Showing 195001 words to 198000 words out of 318746 words

Chapter 66 - saran boye complete by Queen meenali

01 Jul 2024

41640

data kudundune a ciki har kanta.
     Cikin muryar da bata taɓa saninsa da itaba yashiga kiran “Zeeynab! Zeeynab!”.
        “Hasbunallah” tai saurin ambata akan laɓɓanta jin zuciyarta na neman faso ƙirjinta ta fito waje. duk da ba yaune karan farko da aka kirata da wannan sunanba sai taji tamkar na yau ɗin ya banbanta dana kullum. musamman daya faɗa a saitin kunnenta kuma cikin wata irin shu'umar murya. Gashi da wani irin style ɗin daya banbanta da harshen duk masu kiranta da sunan saboda hausa bata ishi nasa harshen ba.
          Ganin duk yanda yaso yaga fuskarta ma taƙi yarda ya sakashi ƙyaleta, dan cikinsa ya ƙulle matuƙa. Idan kuma ya cigaba da zama a ɗakin za'a samu matsala. Da ƙyar yace, “Okay na fita”.
        Duk da tana jinsa batako motsaba. Amma muryarsa ta sakata jin tsoro. Dagaji kasan baya cikin ƙoshin lafiya. Ƙarar rufe ƙofa kawai taji, daga haka bata sake jinsaba sai da daddare wajen sha ɗaya saura ya shigo lokacin tana ƙoƙarin hawa gado ta kwanta.
          Tanajin ƙamshin turarensa tai saurin ƙoƙarin jan bargo zata lulluɓa. Sai dai tayi rashin sa'a dan harya rigada ya shigo. Ta bashi dariya amma sai ya gimtse. Bakin gadon ya ƙarasa saitin inda ta saka fuskarta. Ya ajiye ledar hannunsa yana faɗin, “Ga wayarki nan, da sassafe zan wuce UK. Please banda jan faɗa wa kowa”.
         Duk da tana jinsa bata motsaba. Sai dai tana kallonsa ta cikin ƴar ƙofar data bari kaɗan kasancewar bata kashe wutar ɗaki dama ita. Daga haka bai sake cewa komaiba ya juya ya fita. Da kallo ta bisa tana mamakin yanda duk yay wani laushi duk da fuskar a matuƙar tamke take ma fiye da yanda ta sani.
      Tanajin ya fita ta yaye bargon da sauri. Mikewa tai tsaye a saman gadon ta dirgo ƙasa. Ta nufi ƙofar da gudu ta murza key kamar ance mata zai dawo. Sai da ta tabbatar tayi gam sannan ta dawo wajen wayar da yace. Ledar ta buɗe cike da doki, sai ko ga waya mai azabar ƙyau ta kamfanin Apple ta bayyana ƴar yayi. ai batamasan ta dirga wani uban tsalle da ihu ba ta ɗane gadon. Sai kuma ta miƙe ta hau rawa duk a saman gadon harda kwaso shoki ta manna a ido duk tana kallon kanta ta mirrorn ɗakin dake kallon gadon.
       Sosai Aymah tasha rawarta da ihun daɗi akan wannan waya kafin ta zauna ta fara dubawa. Komai na cikin wayar yana akwalin dan sabuwace fil. Sai dai a mamakinta anyi caji full, sai dai sim card guda biyu duk suna jikin ƙashinsu bai ɓalleba. Ta ɗauki ƴar guntuwar takardar dake ciki ta karanta abinda ya rubuta.
         _Ki shirya Gebrail zai kaiki kiyi register ɗin layukan duk sanda kike buƙata. Zanyi kwanaki goma ne ko sati biyu. Please banda tsokana, dan an tabbatar min kece kika karyama Miracle ƙafa ranar._
        Da sauri ta zaro idanu waje tana faɗin, ‘La'ila wane shugaban ƴan sherin ne ya faɗa masa? Tab ashe gidan bayan masu shegen kallo da rawan kai akwai magulmata ma. Indai suna son karna shiga harkarsu nima karsu shiga tawa. inko ba hakaba na rantse da gemun baba malam nata karya ɗiyan jama'a a gidannan ana kaima likitoci ɗorinsu’.
     Daga haka ta murguɗa baki tana miƙewa taje ta kashe wutar ɗakin ta dawo ta kwanta tana ƙanƙame wayar a hannunta. Tace, ‘Tab, ai wlhy dake zanyi barci ko sauron ɗakin nan sai dai yayi shawagi a bayan hannuna ya wuce’.
       Da wannan shiriritar tai addu'a tai barci...............✍

         
ZAFAFA BIYAR 2021

Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
  
          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍

ALLAH ka gafartama iyayenm*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.


