Showing 36001 words to 39000 words out of 81012 words

Chapter 13 - KALBIM HAUSA NOVEL

MAMUGEE   

16 Sep 2025

199

siyo mata yana kallanta yace

"Yaya dai?
Jikin ne?
Mama kodai zamu tafi asibitin ne?

Cigaba da aikin abinci da maman keyi tayi tana cewa

"Eh nace mu tafin amma tace basai antafi ba
A bari zuwa anjiman idan bata dena jin yanayin ba sai mu tafin kawai"

Wayar Sayyid dince tafara ringing da sauri ya daga ganin Hamman ne yake kira.

Yana dauka kai cikeda girmamawa ya gaidasa yana cewa Ummitan ce batajin dadi.

Shiru ABDULAZIZ yayi batareda yace komaiba sbd yanda yaji a zuciyarsa a duk lokacinda akace Ummitah batajin dadi wani irin nauyi da daci yakeji ya cike zuciyarsa sbd ganin kaman ya gaza ne har akai mata auren wuri daya sakata a halinda take ciki wanda bata isaba yake gani kwata kwata hakama an sauya masa tsari da burinsa gaba daya akanta dan kuwa duk gwagwarmayarsa da nemansa akanta ne sbd ita ne,

Komai dayake son ya zama a rayuwarsa sbd Ummitah ne,
Sbd ya inganta rayuwarta ya hanata shiga quncin daya taso a cikinsa,
Sbd ya bata farin ciki da gatan da kowanne da zai samu amma a lokaci daya an sauya masa komai an lalata masa rayuwarta ta hanyarda baida zabi bayan karban hakan hannu bibbiyu dan hakan nema ya karbi Sayyid tareda alqawarin inganta rayuwarsa shima kamar qanin dasuka fito ciki daya.

Numfashi me sanyi ya sauke tareda bude baki a natse yace

"Ku shirya gaba dayanku yau komai dare zaa taho a tafi daku,
Karku bari Ummitah tayi komai hakama basai kun tafi asibitin ba,
Zanyi magana da Ummitah"

Da sauri Sayyid din ya bawa Ummitah waya ta amsa ahankali tareda dorawa a kunnanta ta ambaci sunansa ahankali cikeda kewarsa datake tsananin ji da buqatansa a kusa da ita.

Jin sautin muryanta cikin sanyi daya sauka a kunnensa ya sanyasa miqewa ahankali daga inda yake zaune ya nufi bakin window din dakin ya tsaya yana sauke numfashi mara sauti zuciyarsa na sake daukan wani irin nauyi da dacin rashin kasancewansa a kusa da ita a daidai yanzu datake tsananin buqatansa.

"Ummitah" ya ambaci sunata ahankali cikeda nutsuwa da sautinda ita kadai yakewa magana ahakan sbd matsayinta rayuwarsa gaba daya daban yake da komai.

Hawayene masu dumi suka gangaro mata ta rintse idanuwanta kuka mara sauti na zuwar mata a karo na farko tace masa

"Hammah inason ka dawo dan Allah,
Hammah inason na haihu a hannunka kaman yanda aka haifeni a hannunka,
Hammah ka.......

Kasa qarasawa tayi sbd hawayen da suka tsananta mata gudu haka kawai buqatansa take a kusa da ita sbd ita kadai tasan yanda take jin cikin jikinta.

Mama da sayyid shiru sukai jikinsu na sanyi batareda kowannensu ya iya cewa komaiba saima tsinkewa da mama tayi tana ajiye aikin datakeyi batareda ta juya ta kallesu ba.

Acan bangaren shiru yayi tareda kasa cewa komai dan duk abinda zai samu a aikin daya kawosa ko shine zai qarasa sauya rayuwarsa to tabbas saiya bar qasar ya koma gida a goben nan.

Kasa cewa komai yayi ya kashe wayar bayan yace mata ok kawai dan babu me basa umarni yace ok ko yes kawai sai buqatan Ummitah kadai kaf rayuwarsa kuwa a yanzu.

Yana kashe wayar kai tsaye ticket ya kira aka siya masa ya shirya komawa gida.

Yana gamawa wayar Alh saad ya kira ya sanar dashi a samar masa driver yaje ayau din koman dare ya dauko su Ummitah shima gobe insha Allah zai dawo.

