Showing 6001 words to 9000 words out of 101092 words

Chapter 3 - Zanyi biyayya COMPLETE HAUSA NOVEL

FEENER   

03 Sep 2024

37763

Aure suzo suna jininita maganar, don haka yace shi zai kai kayan,
Domin yasan halin kannen shi mata sam basa son talaka musamman wadda ke Auren sultan of sokoto, tsabar tashin hankalin da suke ciki kota kan kayan basubi ba ranar, malam bala yayi kuka har yaba uku lada, RAHAMA ma kuka take tayi ganin iyayen su na kukan tozarcin da Y'ar uwar ta tayi musu Aure saura kwana hudu ta gudu me take nufi da wannan cin zarafin da tawa mahaifin su,

Gaba daya ya rasa ta inda zai bullowa lamarin washe gari ma haka suka tashi Aliyu ya bazama duk inda yake Sa ran zai ganta bai ganta ba, haka ya dawo gidan, jiki a sanyaye tareda Alkawarin idon shi idon HAJARA sai ya illata ta tunda ta Kunsa musu bakin ciki ta kuma wahalar dasu,
Zaune suke tsakar gidan sunyi jugum inna duk idanun ta sun kunbura saboda kuka haka RAHAMA dake gefe duk jikinta ya yi sanyi ganin iyayen ta cikin tashin hankali,
Aliyu ne yayi karfin halin bude baki yafara magana, " baba ina ganin ka cirewa kanka damuwa HAJARA kanta ta cuta ba muba, ku cireta a zuciyar ku zata dawo duk inda taje zata dawo duniya ce ai,
"Aliyu me nayiwa Ummi da zata yimin irin wannan sakamakon tozarcin, mutanen nan basu kyamace muba mune zamu guje su, duk gatan da ummi keso nayi kokarin bata Amma sakayyar da zatayi min kenan?

Share hawaye yayi tareda kallon su yace "Larai ki zama shaida ta ko HAJARA ta dawo gidan nan bani bata najanye duk hidimata a kanta,
Kuka mai cin rai da kuma tausayin Y'ar uwar ta yasa ta saka kuka tareda riko hannun baban ta tana gunji " baba don girman Allah karka juya mata baya don Allah ka yafe mata baba karta lalace don Allah, tafada duk ta birkice, tareda tsantsar kaunar Y'ar uwar ta da kuma tausaya ma rayuwar da ta jefa kanta,

"RAHAMA, yakirata cikin muryar bada umarni tareda kuma tsantsar damuwa da mika komai ga ubangiji yace " zakiyi min BIYAYYA? Zaki yi biyayyr da Y'ar uwarki ta kasa yimin?
Zabura tayi ta fara girgiza kai tana dafe kanta, " baba karka yimin haka shekaruna shatakwas fa yanzu nake shiga ko secondary ban kammala ba inaso nima inyi zurfi baba don girman Allah baba na kabari inyi karatu irin wanda nake da burin yi,



Cikin tsawar da tsawon rayuwar su basu taba gani ko jin yayi irin taba yace " inkema bazakayi biyayyar ba kibi Y'ar uwarki, duk in sallama ku Alhmdulillah inada magaji a tare dani ko yau zan iya mai Aure ya haifamin jikokin da zasu shafe min ku a zuciya ta,



Kuka ta Kara tareda riko kafar shi tana girgiza kai " ZANYI BIYAYYA wallahi zanyi don Allah ka yafe mana wallahi nayi biyayya bazan watsa maka kasa a idoba, ta matsa jikin d'an uwanta ta rungume shi "yaya don girman Allah kaba baba hakuri na yarda karyayi fushi dani wallahi na karba ZANYI biyayya,
Wani irin hawayen tausayin Y'ar kanwar tashi ne yasa ya rungume ta tareda bubbuga bayanta kadan yace " relax Karki damu baba na Alfahari dake Rahama ke ta daban ce,


