Showing 57001 words to 60000 words out of 81012 words

Chapter 20 - KALBIM HAUSA NOVEL

MAMUGEE   

16 Sep 2025

194

Tsimin mangoro 1k>?m? Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 3800
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
=????=????=????=????=????=???? ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA=؃?


*************
Baby Fatima ce ta zamo sabuwar hasken idaniyar data farfado da rayuwarsa daga mutuwar datake wadda baitaba fatar ya tashi ba,
Fatarsa Allah ya dauki rayuwarsa batareda ya warke ba sedai a duk lokacinda ya kalli Fuskan babyn data dauko kamminsa da mamanta fuskan Ummitah yake gani a cikin tata dan haka ta zama hasken zuciya da rayuwarsa da bazai iya ba dan haka tinda tasa kaddarar ahakan tazo itama zai reneta kamar mahaifiyarta ya inganta rayuwarta ya bata gatan da tarbiyar da zata rage masa filin da Ummitah tabar masa dan har abada wannan filin bazai taba cikewaba harya bar duniya sbd Ummitah itace rabin ABDULAZIZ AYOUB LIMBA kuma ta tafi dan haka ta tafi da dukkanin emotions da feelings nasa babu abinda ya rage masa bayan fili a zuciya.


Lokaci na tafiya lafiya tana samuwa garesa amma duk wannan lokacin bai taba bude bakinsa yayi magana suma tin suna jiran maganarsa har suka hakura suna fatar samun lafiyansa tukuna.

A ranar daya fara karban baby fatima da hannuwansa biyu a ranar ne ya bude bakinsa ya fasa wani irin kuka mara sautin daya girgiza mama da sayyid suka shiga tashin hankali gidan yayi tsit a ranar babu wanda ko ruwan gidan yasha da dadin zuciya daci da qunci ne ya cike koina na cikin gidan har dare bai fitoba.

Ranar a gurinsa Baby fatiman ta kwana wadda itama tafara sabo dashi dan bataima wayon sanin waye babanta a tsakaninsu ba duk da Sayyid ya sadaukar nuna mata yakeyi ABDULAZIZ dinne mahaifinta tinda tafara wayo da girma sbd shekara biyu cikin ta uku ake magana.


******Sayyid da rayuwarsa sun sauya sosai acikin shekarun sbd dawainiya da zamowa kaman shine shugaba a familyn yanzu hakama ga huldodin ABDULAZIZ da abokan aikinsa suke tafiyar dasu sosai shine mai bibiyarsu tin bai sababa harya saba ga karatunsa dayake masa wuya sbd rashin qarfin turancinsa ahaka yayita fama harya tsayu ya zama dan qasa ya goge ya wanke ya koma SAYD yanda suke kiransa,

Mama ta dade da dawowa hayyacinta sbd ganin zasu rasa ABDULAZIZ dan haka ta miqe tsaye sukai gwagwarmaya harya dawo kan kafafunsa y dawo ABDULAZIZ wanda ya tashi daga wanda suka sani,

Tinda ya warke bai taba bude bakinsa yai maganar rasuwar Ummitah ba suma sbd gudun janyo masa wani radadin dayake kokarin boyesa aransa yasa basu tada maganar komaiba sbd tin yana ciwo Sayyid yasha fada masa yanda ta rasu da inda take a rufe da janazah da akai da komai.

Bai fara fita aiki ba bare yawon business a gida yake aikinsa da laptop irinsu conference calls da meetings da sauransu.


Jinyarsa bata saka arzikinsa baya ba sbd babu abinda ya tsaya a ciwonsa cigaba akai da business kawai dan haka arzikin yanzu yake take na bayan dan haka yafara kokarin fitowa karban ragamar komai tareda sayyid daya goge a harkan business da computer daya yiwa karatun qurulla sbd kusan maye ne shi akan duk abinda ya sakawa ran sani dan haka yake kamar wani maye akan karatunsa da aikin da duk ya shafi ABDULAZIZ LIMBA.


