Showing 27001 words to 30000 words out of 318746 words
din hoton Nadeeya da aka Mata lokacin da zaa Saka su a makaranta ya fice da sauri.
Ni kuwa na durk'ushe a wajen na cigaba da kuka na kasa yarda Wai Nadeeya ta b'ata yarinya da nayiwa wanka da hannuna ko wando babu.
Maganar da Umma keyi cikin huci yasa na tsayar da kukana Ina kallonta
"Yau ni Naseer ya ke d'agawa murya yake min ihu sabida yarsa ta Bata lailai Naseer yayi Nisa ba karamin asiriceshi wanan tsinananiyar tayi ba ba dai Dan Nadeeya kike wanan kukan ba ba Dan Nadeeya Naseer yamin ihu Ina mahaifiyarsa ba toh sai ku ganta nagani"
"Duk wannan Abun fa laifinki ne Hajara ke Kika bar yarinya nan ta zauna dashi har yanzu har ta juyar Masa da kwakwalwa ace yau sati biyu da auren mu ya kasa kallon Inda nake tsabar wanan kanjalalliyar ta asirice shi ki barwa Umma komai ta Miki maganin shegiya"
Ta ce tana jefomin harara
Umma kuwa tayi wani irin murmushi ta mik'e tana k'ok'arin shiga daki.
Da Sauri na rik'e kafarta na saki ihu Ina ta taimaka ta fitomin da yata wlh idan Naseer ne Zan rabu dashi a yau
Tureni tayi ta shige daki.
Zahira dake lab'e a bayan kofar dakina ta fito ganin Ina ta rusa kuka Ina Kiran sunan Allah Dana Nadeeya ba irin tunanin da ba darsu a Raina ba Kar dai su Umma kashemin Nadeeya sukayi.
Zahira Humaira ta mik'o min dake ta tsalla kuka daga ita har Minal ba Mai Kaya a jikinsu sai Zahira karbar Humaira nayi na sa Mata no-no a baki take ta karba na umarci Zahira ta d'auko wa Minal Kaya ita da Humaira.
Tana tashi Mmn Mannir ta shigo ita da wasu makotana wasu ma ban San su ba duk sun zo min jaje sai Kara tambayata suke Taya Nadeeya ta b'ata ban ma iya musu magana ba sai bani baki suke suna kwantar min da hankali akan za'a ganta an Kai cigiya gidajen radio har da tv dayake Naseer nada Abun hannu duk an raba musu passport din Nadeeya.
Ni dai har lokacin sai Naga kamar zanga Nadeeya ta fito daga d'aki.
Mmn Mannir kuwa Humaira ta karba daga hannuna ta goyata Ni kuwa na mike na Shiga bandaki na daura alwala na fito na hau Kan Sallaya na tadda Sallah karatun Sallah ma da k'arfi na ringayi Ina kuka a Sujadda kuwa Haka na ringa rokon Allah ya Kare min yata a duk Inda take ta dawo gareni cikin koshin lafiya Ni nasan su Umma ne suka daukemin 'ya har tsawon wane lokacin Zan ringa irin wanan rayuwa a yau na gaji wlh na gaji ya zama Dole na dau mataki.
Ina iddarwa na fito nayi k'ofar gida Inda duk makotana suke tsaye duk Yan layin ban gansu ba sun tafi neman Nadeeya daidai da masu shaguna duk basu bud'e ba sabida mutuncinsu Amma ace uwar mijina ita Tana daka ko a jikinta.
Waje daya na samu na zauna Ina ta tunanin ganin ta Inda zanga Nadeeya ta b'ullo addua kuwa na fili Dana zuci Haka na ringa Yi.
Lukman da danladi Mai Kai su makaranta sun dawo gidan yafi a kirga Akan suji ko an ga Nadeeya Amma shiru ba a ganta ba ahaka har Yamma tayi babu Naseer babu dalilinsa.
Kuka nake sosai Ina rokon Allah ya karemin Nadeeya har yanzu na kasa yarda Wai daga fitowa Nadeeya wanka an nemeta an rasa.
Naseer kuwa kudi ya saki sosai ya bada cigiyar Nadeeya gidajen radio da unguwa unguwa har Inda baa yi tunanin zuwa ba Haka aka ringa neman Nadeeya da passport din hotonta Sallah ma Naseer ba a nutse yake Yi ba har kunyar ya cewa mutane daga wanka Nadeeya ta fito aka nemeta aka rasa sai kace wata Kaya.
