Showing 6001 words to 9000 words out of 81012 words

Chapter 3 - KALBIM HAUSA NOVEL

MAMUGEE   

16 Sep 2025

178

Mama sakinar ba dan yana taba kofar gidan baba ilan dukan da bazai iya bawa ummansa kulawa ba a yanzu datake tsananin buqatansa zai masa shikuma bazai iya barin komai ya samesaba a yanzu dayake son kulawa da umman da 'yar data haifo musu.

Gefen kofar gidan ya koma kadan ahankali ya durqusa yana sunkuyar da kansa qasa dan jiran ayi kiran asubar da yasan lokaci yayi insha Allah.

Wani irin sanyi ake kadawa sosai
Sauran ruwan da aka dan dauke suna yayyafowa akansa ahankali suna ratsasa amma bai ko matsaba bare alamar tashi bakin kofar gidan.

Jiran kusan awa daya da mintina yayi kafin masallaci daya kwal dayake kauyen suka rangada kiran sallan daya sakasa miqewa da dauri kafafunsa da sukai wani irin riqewa suka kasa daukansa ya zube a gurin cikin ruwa da lakar datake lalace sosai da kofar gidan.

Rintse idanuwansa yayi zuciyarsa data fara bushewa tin yana karamin nasa ta masa wani irin nauyi yana jin kirjinsa na masa ciwo.

Hawaye masu dumi ne suka gangaro masa ya dafa yana kokarin miqewa aka bude kofar gidan.

Baba ila ne da babban dansa dayake uztaz wanda shi yake sako uban nasa gaba zuwa masallaci lokutan asuba a gida yake sallan baya zuwa masallaci da asuba.

Bude kananun idanuwansa masu kama da kamar an kashe kwarkwata ya waresu akan Abdul din duk da akwai duhu sosai har lokacin amma baya buqatan wahalarda kansa gurin sanin waye dan kai tsaye yasan baida tsohon dan iskan dazai zuwar masa gida bayan Abdul din wanda yake fatar Allah ya nuna masa sunbi duniya sunbar kauyen ko gidansa zai huta da maitar Abdul din.

Cikin zafin rai ya harbi Abdul din da kafarsa yana cewa

"Uban waye a kafar gidana cikin duhun nan??

Cikinsa daya harba ya dafe da hannunsa daya yana dagowa cikin tsananin azaba ya dafa hannunsa daya ya miqe yana kokarin bude baki zaiyi magana Baba ilan ya rigasa da cewa

"Nace uban waye ne a gurin?

Gali dayake gefen baban fitilar hannunsa ya kunna yana haske Abdul din da ita cikeda mamakin ganinsa duk da yasan yana zuwan amma a cikin ruwa da sanyin nan me yakeyi a kofar gidan wanda da alama ya dan jima.

Wasu hawayen ne suka sake gangarowa daga jajayen idanuwansa kafin ya bude bakinsa muryansa a sanqare da sanyi duk da yasan suna sane da waye din amma bude baki yayi yace

"Nine Abdul"

Katsesa Gali yayi da cewa

"Lafiya kuwa cikin sanyin?

Bude baki yayi zaiyi magana amma Galin ya wuce cikim sauri yayi masallaci sbd jin angama kiran.

Baba ila ne ya kallesa cikeda baqin ciki da tsana me tsananin gaske yace

"Allah ya tsinewa sanayyar datake tsakanin Sakina da Uwarka dan kuwa babu abinda kuke qararta dashi sai baqin talauci da baqaqen masifun da kuke yawo dashi,
Ace har tsakar dare bata huta da masifunku ba,
Yanzu ubanme zatai muku da asubar farin??

Wani abu me daci da nauyi Abdul ya hadiye kafin ya bude baki yace

"Haihuwa ummana tayi"

Cikin sabon baqin cikin daya tirniqe baba ilan ya tsaki tsokin daya saka Abdul din rintse idanuwansa yace

"An haifowa sakina wata sabuwar Masifar kenan,to wlh tallahi baa gidana ba,
Na gaji bazan iya ba,duk yanda nake shan rantsuwa da masifa sakina ta ture bata ji bata gani saita ringa daukan abincin danake wahala ina nemowa na gidana ta baku to daga yau ankai karshe sbd bazai yiyu ni ban tara nawa yaran dazan ringa ciyarwa ba haka kawai na koma ciyar da 'yayan wani katan"

Juyawa yayi ya koma ciki yana fasa zuwa masallacin bakinsa na cikowa da kumfan masifa sbd yasan yana tafiya wlh sai an dauki abincin gidansa ko wani abin antafi dashi sbd sakina dai sedai ya barwa fatima da 'danta dan bazata iya rabuwa dasu ba.

