Showing 234001 words to 237000 words out of 318746 words
tayi. A fili kuwa sai tace, “Kinga kwantar da hankalinki, bara na gama da babyn nan na gabana zanzo gidan”.
Da matuƙar tashin hankali madam Chioma tace, “Haba Rebecca. ina miki maganar matsalata kina magana irin haka? ki tausaya min mana. Banason na rasa Yoohan a rayuwata ko cika burina ban samu nayiba”.
“Hah!! Kinada matsala Chioma. Kema kinsan inaa wannan yanayin babu abinda zan iya miki koda nazo. Garama kiyu hakuri ki bani 1hour kawai”. Cike da matsanancin takaici Madam Chioma ta yanke wayar. Maida akalar kiranta tayi ga Number Yoohan. Sai dai harta yanke ba'a ɗagaba. Dan a lokacin bama wayaba har ita kanta dake matsayin uwarsa ya manta da ita a duniya. Nu'aymah kawai ya sani a yanzu, ita kaɗai kuma yake gani.
Ta jera masa kira kusan biyar babu amsa. Hakanne ya ƙara rikitata ta koma kiran Solomon. shima dai akai sa'a bai ɗagaba. Dan a lokacin yayi barci saboda gajiyar yawon da sukasha, yana dawowa kuma ya samu wata ƴar baby suka shige da ga ciki. Ai saita sake haukacewa. A ruɗe ta fara haɗa kayan tafiya ƙauyensu Madam Rebecca, dama daga can aka yo mata aikin. Dan bazata iya kwana garin Abuja ba batare data san makomar abinda ta ganiba. Bayi ta shiga ta facaccala wanka ta fito. Yanda take komai a birkice sai ka ɗauka tama zare ne. Sai da ta kimtsa tsaf ta fito jaye da ƙaramin trolly da handbag. Sashen Papa ta nufa, kamar yanda tayi hasashe kuwa ta samesa a falonsa zaune shi da Uncle Godwin suna tattauna mai fishshesu. Da ƙyar ta iya ƙoƙarin control ɗin ruɗaninta suka gaisa da Godwin ɗin. Papa dake binta da kallo ya miƙo mata hannu alamar tazo garesa. Zuwa tayi ta zauna a jikinsa cike da dauriya, ta ɗora kanta a kafaɗarsa. Kiss ya bata a goshi da bakinta yana faɗin, “Are you Ok?”. Kanta ta daga masa. Murya a sanyaye tace, “Yes. I'm. Kirane ya sameni na gaggawa daga office ɗinmu, akwai wani taro wai da zamuyi a Lagos dama tun kusan sati biyu, anata ɗagawa kuma sai yau ne wai sukace gobe za'ayi, gashi yanzun an turomin saƙo ni akeson na halarci wajen wai kuma”.
Tuni fara'ar papa ta ɓace a fuskarsa. Dan yana tsananin sonta, koda wasa bayason tanayin nesa da shi. Amma kuma bayason ɓacin ranta. Zai yi magana tai saurin ɗora yatsanta akan bakinsa tana faɗin,
“Please baby”.
Ajiyar zuciya ya sauke a hankali. Badan ransa nasoba yace, “Okay. Yanzu kina buƙatar wani abu ne?”.
“No thanks you dear. Basai na ɗaura maka wata wahalaba ma”.
“Bakinta ya sake sumbata, da murmushinsa na yake yace, “Babu damuwa zan miki transfer ɗin kuɗin shan ice-creem ”.
“Thanks you baby”. Ta faɗa tana sumbatar laɓɓansa da mikewa tsaye. Ta sake cewa “Bey”.
Kusan a tare shi da Uncle Godwin sukace mata “Safe journey”. Daga haka ta fice tabar papa da jimami. Duk da shima hakan wata damace a garesa da zai shanama tashi rayuwar.
Ko sallama batai da su mama debora ba ta fice abinta. Yaran kuwa suna can garden dama. Tana fitowa harabar gidan motar madam Rebecca na shigowa. Tsaki taja tare da nufar motar. Batare data yi magana ba ta buɗe gefen driver ta zauna. Reverse kawai Madam Rebecca tayi suka fice da ga gidan.
