Showing 54001 words to 57000 words out of 81012 words

Chapter 19 - KALBIM HAUSA NOVEL

MAMUGEE   

16 Sep 2025

202

hakama ko securities sun san shi kwata kwata baya wani muaamala da mutane hakama baya wani yawo sosai,

A gurin kwance ya farfado sbd sanyin asuba dayake kadowa a hankali daga balcony dinsa dayake bude yana saukar masa..

Jajayen idanuwansa da ganinsu ya dauke ko kadan ya dena ganin komai ya bude suna wani irin radadin da duk azabarsu bayajin komai sbd har Allah ya dauki ransa dayake fata a yanxu bazai taba jin radadin dayake a yanzu yana yanka duk wani tsokar datake kirji da zuciyarsaba azabar daukan raine kadai da baisaniba yake jin zatafi abinda yakeji yana tarwatse zuciyarsa da kwakwalwansa datake dena aiki,

A yanda yaken babu inda yake motsawa a jikinsa har gari yafara haske ya sake somewa a gurin sbd azaba da radadin dayake kirjinsa yayi masa tsananin da baya motsawa amma azabar tayi qarfin datake sumar dashi ya sake ficewa hayyacinsa.

Mai aikinsu shida wanda yake next floor yazo aikinsa aikinsa guraren karfe 9 na safe kai tsaye ya bude kofar sbd yasan code na budewan.

Iskan dayake kadowa daga balcony ne yana ratso palon me tsananin sanyin gaske ya saka Eden nufar hanyar balcony din bayan ya tafi extra room din dayake kaman nasa anan yake ajiye jakarsa da laptop dinsa ta karatu ko kallo ko wani abin idan yazo da ita.

Sauke jakarsa yayi daga bayansa ya ajiye tareda ledar fresh fruits din dayazo dasu me girma wanda Tin jiyan LIMBA ya basa kudin ya siyo idan zai taho yau.

Da ledar ya fito daga dakin ya nufi kitchen ya ajiye ledar ya nufo balcony din dan rufewa sbd sanyin yayi yawa sosai yana mamakin ya akai Mr LIMBA ya bar balcony din a bude sbd bayason sanyi sosai.

Taku biyu yayi idanuwansa suka sauka akan LIMBA din dayake kwance a kife cikin mummunan yanayi ga jini a fuskansa duk ya bushe ba kyan gani babu alamar rai a jikinsa.

Da gudun gaske ya nufesa cikin matsanancin tashin hankali da tsoro yana kiran sunansa.

Birkitosa yayi da karfin gaske sbd nauyin da yay sosai alamar da gasken ba rai a tareda shi.

Ihun gaske ya sake yana sakinsa ya miqe da sauri koina jikinsa na rawar tsoro da firgita,

Kararrawan neman taimakon gaggawa zuwa ga securities da reception na building din ya danna da hannuwansa biyu yana sake daddanawa ba kakkautawa a rikice.

Ganin kaman hakan bazaiyiba sai kawai ya rarumo wayar Limban datake gefe a yashe ta mutu ya nufi gurin caji da sauri yana kokarin sakawa manager da securities suka iso cikin sauri suna buga kofar ya bude da sauri yana jifa da wayar suka shigo da gaggawa suna ganinsa a hakan hankali tashe aka kira ambulance tareda likitansa dayake kamar Abokinsa
Cikin gaggawa Dr Nico yace ayo asibiti dashi.

A cikin nurses da suka taho da ambulance daukansa tin anan aka gane he is paralysed dan haka tin anan suka fara bawa rauninsa taimakon gaggawa aka kwashesa zuwa asibitin.

A asibiti ana isa cikin gaggawa akai cikin emergency dashi sbd zuciyarsa dake bugawa ahankali kaman zata tsaya hakama numfashinsa dan haka hankalin dr Nico ya tashi dan suna buqatan gaggawar dawo da bugun zuciyarsa daidai idan ba hakan ba zaa iya rasashi.


Kamar kar afara basa taimako ya rikice gaba daya kokarin rasashi akeyi dan haka hankalin likitocin gaba daya ya tashi aka saka masa oxygen ana kokarin hana zuciyarsa dena bugawa,

Kokari sukeyi amma kwakwalwansa failing takeyi wanda kwata kwata baa son hakan...

