Showing 51001 words to 54000 words out of 81012 words

Chapter 18 - KALBIM HAUSA NOVEL

MAMUGEE   

16 Sep 2025

193

5k dinki ki kwashi kayan 12k hajiyata =؃?


*********
Tafiyar da Alh Saad yace Zaiyi ya saka Maman da Sayyid samun dan sassaucin Halinda suke ciki.

Baba alhassan na jin hakan shima Ya tattara ya koma gida dayake ya sake zuwa sbd Yiwa Sayyid abinda yake tsananin so yana komawa ya saka gonarsa siyarwa da rabin hatsin daya noma a shekarar yayi kwana biyu yana hada kudin ya dawo da kudi me dan yawa kusan miliyan uku ya kawowa Sayyid suka kaiwa Alh Saad akan a tafi da Sayyid din dubo ABDULAZIZ din.

Itama mama jin hakan ta sake samun sanyi a ranta suka ringa rokon Alh ya tafi da Sayyid din.

Sbd kwanciyar hankalinsu ya amince tafiyar dashi batareda ya karbi kudinsu ba sbd yasa aka fara yiwa Sayyid din komai na tafiya wand hakan ya saka tafiyar ta sake samun tsaiko.


Baba alhassan duqufa yayi da addua da fatar komai ya tafi lfy sbd a zuciyarsa tsoro yaji yana shigarsa.

Mama ma adduar ta sake duqufa yi gashi a kwanakin kullum mafarkin ummitah takeyi wanda take ganin ABDULAZIZ ne a cikin wata masifar kila.

Sbd Lokacinda Ummitah zata rasu mafarkin ABDULAZIZ din ta ringa yi a mummunan yanayi sai gashi ashe rasa Ummitah zasuyi.

Sayyid haka ya ringa jin kaman zai zare sbd jiran shirin tafiya ya kammala visa ta fito,
Karatunsa da Alh Saad ya takura masa yaci gaba da zuwa Sosai ya maida hankali kaman zai kwana ya tashi a ace ya kammala sbd tsananin burin da ABDULAZIZ ya dora akan karatunsa tin farko yasa duk masifar da zuciyarsa take ciki ya tsaya ba gardama yana bude kansa sosai akansa.

Baba alhassan kuwa komawa yayi duk bayan lokaci yana hanyar zuwa abujan dubosu.

Baby Fatima kuwa anata renonta cikin koshin lafiyarta tana girmanta duk da bata samu nono ba jikinta nata yin kyau tana yar kibarta,

Anty maryam sbd basada nisa a anguwa daya suke bata tsallake ranar zuwa duba Baby fatiman da Mama wani lokacin kuma zuwa take ta dauketa acan zata wuni sai dare take kawota a mota dan basa bin hanya da ita duk da da nisan da sai anshiga motar.

Wata daya da sati biyu suka dauka kafin tafiyar ta kammalu suka tsayar da rabar tafiya.

Mama Kallan Sayyid tayi ranar da zasu tafin tana rungume da Baby Fatima ta zuba masa ido tana kasa iya cewa komai sbd batama san me zata fadan ba.

Baby fatima ya kalla kafin ya kalli maman yana bude baki Ahankali yace

"Mama nai miki Alqawarin zan dawo miki da ABDULAZIZ LIMBA a gabanki ko a yaya yake insha Allah sannan zan kula dashi fiyeda nawa kan"

Numfashinta ta hidiye cikin sanyi da samun dan sanyi a ranta tace

"Allah ya tsareku gaba daya ya dawo daku lfy yasa shima yana lafiyar"

Alh Saad ta kalla cikin mutuntawa da kulawa tace ta gode.

Baba alhassan ma addua yayi musu yana yiwa Alh Saad godia.

Mota suka shiga drivern gidan Alh Saad dinne zai kaisu Airport su mama na kallo motarsu ta fice daga gidan.

Ajiyar zuciya Baba Alhassan ya sauke ita kuma Mama kasa sauke ajiyar zuciyar tayi ta juya ciki tana sake rufe Fatima dake bacci a jikinta tana dan motsawa ahankali.


Tinda suka isa airport Alh Saad ya kalli Sayyid wanda kai tsaye kallo daya zakai masa kasan ya sauya daga asalin Sayyid dinsa na baya idan ka sansa.

Har a cikin jirgi bayan sun zauna babu walwala a tattareda Sayyid din dan haka bai takurasa ba ya kyalesa dan yasan zuciyarce ba dadi ko kadan.



