Showing 273001 words to 276000 words out of 318746 words
kana ganinta da ƙyau?”.
“Yes maaa!”.
Duk da Rabi ta kalli fuskar lap-top ɗin itama bata kawo komaiba, tadai ga kamar hoton mijin Nu'aymah, kafin tunaninta ya faɗaɗa Little bee ta katseta da faɗin, “Minene sunanki?”.
Murya na rawa tace, “Rabi?”.
“Shekararki nawa kina aiki a gidan Sheikh Soorajidden Hashim Jibiya?”.
“Goma sha takwas. Dan an kainine lokacin matarsa nada tsohon cikin dake wahal da ita dan na taimaketa”.
“Kin taɓa aure?”.
“Eh na taɓayi harda yarana biyu”.
“Keda ke aure miya kaiki gidan aiki har tsahon wannan shekarun?”.
“Ranki ya daɗe ai auren ya mutu ne a wancan lokacin. To domin neman na kaina saina samu aikatau ɗin dan nayi saboda iyayena duk sun rasu ni marainiyace”.
“Ƙwaɗayin zama gidan masu kuɗi yasa baki sake tunanin sake ƙara aure ba kenan?”.
Shiru tayi kanta a ƙasa ta kasa bada amsa. Shima Dawood da yay maganar sai ya shareta da ga haka ya sake jeho mata wata tambayar.
“Waye ya kaiki gidan?”.
A take ta ruɗe jikin na rawa, sai in ina take ta kasa bada amsa. Hakan yasa Dawood daka matsa gigitacciyar tsawa. Fashewa Rabi tayi da kuka. “Dan ALLAH ku gafarce ni zan faɗa”.
Babu wanda ya tanka mata. Sai bindiga da little bee ta ciro a gefen ƙugunta ta dire a gaban Rabi. Hakan yasa ta kuma diriricewa. Cikin hadiye kukanta tace,
“Ranku ya daɗe ni bansan ainahin wadda tasa aka kaini gidan ba. amma naje ta hannun wata matace amma yanzu ALLAH yay mata rasuwa”.
“Oho, idan na fahimci amsar nan taki kenan dama an kaiki gidan ne da wata manufa? Ba wadda kike a wajenta bace tasa aka kawoki gidan!!”.
Yoohan yay magana a matuƙar zafafe. Maimaita mata Dawood yayi da hausa. Dan duk da Yoohan ya haɗa da kalmomin hausa a maganar Rabi bata fahimta da ƙyau ba. Amma shi Alhmdllh yana fahimtarta sosai tunda jin nasa yafi faɗi da baki.
A take Rabi ta ƙara rikicewa, dan har ga ALLAH tazatafa hoton Yoohan ɗinne kawai a wajen. Suma dai su Bily yanda yay maganar duk sai da ya sakasu kallonsa. Tebir ɗin Little bee ta daka da hannu, da tsawa tace, “Ki basa amsar tambayarsa malama kin ɓata mana lokaci”.
Jikin rabi na cigaba da rawa tace, “Ranka ya daɗe ba haka nake nufi ba. Ni dai kawai an kawonine na kula da mai ciki, daga haka babu wani dalili dana sani na rantse muku da girman wanda ya halicceni”.
A karan farko taji saukar mari mai gigitarwa a fuskarta. Kafin ta dawo hayyacinta Dawood ya ƙara mata wani. Sannan kuma Bily dake zaune duk tana kallonsu ta hanata kuka. Dole Rabi ta haɗiye hawayenta sai ajiyar zuciya.
Dawood yace, “Inhar zakiyi mana ƙarya to zakiyita amsar irin waɗanan marukan babu ƙaƙƙautawa. Wa kikema aiki a gidan?”.
“Wlhy yallaɓai iya gaskiyata nake faɗa muku. Bani yima kowa aiki sai Hajiya Firdausi matar Sheikh Sooraj ɗin”.
Sai a yanzu Umar yay magana. “Eh ansan dama ita kikema aiki a zahiri. a baɗini kuma akwai ogarki mai sakaki shiryamata sharri ita da tilon ƴarta. Bayan ƙyautatawar data dinga miki a rayuwarki na tsahon shekaru goma sha takwas”.