Abdul cikin tsananin sanyi da azabar data gama shigarsa ya bi bayan baban da sauri dan kada ya hanasa ma shiga.

Kai tsaye dakin sakina ya nufa ya kiran sunanta cikin tsananin baqin ciki da masifa taresa bacin rai yana cewa maza ta fito.

Daman ba wani nauyin bacci ne da ita ba dan haka cikin bacci taji yana kiran sunanta da karfi ta bude idanuwanta tana kokarin tashi zaune ya shigo dakin sbd daman baa dakinta ya kwana ba ranar a dakin uwargidansa ya kwana.

Yana shigowa dakin ta lalubo fitilarta ta kunna haske ya wadata dakin,

Akan Abdul dayake tsaye a kofa bai qarasa shigowaba idanuwanta suka sauka.

Faduwa gabanta yayi da sauri ta janyo dankwali tana daurawa akanta ta miqe daga katifar datake kai tana ambatar sunansa baba ila ya katseta da cewa

"Ayau idan har kika fita gidan nan kika bi yaron nan gurin uwarsa wlh tallahi a bakin aurenki hakama abinci na ko wani abin dayake nawa a gidan nan kika basu shima a bakin aurenki,
Bazan iya ba na gaji da renan 'da da uwar da banda hadi komai dasu bare yanxu wata wahalar da aka sake haifowa......

Da sauri sakina ta dago idanuwanta da ciko da hawayen tashin hankali da firgicin maganarsa ta farko ta kalli Abdul jin maganar haihuwar.

Shima dago jajayen idanuwansa yayi ya kalleta cikeda girgiza da tsoron abinda Baba ilan ya fada.

Gangarowa hawayensa masu tsananin zafi sukai ya dan ja baya ahankali batareda ya iya cigaba da tsayawa ba sbd bai san me zai fadawa mama sakinan ba kuma.

Bude baki tayi ahankali tace

"ABDULAZIZ"

Cak ya tsaya batareda ya dagoba.

Kofar inda kayanta suke tai batareda ta cewa baba ilan komaiba,

Zannuwan kayanta na sakawa masu tsafta ta dauko tareda guda biyu da rigarta ta sanyi daya da ita kadai takeda ita ta dauko wanda itace da kanta ta siya abinta da yan kudinta.

Inda take ajiye kudi ta duba tana saka hannu cikin kofin silver me murfi taji babu komai a ciki.

Juyawa tayi ta duba gurin ajiyarta daya taga dari bakwai ne kadai da ita dan haka ta dauko dari biyar ta juyo ta nufi kofar ta fito.

Kayan ta miqa masa cikeda kunyarsa duk da yana qaramin yaro ta bude baki asanyaye tace

"Ka siya mata koko me zafi sauran canjin ka siya itace ka dafa mata ruwan zafi tayi wanka itace da abinda aka haifa"

Hawayensa ne suka gangaro ahankali suka sauka akan dari biyar din data dora masa a tafin hannunsa.

Kasa magana yayi kai ya gyada mata ahankali yana damqe kayan hannuwansa na qara daukan sanyi.

Baba ila daya kasa motsawa sbd baqin ciki da mamaki kallanta yayi ita kuma taqi kallansa
Baqin ciki sake rufesa yayi kamar zai fashe sbd baqin ciki yace

"Sbd ki nunamun ban isaba shine a gaban nawa ko matsawa daga inda nai maganar banba zaki dauki abubuwa ki basu??
To meye amfani na a rayuwarki sakina tinda kinada Fatima da 'danta ai saiki fice ki bisu kije na bar musu ke wlh"

Abdul kafafuwansa da sanyi yayiwa mugun shiga ya ja ahankali yabar gurin yana qanwame kayan data basa da kudin.