Duk yanda suka ringa kokarinsu babu abinda yake karban kokarin da sukeyi a jikinsa,

Ba yanda suka iya dole aka yaga rigar jikinsa
Dr Nico yace nurses su kawo Defibrillator

Da gaggawa aka kawo tareda sauran abubuwan Dr Nico ya bawa dayar dr din shi ya fara hadawa da sauri

Cikin sauri dr yace su kunna yafara kirga da sauri ya danna a kirjinsa ya basa AED a kirjinsa wanda ya sakasa yowan sama yana komawa ya zube babu alamar rai a tareda shi..

Da sauri ya sake cewa su basa wuta ya sake manna masa yana cewa

"Com on com on com on LIMBA pls pls pls......

Cikin sauri nurse tace "hes Getting it Doctor"

Cikeda fatan ya tashi ya hada na ukun yana danna masa sbd daga shi idan bai tashiba shikenan.

Danna masa yayi yana daukewa Nurse tace "dr the heart.....

Bata qarasa ba ya juyo da sauri yana cewa a basa sauran alluran da zai masa da gaggawa.

Dr Nico ne yai masa alluran sbd bugun zuciyarsa ya dan samu karfi.

Aden dayake wajen Emergency din yana kaida kawo cikin fargaba da rikicewa ya zauna ya tashi ya rasa ya zaiyi sbd tsananin Tausayin yanda A lokaci daya LIMBA ya koma kalar tausayi.

Dr Nico damuwa ce sosai a tattare dashi sbd Bugun zuciyarsa ya dawo daidai sedai babu inda nasa yake motsi sun bincika sun tabbatarda ya samu paralys din da shock ne me girman gaske ya haifar masa dashi wanda zuciyarsa take kasa dauka.
##MAMUH
#BESTLOVE
#BROTHERS LOVE
#RESTINPEACE UMMITAH LIMBA

ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
mamuhgee

A DUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo

Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi

Shedan biya
09033181070

Or mtn vtu at
09032345899
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
29
*_LADIES COLLECTION AND MORE_*
08169307477
SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE?
KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU?
KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI?
KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA?
Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa,
Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai?

To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane,

MAZA KI ZIYARCI LADYS COLLECTION AND MORE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah,

LADY'S COLLECTION AND MORE

ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA =?G?
Zumar kiba
Zumar breast
Zumar hips
Zumar infection
Zumar sliming
Zumar sabon budurci
Back to virgin
Abayas
Atamfa
Less
Hijabs
Supplements
Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko

08169307477

Address bayan gidan drugs katsina State

Kayan mu masu inganci ne sosae

Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba=?O? SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA=د?


***********
Duk yanda Dr Nico ya dage sosai cikin tsananin tausayawa yana neman lafiyar LIMBA sam babu cigaba sbd baya karban treatment da ake basa sbd Zuciyarsa data riqe da abinda yake cikinta sai sauki baya samuwa,

A kwance yake ba motsi ba magana ba kuka ba kowane irin reaction da ake samu daga garesa dan haka jikin nasa yake sake mutuwa,

Manyan likitocin da sukeda su asibitin Dr Nico ya sako a case din ABDULAZIZ suka duqufa amma sam sbd bayason ya tashi duniyar yakeson bari shima sai babu sauki a zuciyarsa ko sassaucin tsananin quncin dayake cikinta sai anata magani amma ba sauki.

Aden ne yake kulawa dashi sbd ABDULAZIZ yayi masa abinda baitaba samu daga kowa ba,
Shine ya dauki nauyin karatunsa dana kanwarsa sbd duk inda yaga yaya yana son kanwarsa jin yake yana kauna da Tausayinsu dan haka babu abinda bazai iya yiwa ABDULAZIZ LIMBA ba dan haka yake jinyarsa.


****lokaci yafara tafiya babu wani sauyi daga lafiyarsa,
Wata rama yakeyi sosai tana cinyesa daga kwance tana busar da fatarsa,
Ya tara suma da gashin fuskan har lokacin babu abinda yake motsi a jikinsa,

Asalin qunci da radadin da babu magani ne yake cin zuciya da ruhinsa ko idanuwansa bai cika budewa a rufe suke kusan koyaushe sbd basuda kyan gani suma sun kode sun jeme radadi da qunci kawai kake hangowa a cikinsu tareda cire rai daga duniya da abinda duka yake cikinta.