Dawood ne ya sake fassara mata. Dan haka cikin rawar harshe da kuka mai cin rai tace, “Na rantse da ALLAH. wlhy tallahi ban taɓa cutar da Hajiya Firdausi da zuriyar ta ba. Ko Nu'aymah da muke yawan faɗa wani lokacin ina takalartane kawai wlhy saboda nasan bata barin saita kwana. Amma bada wata manufaba. Ko a mafarki bana fatan na cutar da waɗan nan bayin ALLAH ai balle a zahiri”.
Cike da ɗaurewar kai suka shiga kallon juna. Amma duk da haka bayan Dawood ya gama sanarma Omar abinda ta faɗa sai Umar ɗin ya bada vr ɗin nan na kwanaki da sukaji tare da Nu'aymah. Aka kuma tabbatar mata a wayar wanda aka samu.
“Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un ni Rabi. Wlhy wlhy kinji na rantse ni ban taɓa waya da mai aikin Nu'aymah ba. Hasalima sam ban santaba tunda randa akazo za'a wuce da ita abuja a sashen hajjo Umm taje ta sameta itama. Yanzu haka ko zaku kasheni bazan iya nuna fuskartaba balle harna samu Number ta nayi waya da ita akan Nu'aymah. To niko idan ta faɗamin halin da Aymah ke ciki gidan aurenta ribar mi zanci bayin ALLAH?”.
Tsawa little bee ta daka mata. “K bama son rainin hankali. Idan kince bake bace waɗan nan lambobin dake akan wayarki harda ta Uwaliya ɗin na uwar waye? Wa kuma ya sakasu da har zaiyi zaman magana da su a wayarki batare da kin saniba?”.
“Wlhy iya gaskiyata nake faɗa muku. Ni yanzu haka ko waya zanyi ma sai naba Muhammad ya dubamin lamba. Dan shine kemin sebi idan ko zansa lambar wani ɗan uwana. Idan kuma zanyi kira shima ke dubamin abinda ya samun dan banyi boko ba. Da Nu'aymah ko Adawiya kemin, to sai suyita jamin rai, shine na koma bama Muhammad ganin ya iya. Amma ni lambar ma ƴan gidan bata kowa gareniba wlhy”.
Hannu Dawood ya ɗaga zai ƙwaɗa mata mari Bily ta dakatar da shi. Dan ita duk shirun datai musu nazarin komi takeyi. sannan kuma Jay ma duk yana saurarensu daga office ɗinsa ta hanyar na'ura. Shinema yay saurin cema Bily ɗin kar Dawood ya mareta yanzun ta hanyar abibda ke a kunnenta da su basu fahimta ba.
Dakatawa kuwa Dawood yayi yana huci. Bily dake kallon Rabi cike da nazari tace, “To amma ranar da Nu'aymah tai bleeding ko zamu iya sanin miya faru? Dan bincikenmu ya nuna mana kece kika bata abu na ƙarshe tasha a gidan. Daga haka ta fara ciwon ciki sai jini kuma ya ɓalle”.
Shiru Rabi tayi tana tunani dan tama manta. Sai zuwa can kuma tace, “Lallai kuwa ranki ya daɗe kamar anyi hakan. Ta sakani na dafa mata ruwan shayi baƙi”.
“Kenan a ciki kika saka mata maganin zubda jini da aka ɗauka cikine ta zubar??”..............✍
*_Tofa masu karatu man kai na fa zai fara malalewa a dalilin amsoshin Rabi, nama rasa mizan tunano kuma. amma bari mu bita muji wace amsa zata bada a gaba??😱🤧._*
ZAFAFA BIYAR 2021
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻
TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[7/3, 3:48 PM] Queen Meenali👑: *_LITTAFIN nan na kuɗi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haƙura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaɗa mana🙏🏻_*.
No. 71
..............Saurin zaro ido waje Rabi tayi tana mai girgiza kanta. “Wlhy ba haka bane ranki ya daɗe. Mizaisa na aikata hakan ga Nu'Aymah. Bayan sikari da Lipton sai ruwan dana dafashi da shi ne kawai a ciki”.
Wani irin tafasa zuciyar Yoohan takeyi daga can, ji yake kamar ya ziro hannu ya shaƙo wuyan Rabi ta cikin system ɗin, sai dai babu dama.