Yana ficewa gidan Mama sakina ta dago ta kalli baba ila har zatai magana sai ya katseta cikin tsananin zafi da cewa

"Wlh tallahi na barwa fatima ke kawai ki tattara ki bar mun gidana ki bita can saiki kwasheta kiyi kauyenku da ita da 'yayanta"

Kofa ya nufa yana ball da butarta dake hanyarsa ta wucewa yana jin zuciyarsa na wata irin tafasa da bacin rai me tsanani.

Numfashi me sanyi da mutuwar jiki ta sake tana danne zuciyarta akan furucinsa wanda shedan ke ingizata data bar masa gidan nasa ta tafin sbd su fatima sunfi buqatarta amma kuma girman auren nata take kalla ta danne zafi da bacin da ranta yayi dan yanzu ne zata biye masa suyita masifa a cikin gidan har wayewar gari da wuni zasu iya wuni suna masifa.

Butarta dayayi wurgi da ita ta nufa ta dauka tana qarasa zubar da ruwan ciki da suka rage ta nufi gurin diban wasu ruwan tana duba butar idan bai fasa mata ita ba.

Tana diban ruwan bandaki ta fara shiga tana fitowa tai alwala ta shige dakinta.
#MAMUH
#ZADEENS
#LIMBAS

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
mamuhgee

A DUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo

Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi

Shedan biya
09033181070

Or mtn vtu at
09032345899
*_KALBIM_*
_Mamuhgee_
#ZafafaBiyar



5
*ZUZEAMVENTURES*
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah >?p?=?L? Bononza Bononza Tsimin mangoro 1k>?m? Tsimin dabino 1k Gumba ukku balai 700 Gumba aya da nonon rakumi 700 Garin kafi ciccibi 500
Garin bata gaban kishiya 500
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 9500
Za a bakisu akan 3800
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
=????=????=????=????=????=???? ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA=؃?


************
Abdul kuwa yana fita gidan tafiya me dan tsayi yayi kafin ya durkushe a gurin yana fasa wani irin kuka me tsananin gaske sanyin gaske na ratsatsa.

Saida aka fito masallaci kafin ya daure ya qarasa gida,

Koda ya isa zanin dayake rufe da umman me sanyi kawai ya yaye mata ya rufa mata daya daga cikin wanda mama sakina ta basa,
Leqa babyn datake kwance gefen umman yayi yaga bacci takeyi lafiya kalau dan haka ya fice.

Alwala yayi ya dawo daga kofar dakin ya samu inda yayi sallah.

Yana idarwa ya dawo cikin dakin ya taba ummansa yaga tana numfashi.

Ajiyar zuciya me tsananin sanyi ya sauke kafin ya fita sbd gari ya waye sosai.

Gurin me siyarda koko ya tafi
Sai alokacin ma take hada wutar hada kokon dan haka yabar kudinsa ya koma ya nufi daji ya samo abinda zai hura wutan ruwan zafin da mama sakina tace.

Duka sun jiqe abubuwan daya tsinto amma hakanan yaje ya siyo ashana ya karbo kokon daga nan ya kawo mata.

Daqyar ya iya taimakawa umman ta tashi zaune ya dora mata robar kokon wadda ta bude bakinta daqyar kokon na shiga wanda zafinsa ya sakata jin hanjinta da suka nade suka dunqule fara warwarewa harma cikin na dan mata ciwo.

Tana gama shanye kokon amai ya taso mata gabaki daya ta amayar dashi.

Wutar ya hau hurawa wadda ta cinye gaba daya ashanar daya siyo sai daya koma ya qaro wata itama saida ta kusa qarew kafin wutar ta kama jikinsa na rawa ya dora ruwan.

Hura wutar ya zauna yanayi sosai batareda ya hutaba har saida ruwan sikai zafi sosai.

Umman daqyar ta iya tasowa ta nufi bandaki yakai mata ruwan shima ya fito ya dauko babyn ya fito daga daki sai a lokacin ya zuba mata idanuwansa yafara yi mata wani irin kallan tsafta me hade da wata irin kauna me tsananin gasken da batada sirki.

