Showing 267001 words to 270000 words out of 299804 words
sauƙa bisa fuskar Ummey.
Jiki na rawa ya juyo ya kalli Sheykh dake mgn cikin rawan murya da rauni yake cewa.
"Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Yah Allah na gode maka bisa wannan rahama da kaimin ko yau ka ɗauki raina burina ya cika, yau gani ga Mameyna a cikin masarautar Joɗa a suffar mutun bani Adam ba tsuntsuwar Boleru ba".
Wani irin kuka ne mai rauni ya kwabce mishi.
Yah Jafar ma kuka yakeyi tare da cewa.
"Alhamdulillah al'ƙadarin Magauta ya karye".
Ummi kuwa da rarrafe ta rusuna gaban Ummey tare dayin ƙasa da kanta cikin rauni tace.
"Barka da dawowa Adalar Uwar gijiyata".
Umaymah kuwa da sauri ta jawo wayar da ta gani kusa da ita.
Saida ta danna sai taga ashema wayar Hibba ce da ta bawa Junainah nayi Game.
Jadda ta dannawa kira.
Yana ɗagawa tace.
"Assalamu alaikum Alhamdulillah Allahu Akbar Jadda! Jadda!! Jadda!!!".
Cike da kaɗuwa Jadda dake kishinƙiɗe ya miƙe zaune tare da kallon Sitti dake yanka mishi lemu wanda tana iya jiyo abinda Umaymah ke faɗa sabida yadda take mgn da ƙarfi.
Wani irin dogon numfashi suka sauƙe a tare jin Umaymah na cewa.
"Alhamdulillah Jadda Aunty Mamey ta dawo Jadda zatonmu da tsammanin mu ya zama gsky Aunty Mameyna ta dawo gata gabanbu Jadda kace Alhamdulillah".
A tare Jadda da Sitti suka fara maimaita kalmar hamdala.
Affan kuwa cikin wani irin sauri ya juya a guje tamkar ƙaramin yaro ya nufi Part ɗin Abbansu.
Yana shiga da gudu yana mai cewa.
"Abba Abbanmu Abbana Mamey Mamey".
Da sauri Gimbiya Samira amaryar Abban ta fito tare da cewa.
"Affan lfy kuwa Abbanku yana fada".
Ai bai kuma bin ta kanta ba ya fito.
Kiciɓis yayi da Hajia Mama tana cewa.
"Kai lfy kuwa kake gudu kamar yaro?".
Ba tare da ya tsaya ba yace.
"Abba nake nema ina yaje Mamye."
Daga nan ya nufi fada.
Ita kuwa Hajia Mama cikin wani irin masifeffen tsinkewar zuciya da fargaban jin sunan da bata ko son jin an kira ta juya ta nufi ɗakinta.
A can fada kuwa bayan sarkin ƙofa yayiwa su Bappa iso cikin ƙaton falon.
Abboi na gaba Bappa da Arɗo Bani da Alhaji Haro suna biye dashi a baya kana sai masu tsaronshi da suka tsaya can bakin ƙofar shiga sabida dakatar dasu da yayi.
Suna shigowa Lamiɗo dake fuskantar Kofar shiga fuska cike da annuri da haiba yace.
"A a a Masha Allah lalle marhabin da Alhaji Abbo lale da zuwa masarautar Joɗa Fulle bandu fullo".
Da sauri Wambai, Dirankadi, Ɗan isa, Ɗan buram, Sarkin fada, Ɗan kade, Galadima Ɗan maliki Chiroma Durbi Ma'aji. Duk suka miƙe tsaye cikin tsananin sakin fuska da alamun sanayya na mutuntaka suka kalli Abboi tare da haɗa baki wurin cewa.
"Marhababika da zuwa masarautar Joɗa".
Sai kuma ɗan zagi ya fara baza rigarsa tare da cewa.
"Sarki ya gaisheka. Sarki yace ayi maka sannu da zuwa fullo Nbandu fullo manyan fada na farin ciki da zuwa ka".
Wani irin murmushi Abboi yakeyi mai cike da kamala ya nufi gaban Lamiɗo.
Har kusa dashi ya isa kana ya rusuna, yayinda Bappa da sauran ke biye dashi a baya.
A hankali ya sunkuyar da kanshi tare da ture hularshi yayi baya da ita.
