ma duk sunzo. Ansha sabon kuka dai kam yau ma. Daga ƙarshe baba malam dake ta ƙoƙarin danne tasa damuwar yay musu nasiha da nuna musu muhimmancin ƙaddara. Ya tabbatar musu da cewar hakan jarabawane. Dan bazai yuwu dama a rayuwa a rayuwa babu jarabawa ba. Ya hana kowa kakkausan lafazi akan su Addah, dan kuwa shi a take ranar ya tabbatarma da kowa cewar ya yafe musu. Sai su cigaba da musu addu'ar ALLAH ya basu lafiya kawai.
     Baba malam ya ƙara kima a idanun iyalan Addah da Abban Abdallah. Musamman ma Abdallah da har ran yakejin tsanar mahaifinsa da Addah. Sunso su gurɓata masa tunani ALLAH ya hana hakan. Dan bayan Addah ta ɓale a cikinsu Abbansa sake zaunar da shi yay ya ɗora masa sabon karatu akan maido da Nu'aymah rayuwarsa koda ta ƙarfin tuwo ne. Wannan shine dalilin da yasa dinga bibiyar rayuwarta. Ko a randa ya bisu shopping mail ɗin nan da nufin kidnapping Nu'aymah ya je. Sai akai rashin sa'a Yoohan ya gansa tun lokacin da suke faɗansu da Aymah harta faɗa a jikinsa. Dai-dai lokacin da yake cemata ta tara musu mutane idonsa ya sauka akan Abdallah ɗin. Har suka shiga mail ɗin kuma yana sane da shi. Sannan yana akan sani yabar Aymah a wajen ita kaɗai dan yaga mi Abdallah zaiyi?.
     Lokacin da Nu'aymah taji ƙamshinsa da gittawar mutum Abdallah ne, yana gab da isa gareta Yoohan ya jasa baya da ƙarfi ya toshe masa baki suka koma ta bayansu. Cikin fushi Abdallah ya hakaɗe Yoohan ɗin yana faɗin. “Kai shasha minene haka?”.
     Murmushi Yoohan yayi sannan ya haɗe fuska. Cikin ƙanƙance ido ya nuna Abdallah da faɗin, “Idan ka bari gangancinka ya ɗora zuciyarka bisa dokin shiga gona ta. Na rantse da ALLAH Abdallah sai na dawwamar da rayuwarka a dana sani. Na fika hatsabibanci fiye da yanda kake tsammani. Dan haka ka kama kanka kafin na ajiye mutuncin ahalinka da nake gani gefe na ɓata rayuwarka. Karka zata bansan wanene kai ba da ubanka. Ka kiyayeni kona fallasaku duniya ta sanku da aiyyukanku akan ahalinku”.
     Yana gama faɗa yabar wajen, shine yaje yaja Aymah suka wuce wajan biyan kuɗi.
      Tabbas kalaman Yoohan sun girgiza Abdallah. Hakan yasa ya janye daga bibiyar Nu'aymah. Dan dama can shi mutum ne da a rayuwa bai son yawan matsawa kansa, sannan baison fitina sam. Wannan halayyar tasa tasa lokacin yana yaro ake ganinsa matsoraci a cikin yara ƴan uwansa. Dan da gaske tabbas yanada tsoron faɗa a rayuwarsa. Dai-dai da film ɗin faɗa Abdallah baya zaman kallonsa sam saboda baya ra'ayin fitina, daya zama saurayune ma dai ya fara canjawa. har zuciyar tasa tai tauri saboda zuciyar gidansu ta gado.
      Ƙin faɗama Abbansa zancen yayi. Amma yayi ƙudirin janye jikinsa daga bibiyar Nu'aymah. Daga bakin Abbansa yaji samuwar Uwaliya, dan a randa aka kawota a ranar Abbansa ya tattauna da ita tun a office kafinma a kaita gidansa. Uwaliya akwai son kuɗi. jin maƙudan ƙuɗin da Abban Abdallah ya tabbatar mata zata samu akan kaso masa auren Nu'aymah da kawo musu dukkan bayanai a kanta yasa ta amince zatayi. A ranar ya bata rabin kuɗin, sauran kuwa sai aiki ya kammala.
      Tasha murna a ranar, ta kuma tabbatar da lallai ta shigo Abuja da ƙafar dama. Yo ko Yoohan ɗin sukace ta bibiya akan waɗanan kudin ai ta halakashi kuwa.
       Wannan shine dalilin da yasa ta fara musu aiki. Sai dai abinda bata saniba suna amfani da wayar Rabi da muryartane idan suka kirata.
     Lokacin da aka wuce da Nu'aymah Austria da gaske Abdallah yaje dubatane saboda son da yake mata. Sai dai baiso Yoohan da su baba malam su gansa. Shine yaso su fara haɗuwa da Abbansa. koda suka haɗun Abban ya dinga masa faɗan da har zancen Nu'aymah ya shigo ciki saboda Addah da tazo taga Abdallah ta zata cutar da Aymah zasuyi. Anna ne Yoohan yaji da Hajjo sukaji, abinda kuma basu saniba shine baba malam ma ya gansu, ya kuma jisu. amma sai bai taɓa nunawa ko da Umm ba balle su..........✍  
[7/6, 9:39 AM] +234 913 412 2711: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.