No. 53

_________________
_*HAJARA COLLECTION, HAJARA COLLECTION, HAJARA COLLECTION, HAJARA COLLECTION._*

_Ina mata masu son ingattun kayan kamshi: Na kece raini? Kayan mata masu sa kishiya k’wafa? Bikin dangin miji ba za’a baki yankan albasa ba da wankin tumatir? To matso kusa domin HAJARA COLLECTION ta kawo muku kayayyaki na gyara ciki da wajen mace, Wanda suka kunshi:_

_Khumrahs: Sudaniyya, Chadian, Dufr, Fara da brown, Kai harda masu flavours... _

_Akwai turaren wuta irin su sandal, Hawi, Alut, Gab gab da sauran su.._

_Akwai turaren tsugunno dana jiki original gangariya tafiyayye dan gaske_

_Hajara collection ta kawo muku air fresheners, Mopping sprays da turaren wanki..._

_Akwai herbal organic soap wato sabulun gyaran jiki na maida tsohuwa yarinya.._

_Sannan Hajia hajara collection tana gyaran jiki.. Tana kuma siyarwa da kayan gyaran jiki na dilke set, Fata tai luwai luwai kamar ta jarirai.._

_Akwai special bridal spa wato gyaran jikin Amarya... Duk Amarya mai son tadinga kamshi har bayan shudewar bikinta to ta nemi hajara collection.._

_Akwai duk wasu nau’in kayayyakin turare masu kamsasa unguwa baki d’aya, Ki mopping tiles suyi sati suna kamshi, Kayan Haj hajara collection akwai inganci sosai._

_Akwai page dinta a favebook mai suna *GIDAN KAMSHI* ga mai son zuwa ya duba hajarta, Ko kuma ya tuntubeta a number wayarta kamar haka: 09032069304_

_Adireshi: KANO NIGERIA, MARIRI dake Kan titin MAIDUGURI RD. KANO STATE.._

_TANA BADA KAYANTA AKAN FARASHIN SARI KO SAYA DAYA DAYA, SANNAN TANA TURA KAYANTA A KOINA AFADIN NIGERIA_

_AVAILABLE IN WHOLESALE/RETAILS. Nationwide deliveries. 100% tested and trusted...!!!_

_Kyau, inganci, Rahusa... Sai kayan HAJARA COLLECTION....!_

_idan anje siya ace daga zafafa biyar.. Akwai special package da Za’a hada maka masu kamshi🥰😍🧚🏻‍♂️_


__________________

No. 53

...............Kamar yanda Yoohan ya faɗa da safe basu haɗu da Aymah ba, dan sammakon barin gidan yayi saboda tafiyar tasa ta gaggawa ce. Zasuyi aikine wa wani shararren ƙusa a gwamnatin UK da aka shaƙama poison a wani taro da yaje ƙasar China. Shima tafiyar tazo masa ne a gaɓar da bai so ba. Dan dama yana shirin ɗaukar hutune saboda fita da zaiyi da Nu'aymah wajen nata aikin itama. Ya kuma ƙiyasta zai ɗauki tsahon wata guda kafin komai ya dai-daita yanda yake buƙata a yanda yay fata. To sai gashi kuma an ɓata masa budget. Dolene kuma yaje wannan nema, sai dai idan ya dawo ya sake sabon tsari.
          