Cikin alamun shaƙuwa Lamiɗo yasa hannunsa tsakiyar kansa tare da cewa.
"Allah yayi muku al'barka".
Murmushi Abboi yayi tare da cewa.
"Amin ya Allah Baba".
Sabida Lamiɗo yasan Abboi a matsayin ɗansa yake zuwa gareshi yana jin daɗin abokin mahaifin nashi ya sanya mishi albarka".
A hankali ya koma ya zauna ya tanƙwashe sawunshi tare da cewa.
"Barka da hatsi".
"Barka dai".
Lamiɗo yace.
Abba dake gefenshi ne ya kalli Abboi tare da bashi hannu suka gaisa.
Sarkin fada kuwa da sauri ya fito ya umarci hadimai maza da su kawowa baƙin abin taɓawa ai kuwa nan da nan aka cika gabansu Abboi da abubuwan ci da na sha.
Cikin tarin kula Lamiɗo ya kalli Bappa tare da cewa.
"A a Malam liman tafe kuke tare da shine?".
Cikin nitsuwa Bappa yace.
"Na'am tare muke".
Kai Lamiɗo ya jinjina tare da kallon Abboi gyara zama Abboi yayi fahimtar tambayarsa Lamiɗo yayi a hankali yace.
"Ai mutumin ƙasar mu ne zamane da wani babban dalili ya dawo dashi nan ƙasar ku".
Cikin gamsuwa Lamiɗo yace.
"Makiyayinka ne shi?".
Cikin mutuntaka da kunya Abboi yayi shiru dan shi Bappa yafi ƙarfin makiyayinsa a wurinsa Bappa ɗan uwane".
Cikin yin murmushi Bappa yace.
"Eh ni ɗaya daga cikin makiyayansa ne".
Yayi mgnar sabida fahimtar Abboi bazaice hakanba.
Sai kuma suka sake wani sabon gaisuwa.
Nan Babba ke cewa.
"Tare muke da mai ɗauki shi da kuma ƙanwata sunzo ganin jikar tamu su sun isa can".
Cikin tarin jin daɗi Galadima yace.
"Masha Allah, Allah ya bada ladan ziyara".
Amin Amin duk suka amsa.
Dai-dai lokacin kuma Affan yasa hannunshi ya ture sarkin ƙofa dake tareshi yana cewa.
"Lamiɗo yana ganawa da manyan baƙi".
Cikin haki da ɗaga murya yace.
"Kai da Allah bani wuri. Abbana nake nema Abba! Lamiɗo!".
Yayi mgnar da ƙarfi tare da kutsa kai cikin falon.
A tare suka juyo suka zuba mishi ido Abba kuwa da sauri ya miƙa tare da cewa.
"Na'am Affan meya faru?".
Cikin haki yace.
"Abba Mamey Lamiɗo Mamey'nmu ta dawo wlh Mamey ta dawo gata can a Part ɗin Hamma Jabeer su Umaymah nata kuwa Mameynmu ta dawo a mutun ba tsuntsuwar Boleru ba".
Kusan a tare gaba ɗayansu suka miƙe banda Lamiɗo dasu Abboi tare da cewa.
"Kai Affan nitsu ka gaya mana".
Cikin kaɗuwa ya kamo hannun Abban nasu tare da cewa.
"Zo muje ka gani wlh Mamey na ta dawo a mutun ba tsuntsuwar Boleru ba".
Ai kafin ma ya rufe baki Abba ya juya da sauri yabi bayan Abbanshi.
Abboi kuwa da Bappa da Arɗo Bani da Alhaji Haro kallon juna sukayi tare da yin murmushin zatonsu ya tabbata jinjinawa juna kai sukayi
Sai kuma Bappa yace.
"Ya ilahi meke faruwa?".
Cikin yin Murmushi Lamiɗo yace.
"An tashi taron fada sai gobe".
Nan take duk sauran suka miƙe suka fita kowa ya nufi muhalli sa cike da alhini.
Shi kuwa Lamiɗo Galadima ya kalla tare da cewa.
"Muje gidan Jabeer ɗin Kuma taso muje ƙofar surkin naku".
Yayi mgnar da yaƙini a ransa su Bappa ne ke tafe da abinda suka daɗe suna tsumayin wato dawowar Mamey (Ummey) kenen.