Ahaka suka danganta neman Nadeeya kusufa kusufa lungu da sako kwaryar Kano baa ganta ba wajen Magriba Naseer da wasu Yan unguwarsu suka tsayar da motarsu Dan suyi sallah a wani unguwa kawo dayake unguwar Bata fiye cika ba a wanan lokacin Kamar daji ne sai a lokacin ake yankar fili ake ginawa.
Daya daga cikinsu ne ya nausa wajen daji dajin da yayi fitsari ya fito yayi alwala daga nesa dashi ya hango wani katon Rafi ruwa nata Dan gudu gashi wawakeke wata Yar karamar yarinya ta bada baya tana Dan jefa abu a ciki ba Kaya a jikinta.
Murza idonsa yayi ya sake murzawa idonsa duk da Bai ga fuskar yarinya ba sai yake ganin kamar Nadeeya Amma Dan ya gasgata zargin da yake ahaka ya ringa matsawa kusa da yarinya kafin a hankali yace "Nadeeya"
A hankali Nadeeya ta juyo idonta yayi jawur hancinta duk Majina kana gani kasan taci kuka ta gode Allah wajen a ruwan yake ma da alama baa fiye wucewa ta wajen ba
Ihu ya saka ganin Nadeeya na ganinsa ta fara k'ok'arin mik'ewa tana mik'a Masa hannu Dan Dama Mai kawo Mata d'auki take nema shi kuwa cikin zafin nama ya Isa wajenta ya tarota da Sauri Dan kiris ya rage ta fada ciki.
Wani irin ajiyar zuciya Nadeeya ta ringa saukewa tayi lamo a jikinsa jikinta yayi zafi zau.
Shima Salisun kamkameta yayi yayi wajen da suka Parker motarsu da har Naseer ya iddar da sallah ya gaji da jiransa.
Kamar a mafarki ya hango ya fito da Nadeeya rungume a kirjinsa Bai San lokacin da ya nufesu da Sauri Yana "Mai ya sameta? A Ina ka ganta"?
Yace Yana karbe Nadeeya daga hannunsa ya hau tattab'a jikinta Inda Nadeeya tana ganin Abbanta ta fashe da kuka tana Kara kamkame shi.
Naseer kamar ya maida ta cikinsa ya rungumeta Yana shafa jikinta
Salisu kuwa ya hau bashi labarin yanda ya ganta ya Kuma ringa Al ajabin yanda Nadeeya ta iya zuwa tunda Goron dutse zuwa Kawo idan ba mutum ne ya kawo ta Nan ba Taya zaayi tazo Nan
Naseer Bai iya Jan motar ba sai salisu ne yaja motar shi kuwa ya zauna daga bayan motar da dayan makocinsa suna ta mamakin Inda suka tsinto Nadeeya Naseer kuwa rufe idonsa kawai yayi Yana Jin kukan Nadeeya a kirjinsa Yana Jin wani irin suya a kirjinsa shi ba yaro bane yasan d'auke Nadeeya akayi Kuma ba wasu ne.suka d'auke.ta ba sai Mahaifiyarsa tunda yasan wacece ita.
Baiyi magana ba har suka iso gidan da mutane ke cike Suna jajanta b'atan Nadeeya.
Naeema kuwa taci kuka ta gode Allah tayi zaman dirshan a kasa Ana ta Bata baki
Tsayuwar motarsu yasa ta mik'e da sauri Inda Naseer shi.kuma ya bud'e motar ya fito rungume da Nadeeya
Mutane na ganin ta suka hau hamdala suna "Alhamdulillah Anga Nadeeya a Ina aka ganta"?
Sosai mutane Suka nuna farincikinsu da ganinta suka hau tambaya inda aka ganta.
Naeema kuwa da Sauri ta ture mutane ta karbi Nadeeya daga hannun Naseer tana sauke wani irin ajiyar zuciya.
Ta rungume Nadeeya Gam tana hamdala
Hajara da Hindatu ihun Murnar anga Nadeeya ne yasa Suka fito daga d'akin da Sauri suka lek'o ta saman bene cikin tsananin mamaki Dan bakin ruwa Suka kaita Kuma suna da tabbacin fad'awa zatayi ta mutu Amma ga mamakinsu Wai an ganta Kuma su sun San Inda suka kaita sai anyi dagaske xaa San wajen.