Sai da suka hau titi suka fara magana. Madam Chioma ta dage akan a yau zata wuce dan bazata iya kwana cikin abuja ba. Lallaɓata Madam Rebecca ta shiga yi akan ta bari su sami jirgin da zai kaisu jihar River state. Dan tafiyar mota ba abune mai sauƙi a garesu ba. Da farko sam madam Chioma taƙi saurarenta. Sai da tai da gaske da tuna mata ka'idojin bokan sannan ta dawo hayyacinta ta amince zata kwana a gidan Madam Rebecca ɗin. Can suka wuce. Sai dai a ranar sukai booking ɗin jirgi. Tare da kiran bokan shima sukai magana da shi ya basu damar zuwa a goben. Da ga haka suka cigaba da tattaunawa akan lamarin Yoohan da Nu'aymah, dama basusan sunayi ba, dan su suna can a sabuwar duniya😉😎.........✍
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍*_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 62
............Iya wahala Aymah tasha a yau. Hatta shi kansa Sojan nata ya jigatu balle ita. Yama manta kansa matsayin likita, ya manta matsayin Nu'aymah ƴar shekara sha takwas kacal. Ya manta.. Ya manta... Da yawa.
Duk yanda yaso ɗaga ido ya duba halinma da take a ciki ya kasa. Wani irin azababben ciwon kai ne da jiri ke yawo da ƙwanyar kansa. ya yunƙura da ƙyar ya sauka a gadon yana layi. Toilet ya nufa. da laluben bango ya ƙarasa ciki, amai ya farayi babuji babu gani. Hannayensa duka biyu riƙe da kansa da yake neman tarwatsewa saboda azabar ciwo.
Duk da halin da Aymah take a ciki tana jiwo kakarin aman nasa. Sai dai ko idanunta bazatama iya buɗewaba tsabar galabaitan da tayi. Kusan mintuna goma taji motsin fitowarsa. A yanzunma bata iya buɗe ido taga halin da yake a cikiba. Kunnenta dai na sauraren yanda yake fidda wahalallen numfashi, harya ƙaraso ya faɗa saman gadon yana ambaton sunan ALLAH. Hannunta taji ya kamo cikin nasa dake rawa. Ƙam ta ƙara matse idanunta zuciyarta na harbawa da sauri-sauri.
Haka suka kasance babu mai iya taimakawa ɗan uwansa. Ga shi kuma barci yaƙi ɗaukarsu su duka. Ga ciwuka sun musu rijif musamman Aymah da ko maganinta dama bata samu damar sha ba na daren, ga yunwa da take bala'in ji a yanzu haka.
A hankali Yoohan da idanunsa ke a runmtse ya sake jan jikinsa kusa da ita. Muryarsa a ɗashe yace, “Baby. Are you ok?”. Hawaye ne masu ɗumi suka silalo mata, dan ita dai tasan she's not ok ɗin nan. Jin bata amsashi ba ya sakashi buɗe idanunsa da ƙyar yana taunar lip saboda azabar da kansa ke masa. Hannunsa ya ɗora bisa fuskarta ya shiga share mata hawayen dake ziraro mata. Cikin raɗar magana kamar ɗazun muryar a ɗashe yace, “I'm sorry. Forgive me Please Sweet girl”. Ya kare maganar da ɗora kansa jikin nata shima hawayen na tarar masa cikin ido na tausayinta. Dan jikinta ya ɗauki zafi sosai na zazzaɓi. Ga wani ƙaunarta mai zafi na sake ɗawainiya da zuciyarsa. Musamman da ya tuno sharrin da akai mata na zubar da ciki. Gashi shi kuma a yanzu ya sameta cikkakkiyar mace da ya zam shine namiji na farko daya fara ratsata. Hakan ya sake tabbatar masa da zarginsa akan gidansu.
A hankali ta juyo dan son shigewa jikinsa ko zata sami sassaucin azabar da takeji. sai dai kuma wani zafi ne ya ratsata har cikin ƙwalwar kanta. Ta saki siririyar ƙara da fashewa da kuka. “Wayyo Abba ya kashe muku ni. Ummuna zan mutu”.