******
Lafiyayyan toilet ne dayake da girma sosai komai a tsare,

Qamshi ne me sanyin dadi da nutsuwa yake tashi a cikinsa hakama da dan hayaqin zafin ruwan da ake wanka dasu dayake dan gauraya toilet din yana saka koina a toilet din daukan dumi ahankali.

Wanka takeyi a natse qamshin shower gel dinta me kyau da tsada yana sake tashi harta gama wankan ta kashe shower din tareda miqa hann ta janyo towel ta dauro a jikinta ta fito cikin Lafiyayyar jacuzzi din ta nufo gaban mirror daya kusan cike rabin bangon toilet din ta tsaya cak ta zubawa kanta idanuwanta da suka fara sauyawa ahankali.

Hannunta na dama ta dago ahankali ta dora akan kirjinta seti da zuciyarta dake bugawa ahankali cikin cikakkiyar lafiya..

Tabon dinkin gurin ta shafa ahankali tareda lumshe fararen kyawawan idanuwanta tana sauke numfashi ahankali me dumi...

Tin daga lokacinda ta wayi gari ta samu kanta a sabuwar rayuwa daukeda sabuwar zuciyar datake bugawa a kirjinta tasan duniyarta ta sauya ta dawo sabuwa a daidai lokacinda ta cire rai da rayuwa gabaki dayanta,

Allah ya bata damar cigaba da rayuwa a lokacinda take saka ran ta farko ta samu kanta a duniyar barzahu,

Duk wanda zuciyarsa take bugawa a kirjinta tana masa fatar samun rahamar ubangiji dashi da danginsa a duk inda suke,
Harta bar duniya bazata dena yi masa addua ba sbd sadaukarwansa gareta.

Ajiyar zuciya ta sauke ahankali tana lumshe idanuwanta tana sake jin bugun zuciyar wadda take tata ayanzu yana ratsata cikeda shauqi da samun nutsuwa da yanayin da bata saniba a baya na bugawar Lafiyayyar zuciya a kirjinta.

Ayau kusan wata hudu da kwanaki kenan da aikinta amma haryanzu ta kasa sabawa da sabuwar rayuwar data samun koyaushe jinta takeyi kamar sabuwar mutum sedai kauna da tsananin son datakewa yan uwanta familynta babu abinda ya sauya saima qaruwa da yayi sbd jajirwansu gareta.

Kaman yanda samun lafiyarta ya sauya rayuwarsu gaba daya a qanqanin lokaci sbd sabon farin ciki da jin dadine tareda sabuwar rayuwa ta dawo musu sabuwa dan haka komai nasu ya dawo tamkar baya kusan ma fiye dan farin ciki da kwanciyar hankalin dasuke dashi yanzu na tafiyar da komai yafi na bayan.

Ta jima a tsaye kafin ta juya ta fito toilet din.

Qamshin dayake tashi a bedroom din nata ne ya shiga hancinta ta dan Lumshe ido tana jinsa yana ratsata sbd komai a yanzu jinsa take kamar sabo gareta.

Gaban mirror ta nufa bayan ta zaro wani towel din tana goge jikinta a hankali kamar batason taba soft fatarta sosai.

Da kanta ayau ta shirya kanta sabanin tinda suka gama jinya a asibiti suka dawo gida Mimi ke tayata shiri sbd batason tayi aiki da jikinta ta gaji sbd sun saba a lokacin ciwonta abu daya takeyi zuwa biyu ta gaji sosai ba kuzari.

Body milk me kyau da qamshi ta shafa tareda Turare mai sanyin qamshi ta miqe ta nufi closet nata ta saka undies kafin ta saka oversize skirt and shirt na Liliana ta saka hula me laushi da rashin nauyi a kanta ta fito da slippers a kafarta sbd yunwa takeji abinci take buqata.

Anty Anny ce ta nufo palon itama sanye da shaking doguwar riga mara adon komai sai kudi tana qamshi fuskanta fresh dan itama gaba daya yinin ranar bata fito daga bedroom ma bare palonsu harta fito zuwa nan sai yanzu data fito neman abincin da zata dan duk da a familyn kowa da nasa bangaren amma a hade suke guri daya babu wani rarrabewa sosai dan kusan duka a guri daya suke kowa baifi kayi tafiyar corridor ba zuwa palo da bedrooms wani hakama duk yanda kowa yake bangarensa a tare ake cin abinci dining room dinsu daya ne hakama chiefs dinsu da masu aikin.