Inna ta taso tareda dagota ta rungume ta tace "Allah yawa rayuwar ki Albarka RAHAMA, zakiyi Alfahari kinji kiyi biyayya wata rana sai zakici ribar Abin, Ajiyar zuciya take saukewa saboda kuka ta zauna gefen baba domin ganin sam har yanzu baida walwala domin ji yake ajikin shi itama guduwar zatayi kamar Y'ar uwar ta, don haka ya mike ya fice Abinshi batareda yace musu komai ba,

"Hajara ta cuce mu ta cuci kanta tsawon zama na da mijina bai taba fushi bai karfi ba yau ta Kunsa mai takaicin da ko Y'ar uwar ta bazai yarda da itaba,
RAHAMA ki sharewa ubanki hawaye ki wanke mai zuciya ta hanyar karbar Auren nan,
Hawayen da keta gudu akan fuskar ta ta sharce duk da basa tsayawa ta, "Inna insha Allahu na karba kuma koda zan mutu bazan taba baku kunya ba duk yadda Rayuwar gidan Aure na take zanyi kokarin yin biyayya bazan taba yin Abinda zai zubar muku da mutunci ba,
Tafada tana fadawa jikin inna,
"Nasani RAHAMA ni na haifeku duka nasan tunfarko dake akace baza asamu akasi ba, Allah ya miki Albarka kinji,

Aliyu yayi dariya ya riko ta" come here my lovely sister, ya rungume ta cikeda tausayin his hardworking sister, Am proud of you my sister............ 🖊




*Matar Soja*
🌻🌻
*ZANYI BIYAYYA*
🌻🌻



*By FENERH*


Free page


*ga masu bukatar biya ku hanzarta kar Abaku labari ku biya ku karanta cikin Aminci, 200 ne normal vip 500 kuturo katin ku ta wannan numbar 09011251444 ko ta Asusun banki na 7304736012 nafisa sani Fcmb don Allah vip Kudaina turomin kati idan kana son vip kutura min ta banki katin nayimin yawa sosai in bakuda Account kibayar a pos don Allah sucire charges dinsu a ciki, nagode masoya sai najiku*

9⃣&🔟


Saida taji yunwa na neman kasheta ta mike tareda kallon ko ina a dakin, ba laifi akwai gado da komai a ciki saidai dakin shine daidai zamanta dama, cikin sa'a ta hango d'an karamin mini prige a dakin, tayi saurin matsawa ta bude takoyi sa'a akwai drinks cike harda holandia, ta janyo jikinta na rawa, domin tun rana rabon ta da cin wani Abu, ta kafa kai saida ta shanye tas ta ajiye kwalin zufa ya karyo mata, kofar dakin ta garkame gudun kar wannan mugun ya dawo ta cire hijabin jikinta ta ga dakin baida matsalar komai yama fi mata kwanciyar hankali akan wancan dakin da yake kamar ba za a kwanta kabari ba, shiru tayi tana tuno maganganun shi,
Allah ta mika wa Al amarin ta tareda kudurta duk runtsi bazata taba bari tayi laifin da zai korata gida ba, domin komawar ta na daidai da bacin ran baban ta wanda sam bata fatan shi damara ta daura domin tasan bautar Allah zatayi, da daura damarar yin biyayya duk runtsi duk wuya daga yau bazata taba bari yaga bacin ranta ba ko hawayen ta duk ukubar da ya shirya bata,

Don haka Bathroom ta shiga taga wannan madaidaici ne daga sink sai shower daidai irin wadda tasaba gani ta dauro alwala ta fito, sallloli ta gabatar tareda rokon Allah yabata ikon cinye wannan jarawabar,
Taso ace Qur anin ta na dakin ta karanta Amma tasan ko tana hauka da nad'e nad'e bazata fita waje ba taci karo da beauty but beast, sunan da ta Bashi kenan,
Hayewa gadon tayi tareda kudundune wa cikin hijabin ta, sai bacci,

A ranar tayi wani irin bacci mai cikeda natsuwar da bata tabayin irin shiba duk da rayuwar ta na cikin matsala zama gida daya da namijin da baya kaunar ganin ka,
Gefen Al Ameen kuwa wani daki ya nufa kamar irin nata, yana tunanin dama wannan yarinyar da yake ta nema Y'ar gidan baba bala ce, duk da yasan mutuncin mutumin bai fasa kudurin shi akanta ba ya riga ya gama shirya duk ukubar da zai bata,.

