Showing 297001 words to 299804 words out of 299804 words

Chapter 100 - GARKUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

17 Jul 2024

111412

yake son sanar mata.
Shiru tayi tana jin ɗumin harshensa shi kuwa cikin sake mata kiss tako ina yace.
"In bakya so ki gaya min Aish sai in fasa auren."

(Toh sokuwa kada kiji mijinki yace wai in bakya so zan fasa, kice zakice bakya so.
Yaseen farfaganda ce kawai, da son kwantar miki da hankali da irin su nuna miki kin isa dasu ɗinanne, kada kiyi zaton zasu tozar taki.
To da kinyi wautar cewa eh. Ni bana so ban aminceba kada kayi aure.
To kallon sokuwa zai fara yi miki yoh to ke uwarsace da zaki hanashi yin auren da Allah ya bashi damar yayi.
Ke kuwa amrya uwar kaɗi firi ki shigo rana tsaka ki nunawa uwar gida kin fita sanin mijinta.
Wawuya to wayayyu basa haka, wai ke irin ke ake so ɗinnan irin anai miki zaƙin bakin nan, to wlh kada ki kuskura kiyi zaton uwar gidanshi bata gabanshi maza bakin gangane duk ta inda yafi zaƙi ta nan suke bugawa.
Domin dolene ya miki wannan zaƙin bakin.
Sabida ai duk ɗan siyasa dole yayi kamfen yayin neman a zabesh to, hakama neman aure, kisa a ranki yana son matarsa.
Kema mada kisa a ranki amryafa ana sonta sannan uwar gida kiyi haƙuri domin amarya ko ta buzuzuce za'ayi mata marmari, in kinga yana rawa da ƙafa ɗaya tattara ki watsarsu, basu lokaci zai dawo har kataryarki ya nemeki.

Cikin tsananin zafin kishi Shatu tayi ajiyan zuciya data samu ya danne mata malolon da takejin yana gab da kasheta tace.
"A'a Yah Sheykh na amince Allah ya bamu zaman lfy".
Cikin tarin jin daɗi da gamsuwa da wayewarta yace.
"Amin Amin. Ameeeeeeen ya rabbil izzati, Shatu my happiness my everything my life Mar'atussaliha".
Ya fara jero mata sunaye, wani sunanma ranar ta taɓa jinshi.
Da sauri ta miƙe ta fita.
Tana cewa.
"Laa na manta na ɗaura tukunya".
Ta faɗi hakan tana fita dan kada ya gane halin da take cikin ( Sabida in mijinki ya gane miki kinada mahaukacin kishi to kallon zarerriya zai rinƙa miki, hattara mata).
Tana fitowa bedroom ɗinta ta wuce.
Tana shiga ta meda ƙofar ta rufe, kana ta faɗa bisa gado ta saki wani irin masifeffen kuka mai cike da kishin mijinta abin sonta.
Da sauri Junainah dake Bathroom ɗin ta tanayiwa Khausar wonka ta fito.
Gefenta ta zauna jiki na rawa tace.
"Innalillahi Adda Shatu meya sameki meya faru?".
Kawai sai ta mirgina ta ɗaura kanta bisa cinyar Junainah ta saki kuka mai rauni tare da cewa.
"Ba komai Junainah na tuno su Yah Lado da Inna ne".
Cikin rashin gamsuwa Junainah tace.
"Adda Shatu wai yaushe kika fara ɗaukana a matsayin ƙanwar Hamma Jabeer? Kin mance tare muka tashi muka rayu bani da wani ɗan uwa ko ƴar uwa sama dake, gaya min gsky meya sameki?".
Cikin yin ƙasa da murya tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa.
"Yah Sheykh zai ƙara aure Junainah na kasa hana kaina kuka!".
Murmushi Junainah tayi tare da cewa.
"Shine zaki ɓoye min, to sa a ranki ni nan Junainah ko Ishman Aunty Rahma ya auro ni mai tayaki kishine.
Kuma wlh auren a dole yazo mishi kana kada kiyi kokonton soyayyarshu gareki.
Allah dole Abba ya sashi amsar auren Mamey ma har kuka tayi ita da Ummi wai kuna zamanku lfy kada a birkita muku zama sai dai naji sunce itama Aunty Jazrah Bata faɗa".
Cikin jin daɗi tace.
"Toh dan Allah kada ki cewa su Mamey nayi kuka hankalinsu zai tashi."
Cikin gamsuwa da hakan tace.
"Toh".
Gyara zamanta tayi tare da cewa.
"Wai yaushe kika dawo?".
Cikin lumshe ido tace.
"Yah Junaidu ne ya ɗaukoni wai rana tayi kada in sha rana ya kodar masa sani".
Dariya sukayi baki ɗayansu.
Kana sukaci gaba da hira.