Ummitah kuwa tana miqawa Sayyid wayarsa kasa dagowa tayi ta kalli kowannensu sbd sosai takejin jikinta ba dadi.

Sayyid da maman ma jin sukai hankalinma yafi karkata ga tafiyar sbd jikin Ummitan dan haka ba wani bata lokaci suka fara bankwana da mutane shima sayyid din gida ya koma gurin iyayensa tareda Ummitah duk da batajin dadi amma hakan ya lallaba suka tafi sukai bankwana sosai kowa na tausayawa Ummitan sbd duk ta sauya ta fara kumbura sosai irin na masu cikin daya fara tsufa.

Duka kayansu Mama kyauta tayi dasu tin daga kayan sakawa har kayan amfani da komai,

Sayyid ma kusan komai nasa kyautarwa yayi sutaransa kawai ya bari suma basu fi kala biyu ba ya bari.

Ummitah kwata kwata bata cikin walwala sbd yanayinta dan haka sayyid da mama suka matsu driver ya iso su tafi sbd akai Ummitan asibiti.

Karfe uku na yamma driver ya iso da lafiyayyar motar ABDULAZIZ din aka daukesu daga garin gaba daya bayan sun rabu da yan uwa da abokan arziki ana kukan rabuwa na tafiyar da baa san ranar haduwa ba.

Sayyid Mahaifinsa har cikin ransa yakejin sanyin jikin rabuwa dansa namiji daya tal sedai kaman yanda ABDULAZIZ yayi masa alkawarin Sayyid zai zama abin alfaharinsa kuma har abada ya riga ya zama yaya kuma dan uwan Sayyid din ya saka yakejin damuwarsa bin iska.

Mama ma tayi kukan rabuwa da yan uwanta duk da batada uwa da uba a garin amma tanajin radadin rabuwa dasu.

Ummitah kuwa nauyi kirjinta yayi mata bata iya ko kukan ba sai jajir da idanuwanta sukai mata tanajin ita kam kamar har abada bazata taba dawowa ba ta tafi kenan,

Wani nauyin ta sake jin ya danne kirjinta ta dafe kirjinta ahankali tana zubawa mutanen dake musu bankwana a tsaye ido tana rasa tinanin yi.

Rufe musu kofar mota akai ta zubawa kofar gidansu idanuwanta da suke sake yin ja...

Ahankali aka tada motar aka tafiya ahankali sai alokacin taji wasu irin hawayen da batasan dasuva suna gangarowa akan fuskanta ta rintse idanuwanta ahankali tana dora hannunta akan cikinta dake motsawa da karfi.

Shiru sukai babu motsin komai a motar sai sanyin ac dayake ratsasu babu wansa zuciyarsa batai nauyiba sbd Allah ne kadai yasan rayuwar datake gaba tana jiransu.

Tafiya sukeyi sosai da gudu akan titi da lafiyayyar motar da basa jin iskar komai bare kuka karfe ko jijjigar karfe sbd lafiyar motar da tsadarta.



Qarfe 11 dare suka isa Abuja kai tsaye gidan ABDULAZIZ din aka nufa dasu wanda yake a tsare kaman bana ABDULAZIZ dinsu da suka saniba,

Dayake dukkaninsu suna cikin sanyin jiki da damuwar rabuwa da gida basu tsaya kalle kalle sosai ba Matar Alhaji Saad Anty Maryam taxo ta kawo musu mai aikin da aka tanadar musu tareda abincin da zasu ci lafiyayye sai dakunan dasuke na kowannensu da aka nuna musu.

Dakin Ummitah shine a can daban palonsa kusa da nasa Master bedroom din
Sai dakin Mama dayake dayan palon shima babba lafiyayye dana mai aiki a kusa da nata sai Dakin Sayyid lafiyayye babba da shima yake palon tareda lafiyayyen toilet aciki.

A cikin gidan babu wanda dakinsa baa zuba masa komai na jin dadi da tsarin masu kudi ba.

Sallolin dayake kansu suka fara yi kafin sukaci abinci ba bata lokaci bacci ya dauke kowannensu har Ummitah dake fama da jikinta gajiya ta sakata baccin dole ciwon na tafiyarsa.