Aden ne ke dawainiya dashi komai shine yake masa cikin kulawa da fatan samun lafiyansa gashi duk yanda zasuyi contacting familynsa an rasa sbd wayarsa ya rasa inda ya yarda ita an nema an rasa dan haka suke dawainiya dashi shida dr nico wanda yayi iya kokarinsa akan ABDULAZIZ ya sassautawa zuciyarsa dan saiya sassautawa kansa zasu samu lafiyar da ake nema masa tafara samuwa amma hakan baya samuwa dan haka ya hakura yana cigaba da kulawa dashi sedai ahakan ya sani ABDULAZIZ bazai dade a duniyarba zai iya samun bugawan zuciya daga kwancen.


***Aden ya sadaukar da rayuwarsa a watannin akan ABDULAZIZ din wanda suka hakura suka cire rai daga tashinsa sbd ya koma ba kyan gani
Ahankali ahankali yake rasa sauran ji da ganin daya rage masa....

Kuka sosai Aden yakeyi a lokaci da dama idan ya kalli ABDULAZIZ din idan ya tina asalin kamanninsa da haibarsa tareda wani irin aji da kwarjininsa tareda tsarin rayuwarsa datake cike da Class da burgewa amma ayau gashi a kwance komai sai anmasa.

Ahakan ya dauki watanni koyaushe suna jiran ji daga familynsa tinda su sun kasa samunsu.


*************
Motar fash ce tayi parking a asibitin cikin damuwa da shakkar halinda ABDULAZIZ din yake ciki suka qarasa reception suka fadawa nurse din dasuka samu agurin cewa Dr Nicolas sukeson gani.

Kallansu tayi kafin tace dr Nicolas din ya shiga tiyata sedai su jira.

Kallanta Alh saad yayi yana cewa "akwai patient me suna ABDULAZIZ LIMBA mune familynsa"

Kallansa tayi kafin ta kalli Fash da shima itama yake kalla yana jiran amsarta.

Dawo da kallanta tayi kan Alh Saad tana mamakin lokacinda suka dauka basu taho garesa ba duk mummunan halin dayake ciki baida jininsa a kusa.

Numfashi me sanyi ta sauke tana cewa

"AZIZ AY LIMBA?????

yes" suka ce mata dukkaninsu cikin sauri.

Kallan nurse din kusa da ita tayi ta fada mata familyn Patient din dr Nicolas ne LIMBA.

Itama nurse din kallansu tayi d sauri tana ajiye Wayar datake amsawa da mamaki tace amma basusan halinda yake ciki ba ko?

Yes sukace suna cewa ganinsu kawai suke tsananin so a yanzu.

Room number aka fada musu bayan an duba id cards nasu an dauki sunan da sauran bayanai se dayar nurse din datake kulawa dashi wani lokacin cewa tai su biyota takaisu.

Bin bayanta sukai Banda Fash da akaiwa kiran gaggawa kuma mahaifiyarsa ce dan haka su kadai suka nufi dakin ya juya da niyar zai dawo anjima.

Tinda suka kama hanyar dakin dayake bugun zuciyar Sayyid ya tsananta yana jin jikinsa na sanyi yana jin ciwon lokacinda suka dauka batareda an taho duba lafiya ba jinsa shiru wanda da Ummitah na raye bazata ji dadin hakanba....

A kofar dakin nurse ta tsaya tareda nuna musu su shiga ta juya tabar gurin zuwa aikin gabanta..

Alh Saad ne ya miqa hannunsa ya bude dakin tareda turawa ya shiga kai tsaye yana Jefa idanuwansa

Ko taku biyu baiba ya tsaya cak yana kallan Abinda yake gabansa cikin wani irin tashin hankali da tsoro zuciyarsa na cika da tsoron Allah mai tsananin gaske na ganin ABDULAZIZ yanda koma dan ma kasa gasgata idanuwansa yayi ya juyo da sauri ya kalli Sayyid wanda ya kasa qara taku ko daya daga inda yake yana kallan Hamman Ummitah wanda yake zaune kan kujera an dauresa sa belt sbd baya iya zama kamanninsa kaf sun sunya zuwa wani quncin da kansa,

Tea me kauri Aden ke basa amma baya shiga dawowa yakeyi yana saka tissue me yawa yana goge masa.....