Asubar farko ta mike saboda ta saba ta gabatarda nafila kafin sallar farilla tayi Addu'oin ta, ta mike ta kakkabe kan gadon da ta kwana ta duba ba Abinda zata gyara, ta bude kofar ta fito falon tana lellekawa taga wane aikin zatayi domin ita tariga jikin ta ya horu da aiki batajin zata iya zama ba wani aiki,
Wata kofa tagani can karshe harda labule ya ratsa ta nufi hanyar domin ganin ko kitchen ne a wurin, takoyi sa'a dining ne da kitchen a hade, tundaga kofar kitchen din tayi Hamdala tareda tasbihi ganin na urori daban daban kitchen din ya gama haduwa, tana hango wata kofa ta ci ta matsa ta bude store ne cike tab da Abinci ga manya manyan prige ta bude, daya, namomi ne Kala Kala dayan kuwa kayan miya ne tab da kayan lambu a basket,

Tuni taji tana son ta girka wani Abu da safen nan ko zataji nauyi a cikin ta domin sam bawai ta Koshi bane,
Rayuwar ta kab ta kare ta ne a sonyin duk Abinda ya shafi kitchen, duk littattafanta na girke girke ne wasu domin ita girki is her hubby, fagen kayan wuta ta iya kunna gas domin idan sunje gidan kanwar Inna tanada ire iren wasu Abubuwan amma ba irin wa innan ba, don haka bata sha wahala ba ta shirya indomie sharp sharp taji kayan lambu ta daba ruwan Lipton da yaji kayan kamshi ta soya kwai guda daya domin batason kwai yayi kauri,


Cikin minti kadan ta gyare inda ta bata tsab tareda zama nan taci tayi nak ta wanke komai tareda saka mopa ta goge tiles din kal, tana jin wani irin nishadi,
Kuma duk wannan aikin hijabin dai na nan a jikinta,
Tana gamawa ta dauki abin mopa din tayi falon duk girman shi ta mope shi tas tareda komawa ta nemo towel duk wani Abu saida ta goge shi a falon duk da ba datti,
Tana kammala wa ta koma dakin da aka jefata tayi wanka, Amma tarasa yanda zatayi, kayanta takeson canjawa Amma tana tsoron zuwa wancan dakin kar ya ganta, haka dai ta kuma mayarda na jikinta ta zauna gefen gadon tareda zabga tagumi, yanzu haka ne Auren yake? Haka zata cigaba da rayuwar kadaici ba abokin debe kewa ba wanda zaiji koda muryar ka, wayarta ta tuna tana can dakin a cikin Jakarta, dole ta mike domin tanason waya da inna da kuma ya Aliyu,