Washe gari me aikin gidan ce Fiddausi ta tayardasu sallah dukkaninsu sbd gajiya da sanyin ac ya sakasu wani irin nannauyan bacci.

Suna gama sallah babu wanda ya fito duk da Ummitah tana dakin mama a tare suka kwana sbd sabo.

Karfe 9 na safe Fiddausi ta gama komai na breakfast da gyaran gidan taje ta sanar musu suka fito cin abinci.

Fiddausi ta kaisu har dining ta nuna musu su zauna suka zauna suna kallan gurin dayake kaman wani shagon saida gilasai da qwan lantarki sbd haske da katon madubin console dayake kallansu a gurin.

Ba wani abincin da bazasu iya ci bane doya ce da egg sauce sai Pepper meat da kunun gyada dayaji madara.

Ummitah ce kuzarinsu da yanayinsu dan haka ganin ta samu warwarewa tana cin abincin ya sakasu sakewa suma sukaci abincin cikin jin dadi da mamakin arzikin da ABDULAZIZ din yake rayuwa a cikinsa duk da bai ragesu da komaiba shiyasa basa cikin yunwa sa kwadayi ko kadan daman can.

Suna gamawa Anty maryam na isowa gidan daukesa kayan sakawarsu da aka tanada tin kafin zuwansu.

Sayyid ne kadai babu kayansa se ta saka haydar danta ya daukesa ya fita dashi dan siyyyar nasa kayan.

Ummitah ta kalla cikeda kulawa da tattalinta sbd sanin wacece Ummitah a rayuwar ABDULAZIZ yasa duk wanda yake kaunarsa to tabbas saiya kaunaci Ummitah ma sosai.

Sannu tai mata tareda wuni a gidan tana nuna musu komai tareda debe musu kewa tinda bayanan ABDULAZIZ din.

Ko aranar ABDULAZIZ bai samu isowaba dan haka dole anty maryam ta taho gidan da yaranta duka suka sake yiwa su Ummitan wuni suna debe musu kewa tareda kokarin ganin sun sake batareda nuna qyamar ganinsu yan kauye ba.

Cikin jikin Ummitah ya saka Anty maryam ringa nuna mata wata irin kauna sosai da kulawa dan hakan ne ma mama taji tana samun nutsuwa da sakewa dasu.
#MAMUH


ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
mamuhgee

A DUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo

Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi

Shedan biya
09033181070

Or mtn vtu at
09032345899
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
20/21
*ZUZEAM VENTURES*
Best APHRODISIAC
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah >?p?=?L? Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k>?m? Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 3800
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
=????=????=????=????=????=???? ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA=؃?


*************
A cikin qananin lokaci suka ji suna samun nutsuwa da iyalan Alh saad wanda shima ya shigo sun gaisa har so biyu ya kuma cewa anty maryam da kanta takai Ummitah asibitin taga doctor kafin dawowan ABDULAZIZ.

Da safe suke shirin Anty maryam din tazo suje asibiti dan haka a ranar a dakin mijinta ta kwana sbd Shine zai tasheta tinda asuba sufara shiri bare kuma daman Ummitan da kanta ta tafiyarta gurinsa itama mama bata hanaba tinda kila idan ABDULAZIZ din ya dawo bazai barsu guri daya ba sai Ummitah ta haihu ta koma masa yanda yake ganin ya kamata ta koman.

Irin tsananin Asalin son da Sayyid kewa Ummitah kusan a duniyarta ABDULAZIZ ne kadai nasa ya fi nasa sbd So me tsaftar dayake mata daga Allah ne shi ya halitta masa shi a zuciyarsa,

Kwana yayi a zaune yana kulawa da ita tareda tarairayanta yana jin kaman ya rabata da cikin jikinta taji sauki hakama shi kansa ya shirya bazata sake haihuwa yanzu ba tinda ciwo da wahala cikin yake sata hakama yana tsoron wani abin ya sameta koda agurin haihuwa ne bare ya sani ko Hammanta ABDULAZIZ bazai bari ta sake haihuwa anan kusa ba idanma bai rabasu ba akan sai sun gama karatun dayace zasuyi.

Karfe tara suka fito a shirye tsaf suka nufi dakin mama wadda tinda ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????tai asuba bata koma ba tana zaune tana jiran lokacin zuwan nasu asibitin yayi.