Ai kuwa da sauri su Bappa suka bi bayansu.
Fadawa na musu rakiya.
Ɗan zagi na baza riga da cewa.
"Gyara kimtsi, sarki ya gaisheku".
A haka suka nufi Part ɗin Sheykhhhh.
Kusan a tare suka isa dasu Abba dan rawan da jikinsa keyi ya hana masa yin sauri.
Lokacin ɗaya kuma duk masararutar Joɗa ta cika da lbrin dawowar Mamey kamar yadda labarin juyewarta da bacewarta ya karaɗe ko ina na Masarautar Joɗa.
Suna shiga Affan yaja hannun Abbansu har gaban Shatu da Sheykh wanda ke ruggume da Ummey har yanzu a sume.
Sun kasa taɓuka komai, duk da shi dai Sheykh ya gane a sumen take.
Cikin haki Affan yace.
"Gata Abba ka gani ga Mameynmu".
Wani irin farin ciki ne mai masifar yawa dake shirin ɗauke masa numfashin sa ne ya sauƙo mishi, jin hakane yasa yayi sauri ya sunkuya a tsakiyar falon ya fuskanci al'ƙibla ya faɗi yayi sujjada gaban Ubangijin talikai sarki buwayi gagara misali.
Dai-dai lokacin su Lamiɗo suka shigo.
Ganin Bappa ne yasa kukan Shatu tsananta murya na rawa tace.
"Bappa Ummey na Bappa Ummey na".
Da sauri irin na sarakuna su Lamiɗo suka ƙara so wurin.
"La ha ila ha illalalhu Muhammadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallam".
Suka faɗa a baki a haɗe tare da zama bisa kujera.
Cikin sanyi Bappa ya kalli Shatu kana a hankali ya juyo yankallesu gaba ɗaya hawayene cikin a fuskarsu.
Ga Jamil a sume.
Galadima kuwa da Lamiɗo murmushi sukeyi tare da maimaita ƙalmar hamdala".
Da sauri Junainah tazo ta faɗa jikin Bappa tare da sakin kuka tace.
"Bappa Ummey na ta rasu ne?".
Da sauri ya jujjuya kanshi tare da juyowa ya kalli Khadijah ƙanwar Shatu cikin sanyi yace.
"Khadijah in akwai zam-zam a gidan kawo min in kuma babu bani ruwan sanyi".
Da sauri Ummi ta miƙe kitchen ta nufa tana mai cewa.
"Akwai zam-zam bari in kawo".
To kawai yace mata.
Abba kuwa a hankali ya ɗago kanshi kana ya jingina bayanshi da sawun Lamiɗo ya kife kanshi bisa guiwar Lamiɗo sai ga wani kuka mai rauni ya subce mishi.
Da sauri Bappa ya amshi goran zam-zam mai sanyin.
Matsowa yayi kusa da Shatu.
Da sauri ya buɗe goran zam-zam ɗin ya tsiyayi sassanyan ruwan a tafin hannunsa, kana ya saita fuskarta tare da cewa.
"BISMILLAHI".
Ya watsa mata shi a fuska da ƙarfi tare da sunan Allah.
Shiru babu motsi da sauri ya sake tsiyayo wani ya watsa mata tare da bismillah.
Stiil ba motsi da ƙarfi ya kuma watsa mata a karo na uku.
Da ƙarfi taja wani irin nannauyan numfashin mai tsawo tare da cewa.
"La'ilahaillaha Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam. Astagafirullaha wa'atubu illaik".
Kusan a tare gaba ɗayansu falon suke furta Alhamdulillah.
Cikin wani irin yanayi Jabeer, Jafar, Jalal, da Jamil wanda Bappa ya watsa mishi ruwan ya farfaɗo a firgice suka matso gabanta sukayi mata zobe.
Kana Umaymah da Mamma da Aunty Rahma suna kusa dasu.
Cikin wata iriyar murya mai raunin amo Sheykh ya kamo hannunta murya na rawa yace.
"M...mah..Mam.. Mameyyy".
Da sauri ta ɗago jajayen idanunta da tsananin ciwon kai ya rinasu ta watsa masa su cikin nashi ba tare da ta amsaba.