Wani irin ihu Hajara ta saka ta sauko daga Kan benen ta zub'e a kasa ta hau buburwa ta cire zaninta ta Yar ya rage daga ita sai Dan skirt sai kuka take Tana zubawa kanta kasa.
Mamaki ne ya rufe mutane suna kallonta tare da mamakin Mai ya kawo ihun nata ita da zatayi farinciki anga Nadeeya (wlh page dinan babu fiction ko daya a gaske Haka matar Nan tayi Dan bakin ciki an ga Nadeeya)
Ni kuwa ko kallonta banyi ba na rungume yata na haye sama
Naseer kuwa kamar kasa ta bud'e ya shige Dan kunyar yanda take ihu tana watsawa kanta kasa Wai Nan da Sunan Mahaifiyarsa ce wato gawan Nadeeya taso gani
Mutane kuwa da basu San Mai ke faruwa ba hakuri Suka hau bata suna ba kuka zatayi ba ta Godewa Allah da aka ga Nadeeya ba Kuma abinda ya sameta.
Naseer shima da Sauri ya hau saman bene Yana Jin kamar kirjinsa ya fad'o
Sai Hindatu ce ta sauko ta dauko mata zaninta ta mikar da ita suka koma ciki.
Da yawa ta basu mamakin abinda tayi sabida tunda aka fara neman Nadeeya Bata lek'o ba Amma abin mamaki ana ganinta ta fito tana ihun kuka Mai hakan ke nufi.
Wasu Kuma basu kawo komai ba sun dauka kukan farinciki take da ganin Nadeeya.
Ni kuwa Ina shiga ciki d'akina na wuce da Nadeeya na kullo k'ofar na kwantar da ita na fara duba jikinta Naga babu abinda ya sameta sai kafafunta dai da suka balain suntume sukayi budu bud' da kasa
Sai jikinta da yayi zafi sosai.
Bana rabo da ruwan zafi hakane yasa na hada ruwa Mai balain zafi na wanke Nadeeya tas na Kara zuba wani na hau dadanna Mata kafa sai danaga ya fara Sab'ewa sanan na dauko robbb na shafe Mata jikinta dadin wankar yasa take bacci ya d'auke ta tana ta sauke ajiyar zuciya Ni kuwa na zuba Mata Ido hawaye na sauko min ko a Ina su Naseer suka ganta.
Naseer kuwa a Palo ya zauna ya rik'e kansa sabida azabar ciwo da tunanin halin mahaifiyarsa ahaka su Hajara suka hawo sama tana ta kuka
Suna dab da wuce Naseer
Naseer ya dago Yana "Umma ba Haka Kika so ba ko?kin so ace gawar Nadeeya na shigo dashi gidanan Umma Mai na Miki Haka Dan Allah Dan annabi Umma Mai na Miki Dan Allah Dan annabi ki gayamin na nemi yafiyarki Umma"
Naseer yace Yana durk'usawa Akan gwiwar sa kukan dayake d'annewa ya kwace Masa.
Hajaran Bata ce komai ba ta Shige d'akinta tana Jin kanta na ciwo sabida a rayuwarta Bata da burin daya wuce taga Naeema ckin bakin ciki a Rayuwa tunda ta kasa rabata da Naseer gwara ta Taba abinda tasan sune ranta Dan taso Zahira ta d'auke Dan ta lura itace Mafi soyuwa a wajen Naeema sai Zahira bata futo ba Nadeeya ta fito sai gashi cikin sauki wai har anga Nadeeya bama ta mutu ba da ranta lailai Naeema tabbas akwai abinda ta taka da Bata iya cin Galaba Akan ta.
Har wani zazzabin bakin ciki tayi
Naseer shima halin mahaifiyarsa da matsanacin tunani sai daya saka Masa zazzabi
Ni kuwa Ina daga d'akina Ina Jin duk abinda Naseer ke cewa Umma kukan da Naseer keyi ya tab'ani sosai hakane yasa na Sha alwashin kawo karshen wanan matsalar da muke ciki.
A Daren ranar duk mu ukun babu wand yayi baccin kirki Dan Naseer zazzabi halin mahaifiyarsa ya hau Yi ko shigowa d'akin baiyi ba a palon yayi kwanciyarsa ko sallah daya Saba yi daddare ma a ranar baiyi ba Ni Kuma hanyar da zata bille Dani ya hanani bacci ita Kuma Umma bakin ciki. Duk Abubuwan da takemin Ina tsallakewa gashi shugabarsu tayi fushi tace zata kwace komai daga hannunta tunda Naeema tana neman fin karfinta.