Little bee zatai magana Bily ta dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu. “Inaga ku maidata inda aka ɗakkota tukkunna”.
Babu wanda ya iya cewa komai a cikinsu. Sai tasa ƙeyar Rabi da aka saka wani jami'i yay tana kuka aka maidata inda aka ɗakkota.
Bayan fitarsu ajiyar zuciya bily ta sauke tana rubuce-rubuce. Kusan mintuna biyu kafin ta ɗago ta kalli Yoohan da zuciya ta kume daga can. “I'm sorry Dear wannan case ɗin duk yanda kuke tunaninsa ya wuce haka. Akwai wani abu dana fahimta dangane da wnanan matar wanda sam na kula ku duk baku gansaba. Kodai ya kasance amfani akeyi da ita a gidan batare da ita kanta ta sani ba. Kokuma tana kan sani ta fi yarda ta shanye duk wata azabar data fuskanta anan danta rufama wancan asiri. Kokuma an mata gargaɗi mai girma da tsoratarwa akan sanarwa tun ba yanzuba.
Dole wannan wayar tata na buƙatar sabon bincike. Sannan waɗannan voice recording ɗin suma zamu sake bincike sosai a kansu, idanma har ba'ita ɗin bace zamu gano ainahin mai muryar insha ALLAHU”.
Dukansu sun fahimceta. Hakan yasa Yoohan tabbatar musu da shima zai shigo Nigeria zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu, kuma harda Nu'aymah. Dan ya fahimci lallai wasan na gaske ne.
_____________★★
Tunda ya shigo gidan yau taketa faman binsa da kallon mamaki. Dan tun randa ya dawo daga 9ja ta kasa gane kansa gaba ɗaya. Kullum yana cikin ƙunci da tunani, baya son yawan magana, sai su yini su tashi har dare magana sau biyar bata shiga tsakaninsa da shi ba. Tayi tambayar harta gaji tayi fushi ta ƙyalesa. Daga ƙarshe ma sai ya koma fita asibiti. Idan ya tafi tunda safe sai tayi barci zai dawo. Ta fahimci yana hakane duk dan karta cigaba da masa tambaya akan abinda ke damunsa. Dan idan ya fita yata yawan kiranta kenan wai yaji yaya take ita da Unborn ɗinsa.
Hakan data ƙara fahimtane ya sata sake tattare maganar damuwar tasa ta watsar gefe. to shinefa aɗan kwanaki ukun nan ya fara sakin jikinsa yana kuma dawowa gidan kafin tayi barci. Yau kuma abin mamaki sai gashi kusan ƙarfe uku ya shigo mata.
Yanda batai maganaba shima baiyiba. Sai dai kallonta yake cike da tausayawa a gareta. Tana zaune ne a kujera ta miƙe ƙafafunta bisa centre table ɗin falon. Sai filo ƙarami a cinyarta ta ɗora lap-top a kai tana sauraren lecture da akeyi daga can school ɗinsu.
A ɗan kwanki goma sha huɗu ɗin nan duk ta rame saboda damuwarsa da itama ke damunta. Hakan yasa cikin nata ɗan watanni bakwai sake fitowa sosai gamai kallo. Musamman yanzuma da take sanye da skirt na atanfa da t-shirt mai ƙarancin girma. Sai dai ta ɗara waɗanda take sawa a da kafin samuwar cikin da girmansa. plate ne a cinyar tata shima gab da cikinta ɗauke da green apples a kai, sai ɗaya dake a hannunta da ƙaramar wuƙa tana yanka tana ci a hankali.
Sassanyan numfashi ya sauke da lumshe idanu ya sake buɗewa a kanta. sai kuma ya shiga takowa har inda take dan ganin taƙi daina kallonsa. Gefenta ya zauna daf da ɗora hannunsa akan fuskarta ya juyar mata da kanta ta koma kallon lap-top ɗin.
Cike da sanyin murya yace, “K da kike ɗaukar Lecture miye na zubamin ido kuma?”.
Uffan batace masa ba, sai iska data furzar daga bakinta. Itama da sanyin muryar tace, “Lafiya naga ka dawo da wuri haka?”.