Cikin rauni ya kuma cewa.
"Mamey Mamey na Jabeer ɗinki ne! Mamey kin manceni ne, gani Ga Yah Jafar ɗina ga sakalallun tagwayenki ga Affan ɗinki ɗan lelenki ga Abba na Ga ƴan uwanki Umaymahna ga Mamma na ga autar Sitti Aunty Rahma Mamey Jabeer ɗinkin ne ga Ummi amintacciyar jakadiyarki mai riƙon amana".
Shiru sukayi baki ɗayansu suka zuba mata idanu.
Ita kuwa ido ta lumshe wasu hawaye masu ɗumi suka zubo mata cikin raunin murya tace.
"Alhamdulillah Jabeer na tunoku gaba ɗayanku".
Wani irin farin cikin ne mai tarin yawa ya cika musu zuƙatansu baki ɗayansu.
Da sauri suka juyo suka kalli Bappa da yake cewa.
"Alhamdulillah baiwar Allah ta tuno baya ta gane ƴaƴanta da ƴan uwanta".
Da sauri Sheykh ya juyo tare da kamo hannun Shatu wacce cikin kuka da rarrafe ta matso gaban Ummey da kyau murya na rawa hawaye na zuba tace.
"Innalillahi shike nan Ummey ta tuna baya kenan Bappa zata mantani kenan?".
Wani numfashin Ummey taja tare da zubda hawaye.
Ita kuwa Shatu kamo hannun Junainah tayi cikin rawan murya hawaye na kwarya tace.
"Ummey ki kalleni Ummey nice Shatunki fa Ummey koda zaki tuna baya kada ki manceni Ummey kalleni fa nice Shatunki kalli Junainah'nki ƴar autarmu Ummey koda zaki manceni dan Allah kada ki mance Junainah ke kika haifeta a cikinku muka reneta bata san kowa ba sai nudake".
Wani irin kuka ta saki mai ƙarfi tare da jawo Junainah da itama kukan takeyi juyowa tayi ta kalli Yah Sheykh cikin rawan murya tace.
"Ummey nane fa da tun inada shekaru takwas a duniya na bar gaban Dedde na da Abboi na na dawo gabanta ita ta raineni kamar Uwa itace ta haifi Junainah itace ta bamu tarbiya sanadinta muka baro ƙasar Cameroon muka dawo Nigeria muka zauna Rugar Bani wayyoooooooo Allah na Ummeyna kada ki manceni".
Shirun da Ummey tayi yasa gaba ɗaya tausayin Shatu da Junainah yasa kowa zubda hawaye sabida fargabar kada fa ya zamo ta tuno baya can ta mance yanzu.
Kuka sukeyi baki ɗayansu hatta Afreeen dake hannun Aunty Amina kuka takeyi.
Cikin rawan murya Shatu ta kamo hannun Ummey ɗaya Junainah kuwa ta kwantar da kanta bisa cinyar Ummeynta a tare suka haɗa baki wurin cewa.
"Ummey kin mance mune?".
Da sauri Shatu ta saki wani irin kuka tare da faɗawa jikin Ummey jin tace.
"Ban mance kuba Boɗɗo na Autata".
Murmushi sukayi baki ɗayansu falon ita kuwa Shatu da Junainah kukan farin ciki sukeyi.
A hankali Bappa yasa tafin hannunshi ya share hawayensa dake gangarowa hakama Abboi sai suke tuno kamar yau suka samu ɓoleru'n nan.
A cikin masarautar Joɗa kuwa gaba ɗaya labarin dawowar Mamey ya riski kunnuwan mutanen cikinta da kewaye.
Cikin wani irin mamaki Gimbiya Saudatu ta miƙe tsaye tare da kallon Babba Basiru daya kawo mata lbrin cike da kaɗuwa tace.
"Kai Basiru muje mu gani".
Ai kuwa da sauri suka juyo suka nufi Part ɗin Sheykhhhh.
Yayinda Babban ɗan ta Yah Hashim da Laminu mai binshi suka mara mata baya.
Gimbiya Samira ma amaryar Abban da Mom mai bin Mamey da sauri suka nufi Part ɗin Sheykhhhh ɗin.
Gimbiya Aminatu da Matar Galadima ma jiki na rawa suka nufi can.