**FALAQ AZIZ LIMBA shine Sunan dayake kiran 'yarsa yar kamannin shekara 6 zuwa 7 wadda ta taso cikin gatan daya wuce misali hakama batasan tanada wani ubanba a duniya kaf bayan Daddyn nata wanda take cewa BESTDADDY,

***Sayd ya zama cikakken matashin dayake ji da Ilimi da tsari tareda da Zama final say din AZIZ AY LIMBA sbd zamansa personal person dinsa.,

A lokacinda baby Falak ta cika shekara bakwai a lokacin suka bar italy suka koma United States Sbd sabuwar duniyar datazowa ABDULAZIZ LIMBA ta wani irin kudin dayake tashensu wanda yake zamowa abokin manyan mutane dake ruling qasashe masu powers da iko,

Sayd sake kutsawa yayi a cikin karatun dayake sake sauya rayuwarsa gabaki daya yana komawa kaman black American,

Mama ma rayuwarta haka ta koma kamar batai zaman Nigeria ba dan hutu da kwanciyar hankali ya ratsata tareda da wata irin daula da asalin abinda ake cewa arziki.

Falak itace abu daya da duk duniyar the great AZIZ AY LIMBA baya wasa da lamarinta dan kuwa ko yawan tafiye tafiyensa ita kadaice takeda iko da damar kiransa aduk lokacinda taga dama koda yana tareda mutane masu mahimmanci baya qin daga wayarta gashi sam bata taba normal call dashi ba idan ba vidcall ba dan haka kusan duk abokan businesses nasa sunsan baida kamar 'yarsa tal kuma sun san baya hadata da komai.

Kaf duniyarsa idan ba daidaiku Nigeria ba basu taba sanin ba shine asalin mahaifinta ba kaman yanda itama bata saniba saninta Sayd Uncle nata ne dayake tsananin sonta shima hakama itama tana tsananin sonsa.

Babu aure a gabansa dan bai taba tinaninsa ba bare kallan macen ma da zai iya auren duk da yayan manyan anyita son hada family dashi hakama abokan businesses nasa sunata son hada family dashi sedai bai shirya hakanba kwata kwata,babu tsarin hakan a rayuwarsa 'yarsa ta ishesa rayuwara.



***********
Shekarun da suka wuce da yawa ba iya Familyn LIMBA suka sauyaba da samun sabuwar rayuwar har mutane da yawa da duniyarma kanta abubuwan suna sauyawane da tafiyar kwanaki zuwa shekaru,

Yara qananu sun girma sun zama yan mata,wainda baa haifaba ma an haifa,wainda basuyi aureba sunyi sun hayayyafa,
Wasu sun samu ci gaba wasu sun samu ci baya,
Wasu sun bar duniyar ma hakama wasu suna nan yanda suke saidai tsufa dayake zuwa kaman yanda damuna da rani suke tahowa suna wuce komai ya sauya a koina na rayuwar da duniyar.


JANNAH ZAD ta samu sauyin rayuwar datake cike tattare da cigaba daya zarce na komai a rayuwarta ta baya data zama tarihi gareta da duk ahalinta,

Iyayenta sun turata qasar datake burin karatu ta samo ilimin da ciwo ya hanata samu,
Rayuwarta tana cikin haske da cigaba tareda kwanciyar hankali da walwalwa me tarin yawa musamman sbd tana tareda Ammar dinta wanda yake tamkar kariya agareta sbd checkups nata da baya wasa dasu sbd rayuwarta zata qarasate ne akan checkups da baa denawa lokaci lokaci,

Rayuwarta ta sauya,kamanni da halaye da jiki da dabiu da komai nata ya sauya daga Zeynab zuwa beautiful classy Jannah Zad wadda take tashen Kyan jiki da fuska dana zuciyarta data banbanta sosai data ahalinta,

Akwai kauna mai karfi da tsafta datake ji a tsakaninta da zuciyar datake bugawa a kirjinta wanda lokuta da dama takanji kadaici yana tsananin rufeta da kewan mai zuciyar wanda haryanzu batasan waye ya bata ba kuma waye familyn sbd su Dad kwata kwata sun sanar da ita wanda ya bata najimi ne kuma bama a Nigeria yake ba baida kowa maraya ne daga ghana aka samo.