             Da safen koda Aymah ta fito domin yin gyara sai taita laƙe-leƙe a ɗarare. Sai dai taji ko'ina tsit alamar dai baya gidan. Badai ta saki jikiba harta kammala aikin gyara sashen. Ganin bai fitoba ya sata rumtse idanu ta leƙa ɗakinsa. Shiru babu kowa sai kayansa daya cire na barci a saman gado. Da wasu ƴan abubuwan da baza'a rasaba da ya bari saboda saurin karsu makara.
        Ajiyar zuciya ta sauke a hankali duk da ita bawai taji farin ciki a tafiyar tasa bane. Sai dai koba komai ta samu rangwamen kunyar daya aza mata a yammacin jiya da har a yanzu idan ta tuna ita kanta kunyar kanta takeji dan bai taɓa mata irin kalar k... Ɗinnan ba.
        Ɗakin ta gyara masa, ta tattare kayan cikinsa daya tara alamar bai samu damar wankewa ba tana tura baki. Kamar ta bar masa kayansa sai kuma ta tuna ya saya mata waya. Baki cike da iska tace, ‘Wlhy badan halinkaba dai. Dan kar ace banda kirki ka saimin waya mai tsada ni kuma naƙi maka wanki, da a haka zan barmaka abunka’.
           Fitowa tai da su takai toilet ɗin ɗakinta ta ajiye da nufin sai anjima zata haɗa da kayanta data cire ta wankesu.

★★★-----★★★

          Yau satin Nu'aymah biyu kenan a gidan su Yoohan matsayin matarsa. Yayinda Uwaliya keda kwana biyar. Zuwan Uwaliya ya sake bama Aymah damar fahimtar halayyar mutanen gidan sosai. Sannan tana samun abokiyar ɗebe kewa. Dan sosai suka saki jiki da juna ita da Uwaliya. Uwaliya nada wayewar kai sosai saboda yawon da suka ɗanyi da tsohon mijinta kasancewarsa ɗan sanda, tanajin turanci kuma. hakan yasa rashin Yoohan a gidan bai cika damunta ba tunda dama bawani zaman arziƙine ke haɗasu ba da shi a kwanakin da suka kasance tare.
        Yanzu tanayin abinci a sashenta, dan haka babu ruwansu da abincin gidan. Sai dai idan akayi wani abu na musamman a gidan Blessing bata gajiyawa wajen kawoma Aymah. Dan ita dai haka kawai ALLAH ya jefa mata son Nu'aymah. Wani lokacinma dan kawai tazo sashen nata take ƙirƙirar yin abu. Wannan shigowa jikinta da Blessing keyi yaɗan saka sabo tsakaninta da Aymah har tana samun wasu bayanai akan gidan da tsarin zamansa.
       Kamar yanda akeyo cefane wa mutanen gidan haka itama ake kawo mata nata cefanan dan dama dai Yoohan ne maiyi. Tunda ya fara aiki ya saukema papa wannan nauyin. TA yanzu ma tunda Momy takai masa ƙarar Aymah nayin girki a sashenta sai maimakon ya hana kamar yanda madam Chioma taso, sai gani tai washe gari Blessing da Sj sun dawo kasuwa da uban cefane har kashi biyu. Sj yakai nasu kitchen ɗinsu Blessing ta nufi kaima Aymah.
     Tsaidata Momy tayi tana tamabar ina zata dasu?. Cikin girmamawa Blessing taima madam Chioma bayanin cewar Yoohan ya kirata tare da turoma SJ kuɗin cefane kashi biyu. Ayi nasu, akumayima Nu'aymah itama.
       Ba ƙaramin sosa ran Momy wannan al'amari yayiba. Dan haka da kanta ta nufi sashem Aymah. Lokacin suna falo Uwaliya na mata kitso dan kanta ya isheta sai ƙaiƙayi yake mata saboda rashin kitson duk da basonshi take ba. Ko sallama babu ta banko musu ƙofar. Uwaliya ce kawai ta zabura gefe jikinta na rawa. Dan ita harga ALLAH tsoron madam Chioma takeyi. Nu'aymah kam fuska ta haɗe tamau ta cigaba da game a wayarta da har yanzu taƙi bin Gebrail ya kaita tayo register layin da Yoohan yace. Sai ka rantse da ALLAH bataji shigowar Momy ba.
       Wannan shariya ta sake tunzura zuciyar madam Chioma. Da matuƙar masifa tace, “K! Bakiji shigowata bane ba?”.
        Sake watsar da ita Aymah tayi tsahon sakanni kafin ta ɗago idanunta tana ajiye wayar tata da Momy kebi da kallo kamar idanunta zasu faɗo ƙasa. “Momy a ƙa'ida babu wani addini daya yarda da shiga waje babu neman izini. Sai dai bansan a al'adunku ba ko baku da wannan tarbiyyar. Dan haka a matsayinki na babba gareni, ni ya kamata nai wannan kuskuren kimin gyara, ni kuma idan su Victoria sunyi na gyara musu”.
       Wani irin mugun gurnani madam Chioma tayi, a ranta tana raya ‘Dolene taci uban yarinyarnan la'ada waje’. A fili kam saita zuba mata wani mummunan kallo da a tunaninta zai razana Aymah. sai dai ko gezau a idon mutuniyar taku. Saima tsatstsare ta da idanu data sakeyi tana karanto addu'ar neman tsarin ALLAH daga sharrinta a zuciyarta.
         “Yarinya basai kin ƙara tabbatar min ƴaƴan hausawan arewa baku da tarbiyya ba. Ba akan wannan nazo nanba. So nake naji dalilinki na saka my son yo miki cefane ke ɗaya bayan gaba ɗaya ake girki a gidan nan da kowa”.
         Baki Aymah ta taɓe tana zama saman kujera. Kanta taɗan dafe kafin ta sake duban Momy. “Oh my GOD! Ƴaƴan hausawa ginin ALLAH. To momy wannan kuma ai tsakanin mata da mijinta ne. Yanzu a gidan nan ko Mama debora ta isa jin tsakaninki da papa ne?. Inaga ki kirasa zakifi jin komai daga bakinsa yanda ya kamata kamar”.
     Ta ɗauke kanta tana maidawa ga Uwaliya da kanta ke a ƙasa ita da Blessing dake can bakin ƙofa. Saika rantse ba itace tai maganarba. “Uwaliya Please zomu ƙarasa kitson nan inada abinyi, inba hakaba na banbance tarbiyyar hausawa data aljihun baya dan wlhy ni babu ruwana da matsayin kowa gidan nan”.
       Baki Momy ta buɗe a matuƙar hasale zatai magana dan da turanci Aymah ta faɗa, Papa ya shigo falon. Tsawa ya daka mata cikin yare yake magana a fusace batare da Aymah da Uwaliya sunji mi yake faɗa ba. Ita kanta Blessing batajin yaren dan su papa sunajin yaruka kusan uku ne.
     Gani sukai kawai yaja hannun Momy sun fice tana kumfar baki kamar zata haɗiye harshenta. Su Blessing dai basu motsaba, Aymah kam da uwar harara ta raka bayansu tana jan tsaki. Daga ƙarshema ta tashi ta shige bedroom kitson da ba'a ƙarasaba kenan.