Rayuwar hutu kawai sukeyi mazan gidan ne suke fita aiki suma bawai sammakoba tinda sune masu companies dinsu amma matan kuwa da saleem ma sai lokacinda suka ga dama suke fitowa idanma ba abinci zasuci ba saika wuni a gidan bakaga ko dayansuba sai idan dare yayi ake taruwa babban palon ayita fira da yar hayaniya cikin walwala.

Anny na ganin Jannah ta zuba mata idanuwanta tana kallan yanda take sake warwarewa tana komawa lafiyayyar jannah dinta wadda ita bata saniba a baya,

Wani irin sirrin kyau da kwarjini ne da itama duk da bata gama zama cikakkiyar budurwar data amsa sunanta budurwanba amma haka kawai wani lokacin sai take mamakin saa irinta jannah din kowa sonta yake,
Babu abinda ta nema ta rasa,
Kowa zai iya komai dan bata abinda takeso,
A irin wannan gatan da Jannah din take ciki me zata nema a duniyar nan ta rasa?
Duk yanda familyn suke ganin babu abinda bazasu samar mata indai har tanaso akwai abinda yafi karfinsu shine ikon Allah,
Ita kanta zataso Allah ya kawo abinda Jannah zataso fiyeda komai ko buqata fiyema da zuciyar da aka dauki rayuka da dama akanta amma kaf familyn babu wanda zai bata kuma dukiyarsu bazata taba iya siya musu ba,

Zataso taga wannan ranar sedai batajin tana zuwa dan raine kadai bazasu iya siya mata amma ko rai din da zaace musu ana iya sakawa wani ran wani to tabbas zasu iya sedai Allah bai bada damar hakanba.

Isowan Jannah gabanta ya sakata sake murmushi tana sake kallan Jannah da yanayi na tinani kala kala akan fatan zuwan ranar da jannah zata dandana rashin ba komai ake nema a samu ba.

Da murmushi a fuskanta da kulawa tace

"Hey Jan sai yanzu kike fitowa?
Yaya jikinki?
Ya kikeji yanzu?
Karki manta duk abinda kikaji ba daidaiba ki sanar"

Fararen idanuwanta ta kalli Anny din dasu kafin ta saukar da murmushin kwanciyar hankali a fuskanta tana cewa

"Anty Anny karki damu i dont feel any uncomfortable yanayi,
Am all good"

Gaba tayi anty anny din na bin bayanta tana cewa

"Masha Allah"

Mimi ce itama ta fito a lokacin tana waya cikin walwala da annushuwa tabi bayansu dukansu dining room din suka nufa suka zauna daman dining din baa dauki mintina da yawa da gama shiryasa ba sbd ansan lokacin cin abincinsu na rana yayi kowane time zasu iya fitowa.

Suna zama qamshin Ammar ya doso dakin me sanyi da tsadar gaske tareda rashin hawa kai ko kadan.

Jannah ce taji wani sanyi yana ratsa xuciyarta tareda qamshin nasa ta dago idanuwanta tana kallan kofar daidai da shigowansa sanye cikin black thick riga da wando masu laushi fuskansa fresh da alama bai fita koina ba yau din shima yana gida hutu yake sosai haryanxu.

Kyakkyawan fuskansa jannah take kalla tana jin bazaa samu namijin da zai kai Ammar Zad kyau da kwarjini tareda haiba ba a idanuwanta har abada ba,

Ammar Zad shine mafi kyawun namiji data sani wanda shi kadai take zubawa ido bata gajiya da kalla.

Kallan datake masa ya saka Anny sakin murmushi tana kallansa shima kallan Jannah din yayi yana sake murmushi yana kujera ya zauna yana cewa

"Me Jan Zad take kalla??

Mimi ta kalla kafin ta kalli Anty Anny ta rage muryanta tace

"The one and only Ya Ammar Zad"

Mimi na jinsu farin ciki ya sake cikata tai sallama da wayarta ta kashe ta ajiye tana kallan Ammar din daya zauna kusa da ita yana daukan cup din fresh juice da akai na gida ya kai bakinsa yana cewa

"Mimi barka da rana"

Kafin ta amsa Jannah ma tace

"Sannu da fitowa Mimi"

Anny ma gaidata tai ta hada duka gaisuwar tasu tai musu amsawa daya tana cewa aci abincin tukuna wani zancen.
##MAMUH
#JANNAH ZAD
#AZIZ AY LIMBA
#AMMAR ZAD
#BESTLOVE STORY
#CRAZYLOVE
#BILLIONAIRES WAR