Wanka sosai umman tayi ta gyaro kanta ta fito har lokacin bata iya ko tsayuwar kirki.

Uwar haihuwar data bari a dakin ta shiga ta dauko ta goma gefen gidansu daya zube ta binneta daqyar jikin yana kakkarwa sosai sbd jirin gaske ma take gani.

Yana ganin hakan ya shiga dakin da sauri ya dan gyarosa ya share ya goge duk sanyin dakin tas ya sake shimfida mata wani zanin akan qaramar katifarsu umman ta kwanta.

Fita yayi ya sake siyo mata koko da saura Canjin daya rage ya kawo mata sedai koda ya dawo gabaki daya ta fice hayyacinta bama zata iya ko motsawa ba bare sanin meyake fada.

Ajiye robar hannunsa yayi yana kokarin dagota amma gaba daya jikinta ya sake.

Ambatar sunanta yafara yana shafa fuskanta zuwa wuyanta kuka na zuwar masa sosai.

Kuka me qarfin gaske babyn datake gefensu ta fasa wanda ya sakasa saurin juyowa yana rasa ya zaiyi.

Kuka sosai baby tafara wanda ya sakasa sakin umman ya zauna tsakiyarsu yana sunkuyar da kai shima ya fara kuka yana wani sheshekan da har jikinsa rawa yakeyi.

Ya jima a hakan batareda yasan me zaiyiba har babyn ta gaji tayi shiru ta koma bacci.

Ummansa kuwa wata firgita ta fara tana jijjiga.

Qanqameta yayi yana ambatar sunanta amma batasan ma yanayi ba.

Kusan awa daya a hakan kafin jikinta ya sake sakewa tayi baccin wahala.

Shima a gurin cikin jikinta baccin walaha da yunwa ya daukesa.

Sai azahar ya farka ya fita gidan ya nufi gurin aikin lakar dayake zuwa yana dan tayasu suna basa nera dari.

Acan yayi sallah yayita musu aiki har wanda yafi karfin shekarunsa.

Daga can wani kokon ya sake siyowa ya kawo yasha shida umman wadda sedai ya bata daga kwancen dan bata iya tashi hakama gabaki daya ta koma kamar ba umman tasa ba sbd wasu abubuwa takeyi da fizge fizge da zabura.

Yamma nayi yasan baba ila baya gida dan haka ya dauke babyn ya rufeta da zani kusan uku ya nufi gidan mama sakina da ita sbd tanada kuka.

Harya isa gidan babu wanda ya taresa ya tambayesa sbd gudunsu ma akeyi a kauyen sbd camfa ummansa da akai da baqar mace.

Mama sakin wuni tayi cikin damuwa da tinaninsu dan haka tana zaune tana hada saka da warwara tagansa ya shigo da zani
kallo daya tai masa ta gane jaririyarce ya dauko.

Cikeda mamaki da tsoro ta kallesa tana miqewa ta karbi 'yar tana cewa

"Abdul meyasa ka fito da ita??
Yaya ummanku?
Ya jikinta?

Kasancewarsa mara hayaniya da rashin sabo da magana sosai sbd baida abokan wasa ko wasu yan uwan daya taso cikin gata yasa ita kadaice ma wacce yake magana da ita sosaima
Ya dan dago kansa batareda ya kalleta ba yace

"Tanata kuka ne tin dasafe,
Umma kuma batada lafiya tanata firgita"

Kasa cewa sakina tayi ta nufi daki takai yar da sauri tana fitowa ruwan zafi tafara dorawa kafin ta dauko abincinta na rana da bata samu ci ba sbd damuwa ta miqa masa tace

"Maza zauna ka cinye yanzu"

Zaunawa yayi yaci abincin ita kuma tana sauke ruwan dauko babyn tayi tahau yi mata wanka sbd batason baba ila ya dawo ya taddasu hakama batason yayi dare a hanya da 'yar.

Wanka sosai me kyau tayi mata duk da bata taba haihuwaba batasan yaya akeyiba amma dayake anata haihuwa a gidan tana gani kuka tana dan saka hannu sai ta iya.

Tana gama mata wanka kayan data siya guda daya na jiran haihuwar matar Gali 'dan mijinta ta dauko ta sakawa yar ta dauko madarar shanun datake da ita me kyau ta bata kuma cikin ikon Allah yarinyar tasha take ta koma bacci abinta.