Da wannan aka hanata neman koda familynsa ne sedai tanajin akwai kauna sosai tsakaninta dashi wanda ko sunansa bata saniba amma babu ranar da bata masa adduar samun rahamar ubangiji a makwancinsa.

Ammar Zad shine wanda zuciyarta take tsananin so bayan iyayenta da kuma kauna ta yan uwanta So ne mai karfi a tsakaninsu.

Ammar son dayake mata ya take wanda take masa sedai yana samun kansa a cikin matsanancin rudani da yawan lokuta sbd Soyayyar datake masa tafi kama data jini hakama hakanan yake jin koyaushe kaman bata gama zama tasa ba a zuciyarta da kwata kwata basa gane wane irin so takewa abu,

Amma dai ko yayane tinda tana son nasa bayada burin daya wuce hakan aure kuma basa buqatan rushing abubuwa sbd a yanzu ta samu cikakkiyar lafiya samun iliminta shine komai zatai karatu ta zama cikakkiyar macenta a yanda take yanzu kafin komai.

Familynta na cikin farin ciki da walwalwan dayafi na baya sbd samun lafiyarta komai ya daidaita a familyn Suna komai na businesses nasu cikin cigaba da samun daukaka da kwanciyar hankali,

Basu bar Nigeria ba tinda suka dawo sedai Dr Abraham dasuka koma qasarsu duk da sun sabu da Nigeria din amma suna yawa zuwa inda sbd har koyaushe dr Abraham ya riga ya zama kamar shine me asibitin amma zadeens kuwa kwata kwata zuwa asibitin ya zama shafaffen tarihi garesu tin daga lokacin dan ko ciwo dayansu yayi gida doctors ke zuwa dubasu.


Duk wanda yasan zaadens yasan zaratan Mazan dake familyn masu ji da lokaci da aji tareda tsagwaron ilimi da aji,

MAHEER ZAD ya zama kamar babban mutum dayake hulda acikim manyan mutanen dasuka haifes a matsayin abokan business dan duk abokan business din iyayensa Sun zama nasa abokan dashi ake huldan da duk zaa iya yi da Dad dinsa ko Daddy mahmoud dan haka matsayinsa da Karfinsa yayi girman da girmamawan da ake bawa iyayensa ita ake basa a gurin mutane da abokan business,

A gida kuwa Matarsa ta samu duk duniyar datake mafarki da burin samu harma ta wuce dan kuwa rayuwar iko da daular da bata jin barna take dan haka ta zama cikakkiyar Zad itama daman a zuciya ma daya suke.


AMMAR ZAD kuwa rayuwa biyu yake juyawa ta zamansa Zad da zamansa likata me zaman kansa da duniya bata saniba amma dai businesses din iyayensu shima yake ciki sosai,

Duk wani lissafin tarin kadarori da uban dukiyar da suke da ita shine yake gudanar da komai sai bangare daya bai cika zama ba yana hanyar zuwa gurin Jannah wadda take Cyprus tana karatu tareda a gidan Daddy mahmoud wanda yake jiran ta gama shima su tattaro su dawo Nigeria gaba dayansu.

Ammar kusan yafi su Maheer kyau da daukan ido sbd Mum dinsa ya dauko gaba daya wadda tafi yayunta kyau duk da kusan duk kamanninsu daya dan haka Jannah take ganin a idonta babu wanda zai kai Ammar Zad dinta kyau da aji da kamewa dan bata taba sanin yanada trauma ba duk wannan abin da ake sbd idan ta taso masa sam bayada kyan gani.