ZAFAFA BIYAR

KALBIM 500
mamuhgee

A DUNIYATA 500
Huguma

AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul

KIRJIN ME HANKALI 500
Miss xoxo

Pay at
0022419171 AccessBank
Maryam sani gummi

Shedan biya
09033181070

Or mtn vtu at
09032345899
[27/12/2024, 3:20/ pm] MG: *_Arewabooks@Mamuhgee_*
28
*_LADIES COLLECTION AND MORE_*
08169307477
SHIN MATSALARKI RAMA CE KO KINA SO KI GYARA BREAST DINKI NE?
KINA SO KIYI HIPS HAJIYATA KIYI KYAU?
KO KUWA KINA SO KI RAGE KIBARKI KO TUMBINKI?
KINA SON INGANTATTUN MAGANIN MATA NA GARGANIJIYA?
Kinason shape dinki ya fito kamar yanda kowace mace zatai alfaharin ganinki bare ma oga ko saurayinki da kansa,
Shin kinason ko koma yar dagwas dinki batareda kashe kudin surgery ba kokuma hana kanki cima da dama da kikeso sbd kinason jikinki yayi daidai?

To matsalarki tazo karshe indai ingantattu sahihan maganin gargajiya ne da muka san inganci da gaskiyarsane,

MAZA KI ZIYARCI LADYS COLLECTION AND MORE ko ta waya ko ta asalin inda take ki tabbatar da Buqatarki tazo inda zata biya insha Allah,

LADY'S COLLECTION AND MORE

ANAN NE ZAKI SAMU DUKKAN ABUBUWAN DA KIKE SO KAMAR HAKA =?G?
Zumar kiba
Zumar breast
Zumar hips
Zumar infection
Zumar sliming
Zumar sabon budurci
Back to virgin
Abayas
Atamfa
Less
Hijabs
Supplements
Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko

08169307477

Address bayan gidan drugs katsina State

Kayan mu masu inganci ne sosae

Muna aika kayanmu a ko Ina ba tare da wata matsala ba=?O? SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA=د?


***********
Da asuba jirginsu ya sauka Sayyid yana a sanyaye baida wani kuzari ko yin abinda ya wuce bin bayan Alh saad sawu kan sawu sbd kansa dayaji yana juyawa samun kansa a baqon guri inda bai taba tinanin zuwaba ko samun kansa ga jajayen fata tako ina suna wuce suna sake saka kansa juyawa amma ya daure babu abinda yake buqata irin ganin ABDULAZIZ LIMBA.


Mota suka hau wadda kai tsaye takaisu train station suka siya ticket din zuwa Milan wanda acan ABDULAZIZ din yake.

A train ma wata sabuwar duniyar Sayyid yake kalla wadda tale sake juyar da kansa sedai ko dagowa bayayi kansa na qasa Allah yasa kayan sanyi ne masu kyau da kauri a jikinsu dagashi har Alh saad dan haka rashin wayewansa da gurin ya boyu shi kuwa Alh Saad dayake gogagge ne a yawon qasashe sam babu abinda ya damesa sajewa ma yayi dasu banda banbancin fatar amma turancinsa dayakeyi hankali kwance cikin qwarewa yana waya da wanda zai kaisa har gidan ABDULAZIZ

Tafiya sukai me dan tsayin data saka Alh saad jin daya sani flight suka sake bi zuwa milan din..

Suna sauka daga train Station daga nan kai tsaye motace ta daukesu zuwa Address din Fash wanda yake abokin karatun ABDULAZIZ tin abaya amma yanzu basa tare amma yasan sabon gurin dayake zama yanzu sbd dukkaninsu sun zama busy kowa ya samu success din dayake nema.

Koda suka isa gidansa cikin sakewa ya tarbesu tareda riqesu sukai sallolin dasuke kansu sukai breakfast wanda daqyar Sayyid ya tura abincin a cikinsa sbd ba cimarsa bace hakama zuciyarsa kwata kwata a sanyaye take ba dadi ko kadan nauyi yakeji a kirjinsa.

Wayar ABDULAZIZ din shima Fash ya ringa kira ko zaa dace amma still bata shiga ba kuma a lokacinda Alh saad ya kirasa baya qasar shima bai dade da dawowa ba dan haka bai samu zuwa ya dubo lfy ba kuma yayi masa gaisuwar babban rashin da yayi wanda duk wanda yasan ABDULAZIZ sanin daya wuce awanni to tabbas zaisan Ummitah itace rayuwarsa,jarumtarsa kuma karfin dayake riqe dashi a duk gwagwarmayar rayuwarsa hakama duk abinda yakeyi a rayuwarsa sbd cigabanta da ingatata yakeyi.