No. 75

.............Su Jay dai sun wuce abuja, amma  duk da su Addah na a asibiti suna a ƙarƙashin kulawar hukuma ne. Bayan wucewar su Jay shi ma Omar da Yoohan suka wuce da yamma. Ya bar Nu'aymah anan kano saboda Umm bata da lafiya. Har yanzu ta kasa fida daga ruɗanin data shiga. Ga jininta yaƙi sauka yanda ya kamata. Ita kanta hajjo jininta ya hau sosai. Sai dai ita Alhmdllh bai kai na Umm da komai yazo mata a yanda bata zata ba. Bama Umm kaɗai ba hatta da ƴan uwan Umm dana Addar wannan al'amari yay masifar rikita tunaninsu da basu tsoro. Anatama Addah ALLAH wadarai da wannan hali nata. Su Hajarah kam sunyi kuka har sun rasa hawayen zubarwa. Musamman Kubrah da dama ba daɗin zaman gidan mijin take jiba. Fitinar yau daban ta gobe daban.
      Yanda gidan dai yay wani iri daga shigowa zaga fahimci akwai matsala. Baba malam salla kawai ke fiddashi. Da an idar yake dawowa gida. Komansa ya tsaya cak. Dan duk da daurewar da yakeyi a bala'in gigice ya ke da al'amarin. Bai taɓa ƙawowa a ransa cikin ƴan uwansa za'a samu mai wannan tunaninba akan dukiya dauɗar duniya. Yayi kuka bana wasaba a ɓoye, har ji yake gaba ɗaya ƙasar ta fita masa a arai.