Haka dai aka fara shirin auren Jabeer da Jazrah, Junainah da Junaidu aure haiƙan ƙadaran.


Alhamdulillah anyi aure lfy an watse lfy, amare sun tare.
Kowa ya kama gidansa.

Bayan shekaru goma sha ɗaya.

Abubuwan da yawa sun faru cikin shekarun.

Yusuf ɗan Affan ya auri Afreen sai dai basa ƙasar suna India.

Jabeer ƙarami kuwa yana karatu a jami'ar Madina
Bappa yana nashi karatun a India.
Habibullah kuwa yana karatu a nan cikin jami'ar Ɓadamaya.

Jazrah ma ta haifi yara uku Aliyu takwaran Dr Aliyu, sai Ruƙaya da Aminatu takwarar Gimbiya Aminatu wacce itama ta rasu.
Shatu kuwa ta ƙara biyu Khadijah takwarar Umaymah sai autanta Sultan.

Rayuwa fa ta miƙa komai yana tafiya.

Hajia Mama ta rasu babinta ya ƙare a masarautar Joɗa.

Yau kimanin mako biyu kenan da tafiyar Shatu Cameroon.
Sai yau da hantsi jirginsu ya dawo.

Habib ne ya ɗaukota da Jabeer ƙarami wanda yazo hutu.
Sai Bappa wanda tare suka zo da Afreen da ƴan tagwayenta.
Mu'azzatu da mu'azzam dan da tagwaye tayi haihuwar farinta.

Suna zaune a falon Jazrah Aminatu na goye da Mu'azzam wanda takwaran Yah Sheykh ne.
Tanata juyi tana cewa.
"Sorry Mu'azzam Adda Afreen kizo ki bashi nono mana".
Tura baki tayi tare da naɗewa bisa kujera, taci gaba da bawa Jazrah labarin littafin
*Ba Kason ɗauka bane* na Aysha Aliyu Garkuwa.
Da sauri Jazrah da yanzu take jin hausa ras tace.
"Afreen kamar muryar Mamanku nakeji fa".
Da sauri suka miƙa baki ɗayansu suka nufi.
Side ɗin Shatu.
Da gudu Afreen ta iso ta bayanta ta ruggume ta tare da cewa.
"Oyoyo Mommy".
Cikin sarkuri ta juyo don bayan ta tafi Cameroon Suka zo.
Cikin jin daɗi tace.
"Oyoyo Adda Afreen".
Jabeer ƙarami ne ya ɗan harareta tare da cewa.
"Toh ki barta ta shiga ciki mana, kin tsare mana ita a woje."
Ya ƙare mgnar yana amsar.
Mu'azzatu dake hannun Jazrah tare da cewa.
"Aunty yunwa nakeji fa".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Toh Yah J Jabeer ɗan Jabeer".
Murmushi sukayi duka kana kab suka wuce falon Shatu.

Bayan sun gaggaisa ne, sunci sun sha, Shatu ta wuce ɗakinta.
Tayi wonka tare da al'wala tana fitowa tayi salla kana ta kimtsa cikin wani tattausan yadi Royal blue mai ɗan karen kyau riga da zani.
Ta cancaɗa daurinta ras.
Ta fesa turare, da shafe humra mai sanyin ƙamshi,
Da sauri ta jawo wayarta jin text ya shigo mata a waya.
Murmushi tayi ganin Habibi Da'iman. Sheykh kenan.
Buɗe saƙon tayi.
"Alhamdulillah barka da isa lfy Gimbiya Aysha, hasken Masarautar Joɗa, kina shigowa ƙamshinki har fada yazo ya gaidani.
Yanzu zamuyi salla, Please dan Allah ki gama da yaranki da jikokinki kafin in dawo in sameki a ɗakina, kinji ko Aish na".
Cikin jin daɗi ta maida mishi amsa
"Uhummmm toh Yah Sheykh me zaka bani?".
Murmushi yayi tare da rubuta mata.
"Kayan daɗin ki".
Murmushi tayi tana mai lumshe ido.