     Washe gari da safe papa ya aiko Abraham kiran Aymah. A yanda yaron ya shigo musu babu sallama babu gaisuwa yana magana a gadara ne ya bata haushi. Tako tashi ta tallare masa ƙeya da kama kunnensa ta murɗe tana faɗin. “Kai dan ƙaniyarka ƙaracin tarbiyya yasaka banbance na gaba da kai ne? Ko Muhammad ɗina ya girmeka amma kake neman saka kanka a filin yaƙin da ko uwarka tamin ƙaɗan wajen gwajin ƙwanji”.
       Kuka Abraham ya fasa. Aymah ta sake talle ƙeyar tana nuna masa hanya. “Ficemin anan kafin na maka ɓalli-ɓalli a waɗanan shegun kumatun samfarin gurasar kano”.
       Da gudu yaron ya fita yana kuka. Itakuma ta juya bedroom ɗinta tana bambamin masifa akan wlhy dai-dai take da ƙugun duk wanda yace shi shegene a gidan. Babu mai sakama rayuwarta kahon zuƙa ya tsira. Dan zuru bata cin zuru sai dai a haɗu ai zuru-zuru.
       Itadai Uwaliya binta kawai tai da kallo tana jinjina ƙarfin zuciyarta da tsaurin ido. Sam yarinyar bata da tsoro kamar dangin ifiritu. A fili tace, ‘Koda yake tun kina ciki an gama tsumeki da addu'oi shiyyasa’.