Sake nade masa ita tayi sosai ta basa tace maza ya koma.

Karbanta yayi ya juya ya fice daga gidan.

Koda ya isa gida ummansu ta tashi tana zaune ta zubawa kofa idanuwanta da sukai fari fes hakama bakinta ya bushe sosai.

Cikeda mamaki da dan farin cikin ganin ta tashi ya qaraso yana cewa

"Umma kin samu lafiya?

Juyo idanuwanta da suke kamar a buge tayi ta zuba masa batareda tace komaiba sbd kamar ba yayanta bane take gani.

Sake tambayarta yayi yaga ko kyaftawa idanuwanta basayi kallansu takeyi numfashinta baya fitama daidai.

Babyn ya bude daga zaninta ya dora mata a hannunta yana cewa

"Mama sakina tai mata wanka ta saka mata kaya"

Babyn ta saukar da idanuwanta ta zubawa ido tsawon mintina kafin ta dago ta zubawa Abdul din idanuwan shima
Shima ita yake kallan cikin tsoron irin kallan datake musun.

Sakin babyn tayi da sauri ya tare tareda daukanta ya ajiye gefensu yana cewa

"Umma kin gaji ne?

Har lokacin batace komaiba bata kuma dena kallansaba kaman wanda bata saniba ko bata taba ganiva.

Zamewa tayi ta koma ta kwanta tareda zubawa babyn gabanta ido.

Har dare yai suka kwanta batareda sun samu abinda zasu ci ba umman batai magana ba har lokacin hakama bata dena kallansu ba.

Cikin tsakar dare cikin bacci yaji motsin umman ya bude idanuwansa sai yaga ta tashi zata fita ko dan kwali babu a kanta hakama bata ko iya tsayuwa da kyau.

Kasa daukanta kafafunta sukai ta zube qasa kanta na buguwa da bangon kofar fita dakin take goshinta ya fashe da jini.

Tashi yayi da sauri yana riqota cikin tsoro da tashin hankali yana cewa

"Umma ina zaki?
Zaki bandaki ne?

Kallansa ta juyo tanayi kafin ta dago hannunta dayake wani irin rawa ta nuna masa kofa batareda tace komaiba.

Kofar ya kalla kafin ya kalleta sai ya rasa me zai fada ya kamo hannunta kawai ya dawo da ita kuma ta biyosa kamar yarinya qarama.

Kwantawa suka koma sukai take kuma saita koma baccinta.

Gari na wayewa yaje yayo aikinsa ya dawo mata da koko ya sake dafa mata ruwa ya sake ficewa.

Sai yamma ya dawo musu da tuwon dawa da miyar kuka dan kadan wanda aikin wahala yayi ya samosa.

Kasa cin abincin umman tayi duk yanda yayi sa ita dan haka kaman yanda yake bata koko haka ya zauna ya bata abincin a baki da kansa.

Babyn kuwa sake kaita yayi gurin mama sakina ta bata irin madaran jiya tasha ya dawo da ita gida.

Yana dawowa a hanya ya hadu da ummansa tana tafiya tana jiri ba dankwali akanta,

Da sauri ya kama hannunta suka juya gida yana mamakin abinda ya samu umman ga jikinta duk jini.

Suna komawa gida ya zaunar sa ita yana mata magana amma kwata kwata batacewa komai kallansa kawai takeyi.

Hawaye ya fara batareda yasan me zaiyiba.

Da daddaren ranar ma so biyu tana kokarin fita yana dawowa da ita tim anan ya fahimci ummansa ta kamu da wani sabon rashin lafiyar.

Kuka ya ringa yi har safe kuma da safen ma daqyar ya iya fita yabarta.

Koda ya dawo bata fita ba amma tana zaune babyn nata kuka sosai kamar bataji sai kallanta takeyi idanuwanta sunyi jajir kamar zasu fashe.

Daukan babyn yayi ya zauna gaban umman ya fada jikinta yana fasa kuka shima yana ambatar sunanta.

Kukansa ne ya saka wani irin hawaye masu tsananin zafi da ciwon da bata saniba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login