Wani irin kukan dayake tafe da tsananin qunci da radadin zuciya ya kufcewa Sayyid yana tahowa da sauri ya rungume ABDULAZIZ din wanda ya rintse jajayen jemammun idanuwansa a karon farko hawaye masu tsananin dumi na biyowa gefen idanuwansa suna gangarowa.

Kuka sosai Sayyid keyi yana jijjiga ABDULAZIZ din zuciyarsa na radadin dayake jinsa har cikin kansa yana kasa cewa komai,

Kukansa ne yake ratsa zuciyar ABDULAZIZ da babu komai a cikinta empty take yana zana masa mutuwar yar uwarsa a zuciyar....

Zuciyarsa Alh saad ma kasa riqe jarumta yayi hawayene suke gangaro masa yana kallan hawayen dake gangarowa gefen idon ABDULAZIZ idanuwan a rufe.

Tsit dakin yayi kukan Sayyid me wani irin ciwo ne ke ratsa dakin cikin sauti me ratsa zuciya da sake dawo musu da mutuwar sabuwa.

Aden ma kukan yakeyi sbd ganin se yau hawaye ya sauko daga idanuwan ABDULAZIZ wanda zafinsu yake tabbatar da tsananin radadi da ciwon dayake zuciyarsa.

Sun jima a wannan yanayin me kashe jiki da quncin daya dawowa kowa sabo sai ga dr Nicolas daya taho da sauri jin familyn LIMBA din sun zo.

Hawayen daya tarar sun sauko daga idon ABDULAZIZ ya sakasa jin wani relief sbd zuciyarsa ta fara dawowa da feelings din daya rasa.

Kallansu yayi yaga irin yanda Sayyid ke kuka idanuwansa sunyi jajir ya dawo sa kallansa akan Alh Saad suka gaisa yana musu barka da zuwa tareda fara masa bayani akan ciwon nasa.

Numfashi me zafi Alh saad ya sauke tareda yiwa dr din godia mai tsananin gaske kafin ya kalli ABDULAZIZ din wanda idanuwansa suke rife yafara fadawa dr din qanwarsa ce ta rasu gurin haihuwa..

A kunnuwansa yakejin Ana fadar rasuwar Ummitah amma baya iya ko motsawa bare nuna quncinsa dan ya sake rintse idanuwansa radadin kirjinsa na qaruwa wasu sabbin hawayen suka sake gangaro masa yana jin karban ciwo da radadin da zuciyarsa ke masa.

Rasuwar Ummitah ta girgiza dr Nico din sbd yasan kaunar da limba kewa sister dinsa wanda kaunarta kamar dabiace kokuka ace kamar sunansa ne dayake yawo dashi dan haka ya tausayawa ABDULAZIZ tareda tabbatar musu da insha Allah Zai warke amma saiya bawa zuciyarta sassauci.


Duk yanda sukaso magana da ABDULAZIZ babu damar hakan sbd dai ba alamar ma yanaji din duk da yana jin amma basusan da hakan ba,

Sayyid sunkuyar da kansa yayi a gaban ABDULAZIZ daya kasa tashi ciwo kirjinsa yake masa mai tsananin gaske na ganin ABDULAZIZ hakan.

Shi kansa ABDULAZIZ din bai bude idanuwansa ya kallesaba tinda ya rufe dan haka a haka sukai shiru babu wanda ransa ba cike yake da damuwa da qunciba..

Aden ne ya fita dakin ya basu guri bayan ya qarasa goge masa jikinsa.

A asibitin suka wuni sai dare Aden ya tafi dasu gidan ABDULAZIZ din wanda yake fes cikin tsari me kyau da jin dadin rayuwa.

Alh Saad Sayyid kawai ya bari a gidan wani lafiyayyan lodge ya sauka sbd bazai yiyu ya zauna gidan ABDULAZIZ dinba sbd komai na ABDULAZIZ din akan tsari yake hakama ya wuce wani ya zauna gidansa sbd privacy nasa amma Sayyid qaninsa ne ba damuwa bane.

Shi kansa Sayyid bayan tafiyar Alh saad kasa zama yayi yafadawa Aden shima zai bisa ya kwana asibitin.