Dining suka nufa wanda suka ga ancika sa sosai ayau din fiyeda kullum hakama abincin dayake kai a yau an samu sauyinsa.

Mama ce ta zauna Sayyid kuwa Ummitah yake kokarin taimakawa ta zauna
Ahankali wani irin qamshi me sanyi ya fara shiga hancinsu mai nutsuwa,

Ahankali Ummitah ta dakata daga zaunawan da zatai tana dago fararen idanuwanta dasuke sak da nasa ta waiwayo cikin sanyi hancinta da gurin suna sake gauraya da qamshinsa.

Sayyid ma qamshin ya sanyasa sakin hannun Ummitan Ahankali yana juyowa sbd Tin ranar farkon haduwarsa da Hamman ya riqe qamshinsa sbd Kaunarsa da Allah ya dasa masa arai shima sbd Ummitah.

Inda suke kalla Mama ta juya ta kalla taga mene sbd ita hankalinta da hancinta basu wani bata tinanin qamshinba.

Daidai lokacin ya sako kai a natse cikin wani irin kwarjinin daya saka Sayyid sauke kansa cikeda girmamawa yana kasa qure kallansa akansa sbd ba kwarjininsa kadaiba hatta hasken fatarsa datake wani irin shining na hutu da kwanciyar hankali tareda daula datake samu ya saka kyansa yin yawa.

Ummitah ce ta qure kallanta akansa tana jin dukkanin jikinta na mutuwa wani sanyi yana sauka zuciyarta yana mamayewa,

Batada abinda yafi mata dadin kallo a rayuwarta sama da kallansa a gabanta,

Kyansa da asalin kammminsu dasuke iri daya amma shi ya sauya gaba daya komai nasa daban yake da nata sbd rayuwar da inda suke rayuwar ba dayaba,
Hasken idanuwansa zuwa dogon hancinsa ta kalla tana rokon Allah ya basa tsari da kariya daga dukkan sharrin kowace mace a duniya.

Shima ita yake kallan cikeda wata irin kewanta dake cinsa kaman cikin kansa zai kunce dan haka yana isowa hannunsa duka biyu ya bude ya rungumeta yana karanta mata adduoin tsari da kariya itada abinda yake cikinta kafin ya saketa ya saki wani Kyakkyawan murmushin daya saka sayyid kasa dena kallansa da tattausan sauti yace

"Sorry Ummitah ABDULAZIZ,
Yaya,ya jikinki?

Kafin ta amsa gurin mama ya juyo cikin kulawa da sakewa da girmamawa yace

"Barka da safiya Mama,
Yaya fama da sauyin guri?
Na sameku lfy??

Murmushin farin cikin ganinsa tayi tana cewa

"Duk lafiya kalau
Sauyin guri kuma ai munata kokarin sabawa,
Tafiyar dare kayi kenan?

Zaunawa yayi Ahankali yana cewa

"A cikin dare na iso sai ban tasheku ba tinda kun riga kuna hutawa"

Sayyid ma zaunawa yayi yana cewa

"Barka da dawowa"

Kallansa yayi cikin kulawa da sakar masa fuska sbd ya sake yace

"Thank you,yaya kaima kanata fama da kadaici right?

Gyada kai Sayyid yayi yana kokarin sakewa da hamman.

Ummitah na gefensa fuskanta cikeda da murmushi me kyau da nutsuwar data kwana biyu bata iyawa sbd yanayinta.

Breakfast suka fara cikin kokarin sakewa dasu dukkaninsu sbd sayyid ya sake dashi tinda tsakaninsa da mama da Ummitah babu wani kamewa ko rashin sakewa.

Bazai taba tina yaushe Zuciyarsa ta samu asalin farin ciki irin wanda yake cikinsa a yanzuba sbd kasancewarsa dawowa rayuwa a guri daya da Ummitah wadda babu ranarda zasu sake rabuwar gurin rayuwa daban daban har abada sedai rabuwar kwanaki na tafiya dayake yawan yi sun hadu kenan sai mutuwa insha Allah,

Kallan Sayyid dake cin abinci yayi a natse yana kallan Ummitah yaji zuciyarsa na sake karban Sayyid din cikeda Kauna sbd Aurensa dayake kan Ummitah bazai rabasa da ita ba tinda shi kansa mahaifinsa a hannunsa ya basa amanarsa kuma ya karba har Abada insha Allah.