A tsananin firgice Yoohan ya zabura. Ya riƙota jikinsa tare da saurin dafe kansa yana faɗin, “Achss! My head!. Baby Please i'm sorry, kibar kuka na roƙeki”. Sosai ta mamuƙesa tana cigaba da kukanta jikinta na rawa saboda zafin da takeji wajen na mata.
Gaba ɗaya Yoohan sai ya sake ruɗewa. Duk da matsanancin halin da yake ciki haka ya ɗauketa cak zuwa toilet yana layi, sai jera mata kalmar ‘I'm sorry’ yaketa faman yi kamar shima zaiyi kukan. A wahalcen ya shiga bata taimakon da ya dace yasan kuma zai taimaka mata a irin halin da take ciki. Ya dai sha raki. Dan da azaba ta isheta hardasu ALLAH ya isa tai masa cike da suɓutar baki. Sambatu kuwa iri-iri wani abunma ita kanta batasan mitake faɗaba. Wanda tayi ɗazun yafi wannan, sai dai na yanzu da yake yana a hankalinsa sai yaji ransa duk a jagule. Yana jin haushin kansa akan gaza haƙurin da yay yama tausaya mata kodan ƙananun shekarunta. Yanda take rabzar kuka shima ƙwalla sai famar tarar masa suke a cikin idanu. Da ƙyar dai ya kammala kimtsata ya taimaka mata tasa bathrobe.
Yanzun ma da ƙyar ya iya kawota falo ya kwantar saman sofa. Juyawa yay wajen gadon ya cire farin bedsheet ɗin dan ya ɓaci, sai dai bawani faca-faca ba. Jini ne ɗis-ɗis irin na macen data rasa budurci musamman mai ƙarancin shekaru irin nata. Har aransa yaji takaicin fara sanin matarsa a ɗakin hotel, da yasan hakan zata kasance shikam da gida suka koma abinsu. Amma duk da haka wannan bedsheet kam bazai ƙara yarda wani mahaluki ya kwanta a kansa ba. Inda ma yaji daɗi a ransa dama sabone aka saka musu kamar yanda al'adar hotel ɗin take. A washing machine dake toilet ɗin ya saka bedsheet ɗin ya wanke ya busar da shi. Sannan shina ya tsaftace nasa jikin ya fito.
Kafin ya dawo gareta har barcin wahala yayi awon gaba da ita. Dan idanu ya rumtse sosai da cire tausayinta yay mata gashin ɗaya tamkar da dubu. Cike da dauriya yay order ɗin abinci dan yasan zataji yunwa. kuma ya tunama batasha maganinta ba. Ba'a rufa mintuna goma ba kuwa sai gashi an kawo musu. Lokacin yana ƙoƙarin canja musu bedsheet cike da ƙarfin hali dan jiri yake gani. Ga ciwon kai kuma. Zuwa yay ya buɗe ya amshi abinci ya koma ciki. Sai da ya gama kimtsawa tsaf sannan ya tasheta zaune. Kuka ta sanya masa duk da kuwa yanzu zafin ya ragu, sai dai zazzaɓi da jikinta da takejin na mata ciwo na bala'i. Kasancewar yunwa takeji sai gashi taci abincin daya bata da kansa. Ya bata maganinta daya tabbatar zai taimaka mata tunda zatai barci. Ayko bata rufa mintuna biyarba sai barci. Da ƙyar ma ya samu ya ta yarda ya saka mata kayan barci ya taimaka mata ta koma kan gadon. shima dai kayan barcin ya canja ya kwanta dan jikinsa sai karkarwar zazzaɓi ya keyi. Ga ciwon kai tamkar ana ƙara masa shi.
Sai gashi ita Aymah ta samu barci mai nauyi, shiko dake rungume da ita ya kasa rintsawa. Ga zazzaɓi da ciwon kai. Sau biyu yana zuwa yay amai. Hakan yasaka shi sake galabaita fiye ma da farko.