Washegari Nadeeya ta tashi fes ba wanan kumburin ahaka na had'asu na musu wanka na rufo kofata na nufi kitchen Dan na Dora Mana abinci banyi tunanin shiryasu su tafi makaranta ba Naseer ma ban ganshi a palon ba Dan tunda ya fice da asuba bana Jin ya sake dawowa sosai naji Ina tausayinsa.
Daga Umma har Hindatu banji motsinsu ba har na Gama Abunda nake na ajiye musu nasu a Palo na Kai Mana namu daki Dana Naseer.
Dan nayi alkawarin har na cimma burina bazan Kara Shiga dakinsu ba.
A faranti daya muka ci Abinci da yayana Sansu na ratsani Ina kwarara musu addua a Zuciyata.
A hankali Kuma Ina tambayar Nadeeya yanda ta ba ce bamu ganta ba Bata iya min magana ba Dan tana da Dan nauyin baki.
Har Minal ta Dan fita baki.
Wajen karfe goma na safe na fito daga d'akina bayan na kulle k'ofar dakina har lokacin Naseer Bai dawo ba Kuma banji motsinsu Umma ba Naseer nafi damuwa nasan halin da yake ciki ba Umma ba hakane yasa nayi waje.
Ina su lukman suka hau gaisheni suna tambayar Nadeeya Ni kuwa nace Tana Nan lafiya Lau daga Haka na wuce gidan mmn Mannir Dan zuwa yanzu banida dai Sama da ita bayan Naseer dan naji Dadin yanda ta nunamin damuwarta jiya tamkar yar uwa ta Haka nake ganinta.
Banyi tunanin Zan sameta a gida ba Dan na d'auka taje makaranta amma Ina zuwa na sameta taji dadin ganina anan muka gaisa taso ta tada maganar abinda ya faru tsakaninta da Umma har ta Dan sakomin zancen tana zargin ita ta d'au Nadeeya Ni kuwa na Kau da zancen na hau Gaya Mata abinda ke tafe dani da taimakon danake so tamin Dan Nagaji da irin wanan rayuwar da muke nida yayana Kuma idan na biyewa Naseer Haka zamuyi ta zama muna cutuwa.
Sai data Yi Dan Jim kafin tace zata taimaka min ta hau tsaramin yanda zamuyi take naji dadin shawararta Inda ta tsaramin duk yanda zamuyi Amma fa tana tausayin Naseer.
Murmushi kawai na nata Dan Mai daki shi yasan Inda yake Masa yoyo.
Sallama na Mata akan Zan dawo anjima
Ina koma wa gida Naga Naseer ya dawo idonsa ya fada sosai yayi wani sanyi kalau kamar mara lafiya Bai cemin daga Ina nake ba na Shiga d'aki na dauko masa abincinsa Ina k'ok'arin ajiyew yace min azumi yake bance komai ba na dauke abincin na mayar kitchen na fara k'ok'arin Dora Mana abinci Rana Ina cikin girkin Hindatu ta shigo ta ajiye kwanuka tare da dalla min harara sai anan nasan Ashe ma suna Nan
Ina gamawa na Kara shigewa daki a Inda Naga Naseer har yayi wanka zai fita.
Yacemin bazai dawo da wuri ba fatan dawowa lafiya kawai na masa Yana fita na dauko katon akwatina na hada Mana kayanmu nida Yara sai danaga ba kowa a palon Naja akwatin na Kai gidan mmn Mannir Kuma cikin ikon Allah babu Wanda ya ganmu.
Kamar Naseer yasan Mai nake shiryawa tunda ga ranar Bai Kara fita ba.
Nima sai neman hanya nake kwana biyar da faruwar.haka Umma ta fito palon Wanda tunda aka ga Nadeeya ta shige daki ban Kara ganinta ba sai ranar Dan Hindatu kawai nake ganin tana Shigar musu da abinci.
Wani irin kallo take min Ni kuwa na dauke kaina Zan iya cewa wnan shine Karo na farko a rayuwata da naki gaisheta.
Girgiza Kai tayi ta had'e Rai ta zauna a Palo Naseer kuwa Yana ganin ta fito ya mik'e ya fita.
A ranar wani kallo Umma take jefamin na tsana Kamar zata kamoni ta yankani Ni kuwa Ina Gama ayyukana na shige daki.