         A falon papa ta iske Momy na banbamin jaraba ga Abraham na sharɓar kuka. Dama ta wuto su Joy na nasu masifar a downstairs kuma tasan duk akanta ne. Kallo ɗaya papa yayma fuskarta shi kansa yaji shakkarta. Duk da kasancewarta ƙaramar yarinya kwarjinita na tada masa hankali dan kallon mahaifinta yake mata. Zama tai tana gaishesa batare data kalli ko sashen da Momy take ba. Ya amsa mata da kulawa.
       “Daughter miya haɗaki da ɗan ƙanin nakine?”.
      Zuciyar Aymah ta gado a ƙirji take. Dan haka tama manta da matsayin wani papa. Cikin ɗacin rai da rufewar idanu tace, “Papa har wannan ɗan mitsitsin yaron yakai girman da zai dinga kawomin raini a gidan nan? Tunda nake bai taɓa gaidani ba. Hakan yasa sam bana shiga sabgarsa. Shine tsabar rainin wayo yanzu yaje yana min magana a tsaitsaye kamar wata sa'arsa, shiyyasa naga ya dace na fara koya masa tarbiya idan wadda aka bashi bata ishesa ba, dan.........”
         A wani irin harzuƙe Momy ta katseta. “Yaƙi ya gaishekin? Ke kina girmama nagaba dake ɗinne?”.
        “Tabbas ina girmama nagaba dani Momy, sai dai fa inhar shi wannna na sama dani ɗin ya nunamin shekaruna da nasa babu banbanci to wlhy zan bi na taka shima na koyar dashi tarbiyyar daya rasa tun ƙuruciya. Kuma wlhy inhar Abraham baya gaisheni a gidannan, koya sake rainani saina sakasa a makarantar jiki magayi a gidanan a kuma gabanki”.
       Ba Momy ba hatta papa lamarin Aymah tsoro ya ƙara bashi. Sai faman jinjina kai yake yana magana da zuciyarsa. ‘Like Father like daughter. Lallai John ya ɗakko mana shugabar ƴan boko haram a gidan. dan kuwa tabbas jinin Sooraj dama bazai kasance na banza ba’. A fili ko sai yaya saurin dakatar da Momy da taso yin magana. “Ya isa Darling. Bakiga yarinya bace ita. bai kamata ki biyetaba. Kuma tama fimu gaskiya. shi Abraham ɗin miyasa baya gaisheta?”.
      Nanfa ya shiga yima Abraham faɗa sosai, ya kuma sakashi bama Aymah haƙuri dole. Itama Momy akan abinda ya faru jiya yay mata sulhu da Nu'aymah. Yasa Aymah bata haƙuri, ya kuma jama Momy gargaɗi akan shiga sabgar Nu'aymah inhar ba wadda ta kasance ƙyaƙyƙyawa ba.
      Hakan ya sake cima Momy rai akan yarinyar. Amma sai tayi shiru saboda maganar da suka tattauna da papan a daren jiya gameda shirinsu akan mahaifin Aymah dama ita kanta da zasu raba da ɗansu nanda lokaci ƙanƙani.
     Daga haka ya sallameta ta tafi. A wannan yinin kaf Nu'aymah tayisa cikin ƙunci ne a gidan. Tare da ɗaukar alwashi kala-kala ga duk jama'ar gidan. Dan ta rantse da gemun baba malam duk sai ta gasa musu aya a hannu. Papa ne kawai zai tsira a cikinsu shima idan yaso.
                 Dalilin wannan rikici Nu'aymah ta sake tsumewa kowa a gidan. Bata da abokin hira sai Uwaliya sai ko Blessing dasu Destiny dake fakar ido idan su mama debora basa falo su shigo mata. Ko kuma idan ta fita harabar gidan shan iska. Dan yanzu da gadara ma take fitowa har falon ƙasan ko harabar gidan ko garden ta zauna tana latse-latse a wayar da babu sim card a ciki koda kuwa suna zaune a wajen. Kota duba buks ɗinta na boko kona islamiyya. Kosu zauna da Uwaliya suyi hira idan sun gama aiki tunda yazam aikin nasu bawani mai wahalarwa bane ba. Komai tare sukeyi da Uwaliya, ɗakin Yoohan ne dai bata taɓa bama Uwaliya damar ko taɓa murfinba. ɗakinta ma itace ke gyara abinta, sai dai wani dalili yakai Uwaliya ciki amma badan aiki ba. Abinci ma kusan Aymah keyin abinta, sai dai Uwaliyan na tayata.
      Kullum sai tayi waya da Umm da Baba malam da Hajjo a wayar Uwaliya. Yoohan kam basu taɓa waya ba tunda ya tafi, ita harma mantawa take da lamarinsa. sai dai duk sanda zata sha chocolate sai abinda ya faru tsakaninsu akanta ya faɗo mata a rai. Haka kawai abin


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login