Dayake basa wani gane zancen juna amma ya gane dan haka bai musa masa ba suka koma tare.

A asibitin a wannan daren Sayyid ne yake kamawa Aden kulawa da ABDULAZIZ wanda tinda suka taho bai sake bude idanuwansaba.

Washe gari Alh saad yazo ya sake tattaunawa da Dr Nico akan ciwon.

Sayyid kuwa hankali ya maida kawai akan lura da komai na kulawa da Hamman sbd ya karbi kulawan dashi da kansa.


A ranar ma a asibitin Sayyid ya kwana tareda aden sai gashi cikin kwanaki kadan ya karbi ragamar kulawa da ABDULAZIZ din Aden ya samu ya maida hankali akan karatunsa.


****Sabon treatment aka fara yiwa ABDULAZIZ LIMBA wanda shima sam baya karba amma dagewan Sayyid daya fara taimakawa gurin dawo masa sa emotions dinsa da zancen Ummitah da fada masa yanda tayi rayuwa a kwanakin datake gaf da barin duniya da irin ciwon data ringa ahankali da yanda take maganarsa sai hakan yake motsasa hawayensa masu tsananin radadi koyaushe cikin gangarowa suke daga idanuwansa.

Kusan wata daya Alh saad ya share a garin anata fama kafin yafara shirye shiyen tafiya bayan an sallamo ABDULAZIZ din sunso dawowa Nigeria dashi doctors suka bada shawarar kada ai hakan su bari ayi treating nasa anan dan haka dole yabarsa tareda Sayyid wanda gaba daya ya koma baida hidima saita ABDULAZIZ din wanda ko idanuwansa bai cika budewa.

Bayan tafiyar Alh saad Aden ya dawo gidan sbd Fita siyayyar abubuwan buqatan gidan da sauran abubuwan da sayyid bai saniba shi kuma Sayyid rayuwarsa ta koma ABDULAZIZ kawai.


****jinya sukeyi me wahala sbd babu alamar sauki har lokacin hakama shi kansa Sayyid din ya koma kalar tausayi sbd yanzu wani lokacin idan trauma din ABDULAZIZ din ta tashi haka zai rintse idanuwansa ya wuni ya kwana bai budesu ba hawayene kawai ke fitowa acikinsu suna gangarowa masu zafi..

A duk lokacinda ya shiga wannan halin Sayyid damuwa yake shiga sosai idanuwansa suyi jajir sbd shi a zuwa lokacin zuciyarsa ta fara bushewa sam baida wasu emotions din yakeji shima.

Lokaci yafara tafiya kwatsam saiga Alh saad da mama da baby fatima ya kawosu sbd Mama dake neman mutuwa itama da damuwa da kunci ga jaririyar da takasa bawa anty maryam kuma ita bazata iyaba sosai sbd ciwo da manyanci dan haka ta koyaushe rokonta yakaita taga ABDULAZIZ kafin tabar duniya hakama akai masa 'yarsa yagani kila ya samu qwarin gwiwan da aketa son ya samu.


Zuwan mama da baby fatima ya qarasa rikita jikin ABDULAZIZ din gaba daya wanda komai ya dawo musu baya sedai kuma a ranar da aka ajiye masa Baby fatiman a kan jikinsa har an cire rai daga samunsa sai gashi Allah yasa yanada sauran kwana gaba dan haka likitoci suka ce a ringa kowota gabansa koyaushe.

Alh Saad ganin rayuwar Sayyid na neman mutuwa ya saka ya yanke shawarar sakasa makaranta yafara zuwa yana kulawa da ABDULAZIZ kuma dan haka ya zama baida ma lokacin kansa koyaushe busy yake.

Mama ganin ABDULAZIZ yasaka nata ciwon warkewa dan haka da ita suke jinyar abinsu wanda cikin ikon Allah aka fara samun yanda akeso sedai babu alamar zai taba komawa ABDULAZIZ dinsa na baya idan ya miqe.
#MAMUH
#THE NEW AZIZ LIMBA


ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
mamuhgee

A DUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo

Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi

Shedan biya
09033181070

Or mtn vtu at
09032345899
*_Arewabooks@Mamuhgee_*
30
*ZUZEAM VENTURES*
Best APHRODISIAC
08144015291
Aslm barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah >?p?=?L? Bononza Bononza

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login