Ai kuwa ana idar da salla ya nufo gida.
Kai tsaye ta ƙofar falon Shatu ya shiga.
Su Jabeer, Bappa, Habib, Aliyu, Sultan autanshi na biye dashi a baya.

A falon suka samu Afreen, da yaranta da Amina da Khausar Ruƙayya da Khadija suna cin abinci.
Suna ganinshi suka gaisa.
Kan Mu'azzatu dake hannun Jazrah da yanzu ta fito ɗakin Shatu dan mata sannu da hanya da kyau.
Shafa kanta yayi tare da cewa.
"Jika wahal da kaka ko?".
Murmushi Jazrah tayi tare da cewa.
"Gata ƴar lukuta".
Cikin jin daɗi yace.
"Haka Mamanta take tana ƙarama.
Kamar yau ina tunowa haka Abbanmu ke kiranta ƴar luku".
Murmushi Afreen tayi cike da jin daɗi.
Jabeer kuwa baki ya taɓe tare da cewa.
"Abeey nifa".
Cikin son ɗan nashi Yarima Jabeer kenan motsusu yayi tare da cewa.
"Kai ai na musamman ne".
Duk suma sauran sai suka zuba mishi ido.
Ɗaya bayan ɗaya ya yabasu.
To Sheykh kuwa da tsuntsaye ma sai ya yabawa ko wacce taji bata kishin ƴar uwarta ko ganin tafi ƴar uwarta bare yaranshi.

A haka dai ya wuce ya tafi Side ɗinsa.

Ita kuwa Jazrah ta wuce Part ɗinta dan tasan.
Shatu ce dashi yanzu.

Ita kuwa Shatu a hankali ta fito tana mai baza ƙamshi.
Ganin kab yaranta suna sabgogin gabansu ne yasa ta shafa kan Mu'azzam dake zaune kusa da ƙofar ta wuce Side ɗin Yah Sheykh da ɗan sauri jin yana ɗan kiran Jabeer tare da cewa.
"Kira min Mommynku.