Hajia Mama kuwa wani irin ihu tayi tare da rugawa a guje ta nufi Part ɗin Sheykhhhh a gigice.
Baba Kamal da ɗansa Sulaiman da sauri suka nufi can.
Dr Aliyu ma da matarsa da ƴarsa Rahima da sauri suka nufi can.
A cikin falon kuwa da sauri Shatu ta amshi gorar zam-zam ɗin da Bappa ke miƙa mata, ta sawa Ummey ita a baki.
Sosai tasha kana ta janye goran.
Da sauri ta miƙowa Aunty Amina hannu alamun ta bata Afreen miƙo mata ita tayi.
Ita kuwa amsa tayi kana ta miƙa wa Ummey ita tare da cewa.
"Ummey sa mata al'barka tunda kece kaka mahaifiyar uba da mai renon Uwa sai ki bawa Dedde na ita tasa mata al'barka itama".
Murmushi Ummey tayi tare da amsarta sai kuma ta kalli Sheykh tare da cewa.
"Jabeer na ya girma".
Murmushi dake baiyana tsantsar jin daɗi sukayi.
Nan suka ɗanyi shiru jin Lamiɗo yayi gyaran murya tare da cewa.
"To Alhamdulillah wannan shi ake cewa ƙudurar Ubangiji babu bawan daya isa kaudashi.
Sai kuma ya kalli Bappa da tare da cewa.
"Dan Allah malam Liman bani lbrin yadda akayi Aisha ta kasance tare daku da kuma sanadin haɗuwarku da samun lfyarta?".
Cikin sanyi Bappa yace.
"Bazamu bari ta hutaba tukun?".
Da sauri Ummey ta jujjuya kai tare da cewa.
"A a Bappa gaya musu kawai domin nasan gaba ɗayansu wannan tambayarce a ransu.
Duk da zanso inji ya lbrin Jaddana da Sittina naga kowa sune ban ganiba".
Cikin sauri Umaymah tace.
"Aunty Mamey Jaddanmu da Sittinmu suna lfy suna gab da tasowa zuwa nan suma".
Cikin tarin farin ciki tace.
"Alhamdulillah to Bappa gaya musu ko ince gaya mana meya faru?."
Shiru Bappa yayi sai kuma ya kalli Umaymah dake cewa.
"Dan Allah gaya mana a wacce suppar ka samu yar uwata a wani yankin".
Cikin nitsuwa Bappa ya gyara zamanshi kana ya ɗan yi gyaran murya a hankali yace.
"Ranar wata jumma'a data gabata tsawon shekaru goma sha uku a can ƙasar Cameroon a yanki dake gefen babban birnin Yahunde cikin Rugar Arɗo Babayo...!
Da sauri suka juyo suna kallon bakin ƙofar shigowa sabida jiyo muryar Hajia Mama daga nesa tana cewa.
"Zancen banza zancen wofi kenan ta yayama za'ayi ta dawo mutun har ta dawo nan cikin masarautar Joɗa".
Ta ƙarashe mgnar da ƙarfi tare da banko ƙofar ta shigo a fijajan.
Yayinda duk sauran tawagar masarautar Joɗa ke biye da ita a baya.
Tana shigowa tayi wani irin zabura tare da zaro idanunta gaba ɗaya sai kuma tayi kan Ummey da gudu.
Da sauri Shatu ta miƙe ta tsaya gaban Ummey tare da cewa.
"Da dakuka cutar da ita kuka fitar da ita haiyacinta da halittar ta a zatonku a haka zata tabbatane?".
Da sauri Sheykh yasa hannunshi ya kamo na Shatu yajata ya zaunar da ita.
Ita kuwa Ummey idanu ta zubawa Hajia Mama tamkar zata manna matasu a jikinta sai jujjuya kai takeyi.
Ita kuwa Hajia Mama ganin idon Ummey cikin natane yasa duk wani sihirinta ya dawowa jikinta kamar yadda Ba'ana yace musu zai bawa Ummey mgnin ƙaiƙayi koma kan masheƙiya duk randa tayi Ido biyu da wacce tai mata sihirin zai dawo jikinta.
Bayan kwanaki biyar zata koma tsuntsuwar Boleru kamar yadda sukayi mata.