___________★★

        Su Yoohan na isa Abuja suka iske sabon tashin hankali. Dan sun iske gidansu zagaye da jami'an tsaro. Da ƙyar ma aka barsu suka shiga saboda sanin Yoohan ɗansa ne. Cikin tashin hankali Yoohan ya ƙarasa falon inda ya tarar da ƙannensa duka da mama debora a hagitse. Suna ganinsa kuwa duk suka taso kansa a guje suna rusar kuka. Su duka rungumeshi sukayi har mama debora da Gebrail dake gudunsa a da.
     Kallonsu kawai Yoohan keyi cike da tsoro, maganama ya kasa yi. Sai da Umar yay dauriyar cewa, “Granny wai mike faruwa hakane? Ku sanar mana Please. Gida zagaye da ƴan sanda. Gaku kuma cikin tashin hankali. Ina su papa suke ne?”.
        Cikin matsanancin kuka joy tace, “Sun gudu Brother Richard”.
       “Sun gudu kamarya? Ban ganeba nikam Joy?”.
      Sakin Yoohan duk sukayi, mama debora ta kama hannunsa ta zaunar a kusa da ita. Shima Umar ɗin ya zauna. Sauran yaranma duk zama sukayi bisa umarnin mama debora. Tana sharar hawaye ta fara musu bayani.
         “John munata kiran wayarka tun jiya ai amma mun kasa samunka. daren shekaran jiya kusan ƙarfe goma na dare wani mutum ya shigo gidan nan a kiɗime jikinsa jina-jina saboda harbi da akai masa. Lokacin duk munyi barci, kururuwarsa ta sakamu tashi batare da mun shirya ba duk muka fita compound. Tun a yanda mahaifinku ya ambaci sunansa a kiɗime na fahimci ya sanshi. Dan gaba ɗaya ya ruɗe shi da Chioma da guards ɗinsu. Shine ya sakamu komawa ciki akan dole batare da munji mike tafe da wannan mutumi dake a cikin jini ba. Muna falo tsaitsaye mun kasa komawa ciki mu kwanta sai ga shi sun shigo. Duk ɗakunansu suka shiga batare da sunce mana komaiba. Sai kuma suka sake fitowa a rikice. Mahaifinku ya rungumeni yana faɗin, karna damu na masu addu'a kawai, ga ATM card ɗinsa nan duk abinda muke buƙata Gebrail zai dinga ciro mana kuɗi. Daga haka suka fice zuwa garden. Ban taɓa sanin akwai wata hanyar fita gidannan ta garden ba sai a ranar. Dan sai bayan wucewarsu da kusan mintuna talatin ƴan sanda suka shigo anguwarnan sunata harbe-harbe. wasu suka shigo nan gidan suna nemansu harda guards ɗinkun nan. Sai lokacin mukasan guduwa sukayi harsu Solomon. Amma an kama guards uku a cikinsu. Su kuma ba'asan inda sukeba har yanzun”.
       Wata irin masifaffiyar zufa ce ke ketoma Yoohan ta ko ina, innalillahi wa'inna ilaihirraji'un yaketa faman maimaitawa. Shi kansa Umar zancen yay masifar rikita tunaninsa. Batare da Yoohan yace komaiba ya kama hannun Umar suka haye sama. Duk binsu sukai da kallon mamakin mizaiyi?. Bai saki hannun Umar ba sai da suka shiga sashensa can cikin ɗakin motsa jikinsa. Inda tanan yana iya hango duka ƴan sandan dake a compound ɗin gidan da anguwar ma.
          Cikin matsanancin fushi ya yarfar da hannun Umar sannan ya tsatstsare sa da jajayen idanunsa. Muryarsa da tsananin kaushi da fushi yace, “Umar mi kuke ɓoye min kai da Matata akan iyayena?. kar kaimin ƙarya, dan ba ita nake buƙataba a yanzu na roƙe ka”.
      Yanda ya ƙare maganar muryarsa na rawa kamar zaiyi kuka da haɗe hannayensa waje guda kuma sai zuciyar Umar ta ƙara raunana. Hannayen ya riƙe duka a cikin nasa ya sauke. “Yoohan anzo gaɓar da basai ka roƙeniba zan sanar maka. Sai dai inason ka fahimceni Please. Nima bani da wani zaɓin daya wuce hakan”.
     Komai Yoohan bai ceba, saima cire rigarsa da yayi ya hau wani machine ɗin motsa jiki ya fara da sauri-sauri. Huci Omar ya sauke tare da fara bama Yoohan labari. Tun daga abinda ya fara ji akan kashe Nu'aymah da papa ya bama Dr Mateo kwangila har zuwa ɓoyayyun harƙalloli daya fahimci papa nayi a ɓoye. Kamar safarar miyagun ƙwayoyi da cocaine. Safarar makamai, satar yara yana tarasu a wani gida acan ƙauyensu........
       Ihunsu Mama debora daya cika gidanne ya saka Yoohan dan Umar fita da gudu zuwa ƙasa.
     Cike da firgici da tsoro Yoohan da Umar ke kallon Little bee da tawagar jami'an hukumarsu. Ta haɗe fuska matuƙa, babuma alamar tasansu. A fusace Yoohan yace, “Lafiya kuwa?”.
      Uffan Little bee batace masa ba. Sai ma i'd card ɗinta kawai ta nuna masa. Sannan ta ɗora da faɗin, “Muna buƙatar shiga ɗakin Mr Goshpower domin yin bincike”.
     Magana Yoohan zai sakeyi Umar ya girgiza masa kai alamar karya ce komai. Hannayensa duka biyu ya tura cikin aljihun wandansa ya koma jikin bango ya jingina saboda jiwa dake neman yaddashi a ƙasa.
      Da Gebrail sukai amfani ta hanyar ɗora masa bindiga akai. Tuni fitsari ya jiƙe gaban wandonsa kuwa. Babuko kwana-kwana wajen kaisu har sashen papa. Tun a falo suka fara bincikensu. Yoohan baiyi niyar binsu ba, amma sai Omar ya kama hannunsa suka shiga. Basu sami komai a falon ba sai cctv dake a ɓoye. dan haka suka wuce cikin bedroom. Akan idon su Yoohan akaima ɗakin dalla-dalla. Ta hanyar tsabar ƙwarewar aiki su little suka gano ɓoyayyar drawer ɗin nan ta sirri dake a jikin bango. Sai dai kuma garƙame take da security, gashi kuma basu sani ba. An gwada password kala-kala baiyiba. Daga ƙarshe suka yanke shawarar yin amfani da na'urar fasa ƙarfe ko wane irine. Ta wannan hanyar aka fasa wajen. Sosai Yoohan ya firgita da ganin kalolin bindigu, da harsasai kala-kala. Sai tarin hodar ibilis da ƙwayoyin shaye-shaye masu matuƙar haɗari.
      Kasa daurewa Yoohan yayi, sai da ya furzar da wani zazzafan hucin da sai da kowa ya juyo ya kallesa. An ƙara bibbincika ɗakin sosai kafin su kwashe duka kayan da suka samu ɗin sannan suka sakko ƙasa inda su mama debora keta faman kuka. Ganin makaman kuma ya sake rikitasu fiye da farko.
         Koda suka fito sai suka shiga bincike gaba ɗaya lungu da


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login