Yanzu ne yakejin Nutsuwa da godewa Allah da hakan dan Sayyid dinne kadai Ummitah zata aura suci gaba da zama a taredashi,

Ahankali ya bude bakinsa cikin sauti me nutsuwa da rashin sauti yace

"Thank you Sayyid"

Kallansa sukai dukkaninsu dukda ba sauti yayi maganar cikin turancinsa dayake kashe Sayyid.

Mama ce kadai da batasan wani thank you ba bata kallesa ba.

Bai wani ci abincin ba hankalinsa na kan Ummitah wadda ita kuma idan yana tareda ita take cin abincin dama bata saba cin ba sbd jin take komai nata ya bude.

Mama tasan daman indai yana tareda Ummitah ba wani abincin kirki yake ci ba dan haka bayan Ummitan ta gama sai ta kallesa cikin kulawa tace shima yaci abincin.

Tea da chips mara maiqo yaci yana gamawa gaba dayansu suka miqe suka bar dining din.

A shirye yake sbd yasan da kai Ummitah asibitin dan haka ma ya fito da wuri da sai yakai guraren 11 bai fitoba.

Key din mota da wayarsa ya fito dasu a hannunsa sai tsadaddiyar Hular fcap ta fendi daya sako ya fito.

Daga shi sai Ummitah din suka fita sai sayyid mama a gida suka barta yace ta koma bacci ta huta.

Shine yake driving a hankali Sayyid na zaune a gaba sai Ummitah din dake baya tana kallan garin cikeda shaawa da burgewa.

Sayyid dayake yana fitowa sosai suna tafiya gurare daman can sai baya wani kalle kalle sosai sbd ya saba ganin ire iren hakan.

Wani babban private clinic me tsada sosai yakaita suna isa babu wani jira ko bata time a asibitin sbd kyanta akai mata registern Prenatal visit da zata ringa zuwa.

Wani Dr Ken ne ya dubata dakyau cikeda kulawa ganin Yanda ABDULAZIZ sam tsananin kaunarsa akanta bata boyuwa duk da bai saniba ko shine mijinta ko yayanta koma waye a gunta kaunarsa a bayyane take.

Scanning akai mata bayan angama diban jininta da sauran samples na aune aune da zaa mata.

Cikin kulawa da sake fuska sosai yana tayasu murna ya kalli ABDULAZIZ daya dawo dakin bayan angama Scanning din yace

"Congratulations Sir its a baby girl"

Kallan Tvn yayi Ahankali kafin ya dawo da kallansa kan Ummitan da itama shi ta kalla suka kalli Sayyid a tare wanda farin cikinsa shima yake a fili sedai a duk lokacinda ABDULAZIZ yake kusa baya zaqewa akan Ummitah dama cikinsa dayake jikinta sbd kawaici da nauyin ABDULAZIZ din.

"Thank you dr" Yafada yana karban result din suka fito yana rasa yanayin dayake ji a zuciyarsa duk da abu daya ya sani shine kome Ummitah zata haifa ya fito a cikinta,jininta zai kaunacesa kaman yanda yake tsananin kaunarta.

Sun dade a asibitin sbd formalities din da daukan time da kuma aune aunen,

Suna baro asibitin kai tsaye shopping mall ya biya dasu aka siya fruits masu yawan gaske suka wuto gida sbd bayason yayi yawo da Ummitan dan yanayinta.

Suna isowa gida barwa Sayyid ita yayi ya wuce bangarensa dan Amsa waya da kuma fitowa sallah dan time yayi na laasar sunyi azahar already acan.

Dakin Mama suka nufa sayyid da Ummitan.

Zaunawa tayi gefen mama tana dan kwantawa jikin maman tana cewa

"Mama harna dan gaji"

Murmushi mama tayi tana shafa fuskanta da kulawa tace

"Ummitan Mama Allah dai ya nunamun kin haihu lafiya dan ki samu hutawa kema"

Murmushi tayi tana dafa cikin sbd motsawa da yayi tana cewa

"Amin Mamana"

Sayyid zainawa yayi yana fadawa maman duk abinda akai dama abinda dr yace cewan mace ce

"Kai jamaa har yasan abinda zaa haifa kenan shi likitan"

Dariya sayyid

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login