A lokacin Bappa yaƙi shi dai yace ta samu lfy ta fara mgn amman da gaiya Ba'ana ya bata wannan mgnin sabida zalumcin da akayi mata ya tsananta.
Cikin wani irin gigita Hajia Mama ta kai hannunta ta taɓa fuskar Ummey tare da cewa.
"Kika dawo mutum kenan bokana yamin ƙarya yace min har abadan yadda matacce bazai dawo duniyaba haka bazaki dawo mutunba bazaki taɓa dawowa Masarautar Joɗa ba."
Sai kuma ta kai hannu ta bugi gefen bayanta ta sosa tare da karkata baki kana tasa hannun ta ɗaya ta cire ɗan kwalin kanta ta cillashi gefe tare da cewa.
"Shigayar balarabiya mai nacin tsiya ki aure min miji ki haife mishi zaratan maza harda tagwaye kana ace cikin ƴaƴan ki za'a samu mai gadar mulkin Masarautar Joɗa ai wlh bazata saɓuba".
Sai kuma ta fara yatsuma gashin kanta tare da kurma ihu.
Cikin wani irin yanayi mai cike da rauni kunya tashin hankali kiɗima gigita.
Affan ya kife kansa da jikin sawun Sheykh ya saki wani irin kunyataccen kuka mai cin rai tare da cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun Hamma Jabeer wanne yanayi ne wannan Hajia Mama take ciki wannan wanne ranane mai cike da kunya Allah ya zai nuna min".
Da sauri suka juyo suna kallon Baba Kamal da yake fifita da hularshi tare da kecewa da dariya yace.
"Hahaha ta haukace ta haukace na haukace, zasu haukace duk zamu haukace.
Shegiya muguwar babarbariya ba ke kikayi mata sihiri ta zama tsuntsuwar Boleru ba kika haukata Jafar ba kika sawa Jamil bin mata Jalal bin mutanen banza bw".
Da sauri ta juyo cikin wani irin rawa-rawan haka na sakayyar mugun aikinta tace.
"Tafi daga nan mugun bafulatanin kai kuma ai kai ne kayi mishi ashirin kashe mishi lfyarsa dan kada yayi aure bare ya haihu kana zaton bansan duk abinda kakeyi bane".
Sai kuma duk suka kece da dariyar hauka tare da faɗi ƙasa sunayi harda tafa hannunsu.
Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil waɗannan sune kalaman da gaba ɗaya mutanen falon sukeyi sabida fahimtar sakayyace ta riskesu tun a duniya.
Baba Basiru ne ya matso kusa da Baba Kamal tare da cewa.
"Mugu bashi da kama Kamal kaida Hajia Mama tabbas kun cika mugaye masu cikekkiyar manufa wanda har kuka iya ɓoye muguntarku."
Su dai su Sheykh Umaymah Shatu Lamiɗo Abba Bappa gaba ɗaya zuba sarautar Allah ido sukayi.
Affan kuwa kukane mai cin rai yakeyi cike da kunyar abinda mahaifiyarshi ta aikata.
Shi kuwa Baba Basiru a hankali ya matso gaban Gimbiya Saudatu daketa zazzare idanunta cike da mamakin jin tsantsar muguntar mutanen da kullum take faɗa dasu a zatonta masoyan Sheykh ne.
A hankali ya kalleta kana yace.
"Jabeer yau dai ka yarda ka gamsu da abinda nake ce maka ko".
Cikin yanayi gamsuwa Jabeer ya kalli Baba Basiru wanda mutane ke zato maƙiyinshine har Gimbiya Saudatu ta haɗe dashi bata san cewa ƙididdigarta yakeyi ba.
Shi kuwa Baba Basiru a nitse yace.
"Dama na gaya maka Gimbiya Saudatu sha giri girbauce wautace kawai ke damunta da ƴar hasada, sannan kuma da zugan wannan maƙiyin nata".
Yayi mgnar yana nuna Baba Nasiru wanda ita a zatonta masoyi ta ne.
Cikin gyara tsayuwarshi ya kalleta kana ya kalli shi Baba Nasiru daketa karkarwa cikin zubda hawaye yace.
"Ke Gimbiya Saudatu kullum Nasiru na ingizaki da zugaki da cewa Gimbiya Aisha da ɗan ta Jafar ne suka