Amma koda ta sanin a yanda yake a ranta zata iya sonsa a hakan batareda wani second tinani ba...

SALEEM ZAD shine me zafin cikinsu da baya cika shiga zabgar family business din yanada nasa business na kamfanin saida motocinsa daya bude wanda yake gudanarwa amma dai duka da sunan familyn ne wanda daima kamar family business dinne ya bude musu sabo kuma hakan yana tafiya fiyeda tsammaninsu dan haka sukai investing mugayen kudi akan business din kamfanin motocin sedai Akwai wani shegen daya zarce tinaninsu akan business din na motocin wanda Saleem Zad ke tsananin burin aiki dashi sedai hakan ya kasa samuwa amma yana kokari akan hakan.


Mimi Zad kuwa hankalinta kwance yake tinda ahalinta suna cikin Aminci da kwanciyar hankali kowa na samun yanda yake so dan haka ita hakan shine farin ciki da burinta sai kuma Auren Ammar da Jannah datake fatan Allah ya nuna musu anyi sbd hakanan takejin batada Nutsuwa idan baai aurenba kaman bazaayi ba take gani wanda tasan Ammar na rasa Jannah komai zai iya faruwa dashi sbd son dayake mata ya hadu da trauman datake damunsa ya zama kamar possession.

DZAD da DADDY MAHMOUD kuwa duniya tayi musu duk yanda sukeso sbd suna juya rayuwa yanda suke sonta,

Allah ya basu power da duk abinda suke so a rayuwar dan haka basuda matsalar komai sai rayuwa yanda sukeso suda iyalansu.
##MAMUH
#JANNAH ZAD
#AY LIMBA
#AMMAR ZAD
#FALAQ LIMBA
#SAYD LIMBA
#ZAADENS


ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
mamuhgee

A DUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo

Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi

Shedan biya
09033181070

Or mtn vtu at
09032345899
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
31
*ZUZEAM VENTURES*
Best APHRODISIAC
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci? cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah >?p?=?L? Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k>?m? Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 3800
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
=????=????=????=????=????=???? ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA? NEW PROMO YA KAMMALA=؃?

**********
December 2024
Starling City US
Fresgills No 124 LIMBAs Res

F??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????iddausi ce ta fito daga kitchen dauke da glass bowl me dan girma a hannunta ta nufi dining room tana dan kallan time na agogon dayake hannunta ta kalli hanyar dakin Falaq dayake hanya daya da dakin Daddynta Dayake gari dan hakan ne ya saka gidan yau ba doguwar hayaniya gurin aiki sbd matiqar yana nan hutun gaske yake buqata Sayd yasha fada musu doka ce ba wai kaida ba dole ne ayi maintaining kai.

Dining ta shirya tsaf wanda yakeda girma ta gama jera duk wani abinda tasan Sir AZIZ AY LIMBA yana ci a breakfast dinsa dana falaq wadda gata yayiwa wani irin kamu kwata kwata,
Sai kuma abinda Sayd shima yake cimarsa Mama kuwa yawanci breakfast dinta kome zata ci batada damuwa amma sai an hada mata da kunun Gyada dayake kamarma na madara zalla.

Tana gama shirya Dining ta koma kitchen ta kalli sauran masu aikin biyu ta tinatar dasu nan da awa biyu zaa fara shirin abincin lunch na gidan duk da sun tsani sbd sun dauki shekaru a gidan suna aiki amma kaidarta ne ita kuma tina musu koyaushe sbd a yanzu ta yawanci umarni ne nata sai kulawa da Falaq wadda yake asalin aikinta me mahimmanci kenan.

Fitowa tai daga kitchen din ta nufo lafiyayyan palon gidan dayake tashin wani lafiyayyan qamshi me hade da sanyin aircon daya kama koina,

Dukiya ce take magana koina a gidan sbd luxuries ne koina na waiga a gidan yake magana da class tareda rashin hayaniya da kwanciyar hankali.