Yau ma Alarm ne ya tadasu, koma nace ya tada Nu'aymah dan shi dai Yoohan bama barcin yayiba. Garama gabannin asuba yaɗan fara figarsa sama-sama sai kuma ya farka. Daga haka bai sake komawaba har alarm ɗin ya buga. Sosai jikin Aymah da sauƙi dan zazzaɓin nata ya sauka ita. Sai dai rashin jin daɗi jiki da sabon al'amari ya haifar. Sai ciwo ƙafafunta dake mata. Jinta take fayau kamar iska zata ɗauketa ta kayar. Bakinta ko ɗaci, ɗan-ɗanɗanon data fara samu yana dawo mata ya sake guduwa. Yanda take tsananin jin kunyar Yoohan ɗinne ya sakata tashi zaune batare data yarda ta kalle sashin da yake ba, sai faman matse baki take dan can wajen kam da zafi har yanzun.
A hankali ta dinga tafiya tana hawaye har bathroom, Yoohan na kwance yana kallonta cike da tausayi, duk yanda yaso ya yunƙura ya sake taimaka mata ya kasa saboda ciwon da kansa ke masa ga zazzaɓi irin wanda shikam a rayuwarsa zai ce ya mata rabon da yayi zazzaɓi mai zafi irin wannan.
Aymah na shiga bayin ta fashe da sabon kuka mai sauti tana kiran baba malam da Umm suzo su taimaketa. Ta kai mintuna huɗu zaune a aɗan step ɗin hawa wajen bathtub ɗin kafin ta miƙe da sanɗa ta nufi madubi wani daɗi na ratsata na hango wayar Yoohan a jiye. Da alama dai a daren jiya ya manta da ita kenan.
Umm ta riga da ta mata tarbiyyar duk abinda ya sameta ita take fara sanarmawa, sai dai a yanzu abinda naga Aymah na shirin aikatawa ya sake tabbatar min da tsabar wautar dake a kanta, dan kuwa number ɗin Umm ta shiga lodawa cikin wayar tai dailing. Kuka ta sanya da dariya a lokaci ɗaya jin kiran ya shiga.
Daga can Nigeria kam Umm na idar da sallar magriba kiran ya shigo. Da mamaki take kallon Number dan bata kawo Aymah a rantaba. Tunda tasan indai zasu gaisa a wayar baba malam mijinta ke kira sai shi kuma ya bata su gaisa. Tana gab da tsinkewa dai tai ƙuru ta amsa, tare da kaiwa kunne tai sallama. Maimakon mutuniyar taku ta amsa sallanar sai kawai ta fashe ma Umm da kuka. Shiru kawai Umm tai tana saurarenta dan ta gane abarta. Sai da ta barta tayi kusan na minti ɗaya sannan tai gyaran murya. “Mike faruwa?”. Umm ta jefa mata tambayar.
(Nazata bazata iya faɗaba fa😱) sai kawai Aymah ta gyara zama ta fara faɗin, “Umm dan ALLAH kuce ya maidoni gida. wlhy ban taɓa iskanciba. Na rantse da ALLAH Umm ba laifina baneba, sai da naita roƙonsa karyayi banaso, amma shi mugune sai da yayi. Gashi na kasa tafiya, wajen kamar zai fita, ciwo yake min, gashi inajin fitsari inajin tsoron yi Um........”
Harga ALLAH dariya ta bama Umm, amma sai ta danne abinta tai saurin faɗin, “To ya isa zubaina sarkin magana. Wai nikam yaushene ranar hankalinki Nu'aymah?. Kai ALLAH na gode maka ni Firdausi. Yanzu shi mijin naki yana ina kike zubamin zance haka?”.
Baki ta kumbura na haushin ba'a barta takai ƙarshen labariba tace, “Yanacan ɗaki bai tashi ba. Ni kuma ina toilet asuba fa tayi anan”. Ta ƙare maganar hawaye na silalo mata.
Ajiyar zuciya kawai Umm ta sauke hawayen farin ciki itama na silalo mata. Koba komai dai ta fahimci yarinyarta takai mutincinta gidan aurenta. ALLAH ya ƙara wanketa a garesu ga ƙazafin da akai mata. Hawayenta ta share. Tace, “Ki shiga ruwan zafi kinji ko, ki daure duk zafinsa ya ratsaki sosai zakiji daɗi”.