Washegari jikina duk ba kwari na shirya su Zahira suka tafi makaranta
Wajen Sha daya Naseer na fita na goya Humaira na karewa d'akina kallo hawaye na zubomin
Na ajiye wa Naseer wasika a karkashin gado na fito da ga d'akin
Banga kowa a palon ba Ina fita na amshi kudi wajen lukman a cikin kudin Naseer wajen Dubu goma wanan lokacin.
Na dau hanyar makarantarsu Zahira Ina zuwa nacewa mallamarsu inasan zamuyi tafiya ne an Mana rasuwa take ta Kira su Zahira suna zuwa na rik'e hannunsu muka hau tafiya sai da muka je karshen layin na had'u da mmn Mannir dake ta jirana da akwatin kayanmu.....
[6/13, 10:50 AM] Queen Meenali👑: *NAGA TA KAINA*
*NA SADNAF*🌸🌸
®️ *_PURE MOMENT OF LIFE WRITERS_*
_{We Don't just entertain nd educate we also touch the heat of readers P.M.L}💪🏻_
*Free Novel*
*Page 18*
Bansan hawaye nake ba sai da mmn Mannir da itama Naga jikinta duk yabi yayi sanyi tace "Anya Naeema kina ganin wanan matakin shi ya dace ki d'auka?Anya kina ganin kinyiw Naseer adalci kuwa?
Ban iya ce Mata komai ba Dan matsawar nayi magana kukan danake dannewa zai iya k'wacemin Agaban yayana Zahira tana da wayo tunda muka fito daga makaranta take min tambayoyi Ina zamuje yanzu ma sai kallona take.
Mmn Mannir itama sosai Naga idonta ya kad'a yayi ja Ina biye Mata Haka zamuyi ta tsayuwar hakane yasa na Ciri hannu na fara k'ok'arin tsayar Mana da taxi Dan lokacin ba adaidaita sahu.
Dak'yar muka samu Wanda ba kowa a ciki na sunkuyar da kaina nace ya kaimu tasha.
Sai daya fito ya saka Mana kayanmu na bud'e bayan na saka su Minal Ina k'ok'arin kamo hannun Zahira ta Kara cemin "Umma Ina zamuje Dan Allah idan tafiya zamuyi mu tafi da Abba Kar shima Mama ta ringa dukansa dayake mama suke ce Mata"?
Hada Ido mukayi da mmn Mannir da har hawaye ya fara zubo Mata tana daukewa sabida Kar a gani.
Ni kuwa na saka Zahira a cikin motar da k'arfi Dan banasan magana kukan danake dannewa ya fito.
Ina zaunar da ita na shige na rufo k'ofar Ina k'ok'arin yiwa Mmn Mannir godiya Naga ta bud'e gaban motar ta hau.
Ba Wanda yayi magana a cikin mu har muka Isa Tasha muka sauka na biya Mai taxi bayan ya sauke Mana kayanmu
Mmn Mannir ce ta shigemin gaba wajen Nemo motar garinmu aka cajemu na biya sai da su Zahira suka hau sanan na juyo na rik'e hannun mmn Mannir Ina "Nagode da alkhairinki a gareni bazan manta dake ba"
Hawaye ne ya hau zubo Mata ta damke hannuna tana "Naeema Dan kin dage ne Zaki tafi da kin hakura kin zauna wuya Bata kissa watarana sai Labari da Zaki bani hadin Kai wlh zamuyi maganinta ya Naseer zaiji idan ya dawo yaga bakya Nan kin Kuma tafi da duka yaran wlh Naeema bazaiji dadi ba"
"Bazaki gane ba Mmn Mannir bazaki gane Hatsarin Zama na da Naseer ba Mmn Mannir da iya Ni kadai ummaa zata tab'a kila na iya jurewa da iya Ni kadai zata ganawa azaba kila na iya daurewa ko Dan sabida yarana Amma me Umma yanzu ta bar kaina ta koma Kan yayana Wanda duk abinan sabida su naki tafiya tuntuni Akan me Zan cigaba da zama yau idan Allah ya karemin Nadeeya gobe nasan salon da zata zomin dashi wlh Nagaji mmn Mannir ko baccin kirki bana iya yi na rasa Mai na Mata laifine Dan na auri danta yau kina ganin da iyayena suna rayye zata min abinda takemin banida kowa sai Allah sai Naseer toh shima Naseer din tace sai mun rabu toh na rabu dashi rabuwar