Fitowa tayi tana Kara kallon dukiyar falon, kawai taji ta gabza karo, kafin ma ta dago kanta tajita a kasa tim ya hankadata yana kakkabe jikinshi da ta taba,
Saida bayanta ya Amsa saboda unexpected tajita a kasan, ta ce washhh tareda dago kanta ta kalle shi, tayi saurin saukewa domin kayan geming ne a jikinshi yana diga saboda jugging yadawo, cikin tsawa yace
"Are you blind? Kina tafiya kamar makauniya next time kika kuma bari jikin ki ya shafe nawa sai na lahira yafiki jin dadi, kazama kawai tunjiya, kina yawo da kaya daya bana son datti a cikin gidana ki kiyaye and ki wuce ki wanke min bathroom before inyi wanka bana wanka kullum sai an wanke shi, tashi tayi dakyar domin bayanta da ya rike ta nufi hanyar dakin ta domin wankewar ya buga mata uwar tsawa, " bakiji magana ta bane zaki wuce,? "Da Banji muryar rashin kunyar kiba da zance ke kurma ce Amma bakin ki cike yake tab da manyan kalamai kina kwailar ki dake, don haka bina muje ki mun aiki oya,
Yanuna mata hanya, dole tayi gaba tanayi tana hardewa yabi bayanta, kofar datagani ta tura tashiga, komai na cikin dakin irin na wancan ne don haka saida gabanta ya fadi ta ina zata fara?
Jin motsin shi yasa ta wuce hanyar bathroom din ta tura, hijabin ta ta nade saman west dinta ta daure tareda daukar bucket ta Tara a fanfo ta debo ruwa ta fara wanke wurin da baida datti ko kadan, tsab ta wanke ta fito yana zaune da laptop a cinyar shi yana duba sakonnin da ya dade bai duba ba, hotunan da yafara cin karo dasu ya kurawa idanu domin yagan su kusan hamsin yanzu kusan sati biyu ana turamai kullum bai taba dubawa ba,
Tsaki yaja " classless ya fada tareda delete gaba daya ya rufe ya mike batareda ya kalleta ba " clean this mess yafada domin ko ina dakin ya watsar da kayan da ya cire da ma wa inda batasan ina suka fito ba,

Dukawa tayi ta fara kwashe kayan ta gyara tsab ba musu ta duba closet ta mayarda sauran tareda mamakin ina zaikai sutura duniya, cikin Sauri ta rufe ta dawo kan cycle bed din da yayi kamar Anyi dambe akai ta kakkabe tareda gyara bedsheet din cikin Sauri domin tafita kar ya fito,
Da sauri sauri ta gama zata fita taji yace "wait, tayi saurin juyowa, tuni ta Dukar da kanta kasa ganin yanda ya fito da kirjin shi a bayyane d'an guntun towel ne a jikin shi gaba daya kirar shi tsoro ta bata namiji ne da baka iya kallon shi sau biyu saboda cikar zati da haiba, uwa uba kwarjini da kyau, yanda ta Dukar da kanta kasa yabashi haushi yasa ya matso dab da ita,
"Dago kanki yafada cikin tsawa, ba shiri ta dago, "me kike gudun kallo a jikina? Inada muni ne da zaki kasa kallo na? " ok I understand saboda karkisa ran zan dora miki shi ko never this chest is precious, ko yatsan ki ba zai taba shiba bare banzan busashen jikin ki,
Wallahi an cuceki nima an cuceni da za a min aure da premature sai uban rashin kunya da kika iya, ko gaisuwa ma bakisan yanda akeyin taba,.
Muryar ta na shaking tace " ina kwana? Hold it bana bukata out of my room, yafada yana nuna mata hanya da hannu da gudu ta fita,

Tana dafe kirji, " iya Abinda yake tunanin zaiyi min kenan da sunan horo? Murmushi tayi domin wanna is not a punishment, aikin tane kuma zata iya har karshen rayuwar ta,
Shikuwa kallon dakin yakeyi yanzu duk Abinda ya baza ta gyara cikin lokaci kadan kamar injin, domin yasan aikine mafi wahala a wurin Husna idan tamai laifi horon da yake bata domin batason aiki,
Shiru yayi yana tunanin aikin da zai bata next da zata wahala,