“Umm wlhy jiya daya sakani kamar zan mutu. Dan ALLAH ki faɗamin wani maganin sai nace ya sayo min zansha. Amma dan ALLAH kice Abbana ya kirashi ya kawoni gida yau”.
“To naji, yanzu ki ƙara shiga ruwan zafin bazakiji zafin kamar na farkoba kinji ƴar albarkana”.
Cikin jin daɗin sunan ƴar albarka da Umm ta kirata tace, “To Ummuna. In kiraki video call ki ganni, ƙila zakifi ƙarajin tausayina ma”. Da sauri Umm tace, “A'a jekiyi abinda na sakaki, kije kiyi salla lokaci na shigewa”.
Fuska ta ƙwaɓe zatai wani sabon kukan, zatai magana Yoohan da shirunta ya sakashi a damuwa ya taso da ƙyar ya biyota yay azamar zare wayar daga hannunta dan yaji maganar video call da taima Umm, sai dai baisan amsar data bataba da ga can.
Zabura tayi dan batasan da shigowar tasa ba. Shi kuma ya zaune a step din yana dafe kansa da faɗin, “Acshh!! Kaina”. Miƙewa ta nemayi duk da ganin yanayinsa ya bata tsoro, yay saurin damƙo hannunta ya maidata ya zaunar. Hannunsa dake akan goshinsa ya cire yana dubanta da idanunsa dake jajur. “Zeeynab baki da hankali wa kika kira? Ba dai Uncle ba?”.
Tana cika kumatu da iska tace, “Ni ban kira Abba ba, Ummna na kira na faɗa mata abinda kaimin. Nace tasa Abbah yasa ka maidani gida”.
Tuni ya manta da maganar ciwon kai, ya waro idanu waje yana faɗin, “Kin kasheni Zeeynab. Kika faɗa matafa kika ce?”.
“To wa yace kayi? Gobe ma ka ƙara kaga idan bankira harda Hajjo da Abbana da Addah duk na faɗa musu ba ALLAH. Kai harma Ananah sai tasan halinka”.
Gaba ɗaya kunya ta lulluɓe Yoohan, ji yake tamkar yana a gaban Umm. cike da ƙarfin hali yace, “Yarinyar nan ALLAH har yanzu kanki da motsi, dole na sake maidaki wajen su Dr Liam”.
Umm da duk take saurarensu da ga can ta yanke wayar tana dariya. Dama ta tsayane ta sake gaskata zancen Nu'aymah. Wayar ta ajiye tana faɗin, “Yaron nan kaga takanka indai Nu'aymah ce. Bayan motsin ciwo dake a kanta akwai ma na hali wlhy. Ni harma ka bani tausayi”.....
“Waye ya bada tausayi?”. Cewar baba malam dake shigowa ɗakin. Dan dawowarsa kenan gidan. Juyowa tai tana cigaba da dariyarta. Ya zauna a bakin gadon ya riƙo hannunta. “Jannat da alama dai kina cikin farin ciki, zoki ɗan sammini nima muyi tare”. Sosai take ƙara faɗaɗa dariyarta. Ta shiga bashi labarin kiran da Nu'aymah tai mata da drama ɗin data gama ji tsakaninta da Yoohan a ƙarshe. Shi kansa baba malam sai da ya dara.
“Ai Jannat lamarin mamana sai ita. Yarinya tamkar goyon kaka. Amma koba komai ni hakan yamin daɗi tunda munji cewar dai sharri dai akai mata kamar yanda zukatanmu ke faɗa mana. Wannan shine amfanin ka bama yaro tarbiyya akan duk abinda ya shafesa ya sanar maka. ALLAH yay musu albarka su duka. Ya azurtasu da zuriya masu albarka da alkairi. Wadda zata zama maijin ƙai a garesu damu baki ɗaya”.
“Amin ya rabbi. Sai dai kuma naji muryar mijin nata kamar wanda baida lafiya ma. Dan da ƙyar yake magana”.
Ɗan jimmm baba malam yay yana sauke numfashi. Yace, “To inaga dai bara na sanarma yaron nan abokinsa shi sai ya nema wanda zaije ya