Ajiyar zuciya ya sauke a karo na biyu, ya dora kansa a kafaɗarta tare da kamo hannunta dake riƙe da yankan apple ɗin ya kai bakinsa. Bata musaba ta saka masa itama. Sai da ya tauna ya haɗiye yana kallon lecturer ɗin shima sannan yace, “thanks you Sweet girl” ya ƙare maganar da kaima kuncinta sumbata, ya kuma tura hannunsa a rigarta yana shafa cikinta cike da ƙwarewar likitanci.
Kamar koda yaushe kuwa sai ga cikin na motsi. Dan duk sanda zai masa irin wannan shafar sai kaji ya motsa. Har mita Aymah ke masa akan ita miyasa cikin baya mata haka sai idan yaso motsinsa da kansa yakeyi. Kokuma idan tanajin matsanancin yunwa nanma yana motsawa.
A hankali yace, “Sheikh ɗin Daddy ga daddy ya dawo gida. Ina fatan bakai fushi da canjawarsa ba?. kana kuma cikin ƙoshin lafiya zinarin zuciyata”.
Fuska Aymah taɗan taɓe tana ɗauke kanta ta maida ga lecture ɗin da sam yanzu ma ba fahinta takeba ita.
“Jealous ɗin ya motsane madam?”. Yoohan ya faɗa a cikin kunnenta cike da neman tsokana.
Hannu tasa ta ture nasa da zuba masa harara. “Tunda Jealous ɗin nakeyi mizai hana a ciremin na huta”. Gimtse murmushin dake neman kufce masa yayi yana taɓe baki da ɗage gira ɗaya sama. “Silly girl, ai idan kinga mun barki sai mun cika watanni tara da kwanaki tara ciff insha ALLAH. magajin Uncle na zuwa kuma wata ƙwallon zata kuma faɗawa rag.....”
Lap-top ɗin da take shirin saukewa a jikinta yay azamar riƙewa dan yasan sotake ta gudu. “Oh am sorry sweetheart wasa nake fa ni. Mu mun isa miki gadara bayan yanzu kece boss ɗin gidanma, kammu bisa wuya Mie-mie. Nifa namazo miki da wani albishirne mai daɗi”.
Batare data tanka masa ba ta sake yunƙurawa zata tashi. “ALLAH seriously Sweet girl”.
Ajiyar zuciya taɗan sauke kaɗan. Sai kuma ta kallesa, “To ka bari naje na kawo maka ruwa”.
“Okay harda abinci. dan yunwa nakeji”.
“Ai baka da kaso anan gidan malam”.
Tai maganar tana shigewa kitchen. Murmushi yayi mai faɗi daya jima ba'a gani a fuskarsaba. Ya jingina da kujera yana furzar da zazzfar iska. Shi kaɗai yasan mi yakeji a ransa. Yana daurewa ne kawai saboda fahimtar halin da yake ciki na ƙuntata ta itama. Shikuma bayason haka kodan yanayin da take ciki........
“Uhyimmm! An tafi tunanin ko?”.
Saurin dubanta yayi yana ƙoƙarin canja yanayin fuskarsa, Aymah da idanunta suka cika da ƙwalla ta ajiye tiren data ɗoro masa plate ɗin abinci da ruwa sai kofin lemo ɗaya. Saurin riƙota yayi ganin zata gudu. Ya ɗorata a cinyarsa duk da tanata ƙoƙarin ƙwace kanta ga hawayen sun fara sauka a kumatu da gudu. Matseta yay da ƙyau ya lumshe idanunsa, tun tanason ƙwatar jikinta harta haƙura tayi luf a jikinsa tana shashshekar kuka da sauke ajiyar zuciya.
“Am sorry Zeeynab. I'm very sorry. Nasan tabbas ina ƙuntata rayuwarki da laifin da banakiba. Nima bada son raina bane, ina cikin tashin hankaline mai tsananin ruɗani Nu'aymah.......”
“Shine ka zaɓi ka ɓoye min saboda ni banda matsayin sanin sirrinka? Amma ni har sirrin daya kasance na family ɗina mun baka dama ka shiga tsundum saboda baka darajarka, sai ni da.......”