Ita kuwa can dakin ta, shiga ta kwaso duk Abin bukatar ta ta mayar dakin da ya kaita ta tsoffin kayanta na gida duka da aka kawo mata ta kwashe ta shirya a waldrop din tareda jera littafan ta gefe guda,
Cikin natsuwa ta ke komai tanajin sanyi a zuciyar ta saida ta kammala ta nemi wasu kayan ta canja wanda ta cire ta shiga bathroom ta wanke harda hijabin ta shanya a ciki, bata kuma jin motsin shiba
Har rana Y'an Uwan inna suka kawo mata kayan garar ta tareda wasu kayan ta suka yimata sallama domin duk yau zasu tafi, ji tayi kamar ta bisu taga su inna Amma ba Abu mai yuwuwa bane dole ta hakuri, bayan tafiyar su ta nemo wayarta tayiwa yaya Aliyu plashing, yako kirata sukasha hirar su yana Kara yimata nasihohi, tace yakaiwa inna sugaisa, yace baya gida Amma zai turo mata kati tasa takira numbar ta, ai kuwa transfer ya mata Dari Biyar ta Kira inna taji muryar ta,
Alhmdulillah batada matsalar komai domin sam ko duriyar shi bataji a gidan sam iya kacin ta gyaran gidan da girkawa cikinta duk Abinda taso ta kuma yi karatun ta wani lokaci har baccin rana takeyi saboda hutu,
Sam bata lura da baya gidan ba domin yaje meeting Abuja saida Husna tazo gidan bayan kwana biyu take cewa yaya yau zai dawo, banga kina shiri ba irin na matan da mijin su yayi tafiya,? "Tace wai baya nan ne?

Kallon ta Husna tayi, wato suna gidan Amma batasan ma baya gariba, shiru kawai tayi domin ta lura tun zuwan ta taga dakin da RAHAMA take taji ba dadi don haka ta kudurce sai ta yi wani Abu akai, duk da RAHAMA akwai duhun kai Amma zataso ace ta fito ta shigo gari yanda zata janyo hankalin Al Ameen ko baiwa Allah, don haka cikin hilata tasa RAHAMA ta d'an saki jiki da ita har ta fahimci wato zaman nasu na I don't care ne,


Ina labarin HAJARA?

Bayan tarewar RAHAMA da sati daya ta dawo gidan, lokacin baba baya gida Aliyu ne zaune gefen inna duna hirar su cikin farin ciki tana yanka Alaiyaho, ta yi sallama hankalin ta kwance, ta nufi hanyar dakin su tana "sannun ku inna yaya barka da rana,
Ai kuwa wani uban tsalle yayi ya shakota tareda bugata da gini ya fara kwance belt din kugun shi,
Ta fasa ihu domin ta bugu, inna tace inka bar yarinyar nan tayi numfashi sai na ci mutuncin ka, ai kuwa ya fisge gyalen ta yafara narkar ta kamar Allah ya aikoshi saida ya mata ligis yana kokarin saka kafa ya take ruwan cikinta baba yayi sallama,
"Subuhanallah haba Aliyu mezangani haka? "Baba wanna yarinyar don ta raina mutane taje yawonta ta dawo ta shigo gida hankali kwance kuma inkyale ta ai wallahi baba kabani izini in karasa ta kowa ya huta,
Assha haba d'an Albarka, bayan ka gama yimin BIYAYYA ina fatan kadace duniya da lahira zaka bata aikin ka, ai Ali duk wanda yace zai iya hadiye gatari sakar mai bota kagani,
Wuce zuwa harkar babanka Allah yama Albarka kaji, Ameen yace ya mayarda belt dinshi ya fice, inna taci gaba da Abinda takeyi baba ma ko gefen ta bai kuma kallo ba ya shige dakinshi,
Iya buguwa ta bugu domin tsawon rayuwar ta ba a taba narkar ta irin haka ba don haka dakyar taja kafar ta tayi dakin su tana jinyar jikinta,

Tareda lumshe idanun ta ta sharce hawaye " please A yabo accept me kazo muyi Aure inbar musu gidan su lokacin ne zasu meme ni, tafada tana Kara ciro wayarta da ta tsage yanzu saboda baduwar da tayi ta fara bude data ta ganshi online a Facebook,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login