Saida suka nutsu sosai kafin suka fito a motar fash din zuwa gidan ABDULAZIZ.

Tin a mota sukai tsit babu me magana sai fash din dayake dan kokarin ragewa yanayin nasu damuwa da cewa

"Insha Allah lafia kalau sbd LIMBA yana hakan so da dama idan yana son kadaicewa baya son damuwa"

"Ummnh" kadai Alh Saad yace yana kallan hanya sbd baida abin fada.

Sayyid kuwa shiru har lokacin bai iya cewa komaiba hakama ko kallan gari baida Nutsuwar yi.

Shiru Fash yayi ganin yanayin baya buqatan karfafawa shiru kawai kowa yake buqata.

Tafiyar mintina kusan 40 sukai kafin suka isa dogon building din da gidan ABDULAZIZ yake ciki.

Parking fash yayi yana gaisawa da securities din wajen da suka bude musu hanyar shigowa fededen harabar gurin.

Fitowa sukai dukkaninsu fash da Alh saad ne a gaba suna magana
Sayyid dai har lokacin bai iya dago kansa sosai ba bayansu kawai yakebi a natse babu kuzari.


Lift suka shiga zuwa saman Fash na daga wayarsa da ake kiransa.

Suna isa floor din dayake suka fito fash yana kashe wayarsa suka tsaya kofa tareda sauke ajiyar zuciya ya miqa hannunsa ya danna Door bell dake qara mara damuwa da karfi.

Kofar suka zubawa idanuwa dukkaninsu suna jiran fitowansa.

Sake dannawa Fash yayi yana gyara tsayuwarsa.

Shiru babu motsin alamar bude kofar,

Sake dannawa Fash yaci gaba dayi yana shiga mamaki.

Mintina suka dauka a gurin sunata bugawa babu alamar zaa bude din babu ma alamar akwai mutum a ciki.

Saukowa qasa sukai suka nufi gurin receptionist din building din dake qasan

Fash ne ya kalleta yana mata sannu kafin ya sanar da ita gurin wanda suka taho.

Kallansu tayi dukkaninsu da mamaki kafin ta tsayar da kallanta kan fash da shine a gabanta tace

"His family????

"Yes" yafada yana nuna su Alh saad din wanda shima Alh saad din matsowa yayi yana amsa gaisuwarta kafin tace

"Baya nan for morethan 2 month yana asibiti likitansa yazo ya tafi dashi,
Mutuwa yakeyi ciwo yake sosai.......

Kallanta Alh saad yayi da sauri yana juyowa ya kalli Sayyid wanda bayajin abinda suke fada yana dan nesa kadan hakama turancin ba duka ya iyaba.

Fash cikin Yanke zancen yace wane asibiti and the name of the doctor.

Basu tayi cikin sauri sbd basuda tabbacin ko zuwa yanzu LIMBA din ya rasu sbd a yanda aka bar nan dashi batajin ko kwana daya zai qara a duniyar.


*****A ranar kunnuwansa basu gama sauraron maganar Alh Saad ba yaji tsit bayajin komai jinsa na daukewa ahankali,

Ganinsa ma Fara daukewa yayi qafafunsa ma mutuwa suka fara yi suna gaza daukansa hannuwansa da suka dauki rawa suma mutuwa suka farayi harsuna kashe wayar wadda ta zame daga hannunsa ahankali shida wayar suna zubewa agurin paralyse na kamasa a take.

Buguwa kansa yayi da centetable din dayake tsakiyar palon take jini ya feso daga g???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?efen fuskansa datai mugun buguwar idanuwansa da suka mummunan sauyawa a take na kafe akan wayarsa dake gaban fuskansa batareda ya kafta ba.

Zuciyarsa kokarin dena bugawa takeyi sbd mummunan bugun datai wanda ya sakar masa paralys na take,

Wani irin Radadin da baya misaltuwa ne yake ratsa zuciyarsa dake neman bugawa ta dena aiki gaba jininsa na gangarowa daga gefen goshinsa yana shiga har cikin idanuwansa da suka kafe akan waya bai iya motsa ko dan yatsantsa sbd babu abinda yake aiki ajikinsa bayan zuciyarsa datake matsanancin ciwo da radadinsa yake juyar masa da kai kafin ahankali idanuwansa suka rufe ruf ba alamar rai a jikinsa.


A haka ya wuni a gurin kwance babu alamar rai a jikinsa harya kwana a gurin kwance babu taimakon kowa sbd babu wanda yake shigowa building din saida kwakwaran sanin gurin wa akazo

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login