“Shiii!!!. Wlhy bani da wani sirri a duniyar nan sai ke Nu'aymah. Da ana buɗe zuciya ma'abocin kallo yaga sirrin dake cikinta dana buɗe miki tawa kin gani Zeeynab. Da kinsan wacece ke a gareni da dukkanin tasirin da kikayi a rayuwata da bazaki taɓa yin tunani irin wannan ba. Amma kiyi haƙuri nasan da laifina. Laifina shine ɓoye miki damuwata. Bana ɓoye miki dan baki isa bane, na ɓoye miki ne saboda al'amarine mai girma a gareni. Ki tayani da addu'a ke dai kinji. Ki kuma cire komai a ranki, ki yarda ke ta dabbance ga mijinki. Bakiga duk yanda kika rameba, hakan na tayarmin da hankali.....”
“Yah Yoohan amma ai......”
“Oh my Cutie karkice komai Please. Yanzu dai mu ajiye wancan batun bashi da wani muhimmancin cigaba da hargitsa mana rayuwa da tunani ok?. Ina miki albishirin zuwa Nigeria gobe insha ALLAHU ”.
Duk da kewar ahalinta da ɗokin son zuwa garesu da takeyi sai taji kamar tafiyar bata lafiya bace, musamman da tasan yace itada 9ja ɗin sai ta shiga watan haihuwa lokacin sun sami hutun ƙarshen shekara da Christmas.......
“Tunani again baby?”.
Numfashi ta kawo tana kallonsa. Kallo irin na tambayoyin da baki ya gaza furtawa.
“To ko a fasa nayi tafiyata kawai ni kaɗai”.
Da sauri ta girgiza masa kanta alamar a'a. Ya ɗan murmusa da sumbatar laɓɓanta. “Karfa kisa komai a ranki surprise ne kawai”.
Duk da bata yarda da shiba haka ta shanye abinta a rai. Sai dai ta masa maganar karatunta yace babu damuwa ko suna a can zata cigaba da ɗaukar lectures ta online ɗin. Daga haka suka fara shiri a ranar, duk da daima bawani sun haɗa kaya bane dan bama zasu tafi da kayanba tunda akwaisu acan babu buƙatar hakan.
A dai ranar duk wani abu da zai iya lalacewa sun fitar da shi. Suka ɗan fita shopping na abinda zata iya buƙata saboda lalurarta. Ranta cike yake da ɗokin Isa ga ahalinta bayan rabuwa da su tsawon watanni tara. A gefe kuma cike take da fargabar sakamakon abinda zataje ta tarar.
*_WASHE GARI_*
Washe gari safiyar juma'a jirgin su Nu'aymah ya sauka a ƙasar haihuwarsu batare da kowa yasan da zuwan nasuba. Sai da taimakon Yoohan ta sakko a jirgin saboda ƙafafunta da sukai mata tsami da kumburi. Sai faman taɓe fuska take kamar zatai kuka. Shi kam dai ga tausayinta ga dariya na cinsa a rai. a zuciya ya ayyana, ‘Abufa yazo ga ma'iya’.
Bayan shigarsu texi taji yace a kaisu hotel. Ai babu shiri ta kallesa, “Hotel kuma Yah Yoohan? Gidan papa ɗin fa?”.
Cikin jin zafin dake taso masa a rai ya girgiza mata kansa. “Zamuje, amma yanzu muje ki huta ko?”.
Hankalinta tashe akan tunawa da hoton nan da sauri tace, “A'a ni dai gaskiya inba gidan papa ba sai dai ka sani a motar kano na wuce. Yaya gamu da gidan iyaye mu kama raɓe-raɓen hotel kamar wasu marasa galihu. Kayi haƙuri gaskiya ni dai bazanje hotel ba”.
Duk yanda yaso lallashinta akan suje hotel ɗin dan shi bayason zuwa gidansu. Ko sha'awar kallon fuskar Momy bayayi sam. Amma Nu'aymah ta tubure duk da bawai dan tanason zama gidan bane itama. Tana son sujene saboda hoton nan. Gara suje tun a yau ta ɗauka kafin papa ya farga suna ƙasar tunda ya bada kwangilar kasheta. Daga lokacin da matsaloli suka fara