Hanyar dakin Mama tafara nufa ta bude palonta ta shiga shima qamshi ne da sanyin ac ke tashi me dadi yana sanyaya jiki da zuciya.

Kai tsaye Bedroom dinta ta nufa tana sake duba ogogonta sbd lokacin tashin Falaq datake jira sbd yau weekend ne ba school amma zata tafi school campaign da zaayi na yara dan haka tasan saita lura sosai batareda ta qara ko wuce time da zaiyi daidai da fitowar daddynta ba.

Ahankali cikin nutsuwa ta miqa hannunta tai knocking kofar bedroom din kafin ta bude tareda sallama a bakinta ta shiga tana kallan Mama dake zaune tana waya sanyeda doguwar rigar kuwait me kauri sosai da hula tana waya da Baba Alhassan dayaje Umrah sbd bayajin dadi sosai manyanci yafara masa yawa sosai.

Cikin sakewa dake hade da girmamawa tace

"Mama ina kwana?
Barka da tashi.

Gyada kai maman tayi tana cigaba da waya da hannu ta nuna mata tarkacen kayan Falaq data bar mata a dakin hadda Ipad dinta da tana tashi bata ganta ba zata iya daga musu hankali azo ana bata lokaci gurin lallabata kafin fitarta.

Tattara kayan Fiddausi ta fara tana dariya da cewa

"Mama mutuniyarki ce kike cewa a tattara miki kayanta abar dakinki dasu,
Tanajin haka zata fara ihun ta bata dake daman tace Daddynta kadai ne mutum a gidan nan"

Qarasawa tai tana dariya
Mama ma wayar ta gama ta kashe tana ajewa tace

"Daman wannan me jajayen kunnuwan kowama a gurinta ba mutum bane Ubanta ne kadai mutum mu da sauran mutane duk witches ne"

Dariya Fiddausi tasaki tana qarasa tattara dakin dayake fes tace

"Ke mama tace tinda ke ne kika haifar mata daddynta baki qarasa zama witch dinba mune dai witches din da duk macen datake kallan mata daddy tace witch ce itama"

"Dukan bakinta na dena shiyasa take fadar hakan da kuma shi uban nata dayake biye mata,
A haka takeson ya qare rayuwar ba aure girma sosai yana zuwar masa sbd kawai 'yarsa tace batason kowace mace ta rabesa,
Shima wannan qaton dayan uban nata ya zama wani tuzurun me zaman kansa ba auren tinda uban gidansa baiyiba duk sun qare a yawon duniya da aiki ba mata a rayuwarsu,
Ni duk kin tado mun takaicinsu ma yanzu ana maganar Aljanar 'yarsa ta fara ihu tana kukan babanta bazaiso kowace maceba bataso shikuma yazo yana biyeta su siqani da safen nan abincin arziki ma nazo na gagara ci,
Maza ficemun da kayanta a daki dan karma tazo nemansu ta hanani zaman lafiyar yau"

Humidifier Fiddausi ta kunna tareda daukan kayan Falaq din ta nufi kofa tana dariya da cewa

"Mama keda Aminiyar taki kike cewa ayi waje da kayanta"

"Wannan batai Halin Aminiyar tawa me sunanta ba da 'yata Me sunan nata,
Kina ganin 'ya a sangarce sai kukan banza da girmanta,
Wata ran fasa bakin zanyi kowama ya huta sedai ubanta ya gashi da matse fuska ya hakura ba ruwana"

Dariya Fiddausi takeyi tana ficewa dakin tareda sake duba agogonta taga time yayi kai tsaye ta nufi hanyar dakin Falaq din dayake hanya daya sa Palon Daddynta da bedroom dinsa.

Tana isa hannu takai ahankali ta bude dakin tareda shiga kai tsaye tana rufo dakin tana isa bedside din lafiyayyan gadonta dayake cikeda pillows kusan guda 9 masu tsananin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login