Da sauri ta ƙarasa cikin falon nashi tare da cewa.
"Assalamu alaikum Yah Sheykh gani da kusa".
Da sauri yace.
"Wa alaikassalam *(Y!.M!.D!.G!.)* na! Nooryat Noor ƙalbi My love my happiness".
Cikin jin daɗi tace.
"Yah Sheykh kenan kamar wasu yara".
Da sauri yasa hannunshin ya kamo nata ya jawota jikinshi tare da ruggumeta ajiyan zuciya ya sauƙe tare da sa kanshi tsakanin wuyanta da kafaɗarta yana sunsunan wuyanta yace.
"Aish waya ce miki soyayya tana tsufa? Ai sai dai masu ita su tsufa.
Mu kuma bamu tsufan ba tukun".
Ya ƙarashe mgnar tare da wucewa bedroom ɗinsa da ita.
A hankali ya meda ƙofar ya rufe kirib.
Tare da sauƙe nufamshi kana ya sunkuyo ya ɗagata ciɗak yayi kan gado da ita.
Cikin lumshe ido ta ƙanƙameshi gam a cikinshi.
Haka yasa suka kwanta a tare.
Da sauri yasa hannunshin ya ture rawaanin kanshi tare da cewa.
"Hegen nauyi da takura".
Murmushi tayi tana mai kunce igiyoyin dake sarƙafe gaban al'kyabbar jikinshi.
Tare da cewa.
Ash Yah Sheykh nauyi".
Mirgina wa yayi gefe ya kwanta kana ya jawota jikinshi ya zama sunan fuskantar juna.
A hankali ya kai lips ɗinshi kan mata wani ɗan sasayyan kiss ya manna mata kana a hankali yace.
"I missing You so much my love".
Sai kuma taga ya ɗan juya da sauri ya kalli windows ɗinsa.
Fahimtar yana dubawa ko a buɗene yasata cewa.
"Yauwa Hamma Jabeer niko inda da wata tambaya data daɗe min a rai."
Da sauri yace.
"Wacce tambayace haka faɗeta miji".
Ya ƙare mgnar yana tura hannunshi cikin rigarta.
Hannunta tasa ta ɗan shafa sajenshi tare da cewa.
"Akwai lokuta da dama ina wani dalili yasa munje HOTEL duk ɗakin da ka kama in mun shiga sai ka bibbincika ka dudduba lungu da saƙo, wani lokacin ma kace in fita mu sauya ɗaki. Koma sauya HOTEL ɗin baki ɗaya, meyasa? Me kake dubawa?."
Ronƙofawa yayi kanta yana zare zip ɗin rigarta yace.
"Ok ban taɓa yi miki bayani bako?."
Da sauri ta gyaɗa kai.
Cikin nitsuwa yace.
"Wato shi HOTEL wani wurine mai cike da ƙalubale ga duk wani mutumin kirki, Especially in a cikin ƙasar ka ta haihuwa kake, domin da yawa har yanzu mutane basu fahimci cewa larura zata iya kaika hotel, ba lallai dole sai ɗan iskaba kamar yadda wasu ke zato.
Sai dai abin lura a nan abinda ya kamata ga duk ko wani musulmi, muddin larura ta kaika HOTEL, to ka tabbatar ka binciki duk ɗakin daka kama ciki da woje kama Daga jikin ƙofa, wurin kunna fanka, wurin ajiye Rimot ɗin AC,
Jikin AC, tsakiyar jikin fanka, saman silin, jikin ƙarfen labule, jikin TV Especially in suna fuskantar gado, da kuma jikin kan gado kofar Bathroom dama cikin Bathroom ɗin".
Da sauri Shatu tace.
"Me yasa? Sabida me mutun zai tsaya wannan dube-duben duka!?".
Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa.
"Sabida mafi akasarin HOTEL'S wasu ƴan iskan kajeme kawai dan su dasa na'urar Camera a jikin duk waɗannan wuraren da na faɗa miki.
Ya ɗauka musu duk mu'amalar mata da miji ko ɗan iska da ƴar isa, daga nan sai su sarrafashi ya zama blue Film, da yawa waɗanda suke ciki basa sanin ana ɗaukar su.
Na'urar Camera da suke amfani da ita ƴar ƙanƙanuwace kamar botur ɗin rigar maza, in sun liƙata sai ta ɗauki komai.
Su kansu masu hotel basa sani.
Wasu lokutan kuma su ɗin ne da kansu ke dasata.
In baki mantaba akwai ranar da na samu camara ɗin ma liƙe a cikin abin AC. Har muka canza ɗaki masu hotel ɗin sukayi ta bani haƙuri suda kansu suka binciki ɗakin da muka sake shiga kin tuna."
Cikin jan dogon numfashi tace.
"Eh tabbas na tuna Hamma, eh to lallai kuwa in hakane dole musulmai muyi taka tsantsan".
Kai ya jinjina tare da cewa.
"Shiyasa shi musulunci yana da daɗi kinga koda mutun baya bincika in yana amfanin da hadisin nan da manzon Allah ya hanemu da yin jima'i tsirara har sai an rufu.
Kinga mutun zai tsira.
To amman dai mafi sauƙi ka bincika kawai.
Dan in kayi garaje wata ran za'a yaɗaka a bazaka a duniya kana jima'i da iyalinka ace BF ka fara yi. Kaga anci zarafin ka anci zarafin addinin ka".
Ya ƙare mgnar da fara yin ƙasa da rigarta.
Ita kuwa Shatu kai ta jinjina tare da cewa.
"Masha Allah da kamilin miji mai cikekkiyar kamala da Nagarta.
Sai kuma wata tambayar".
Da sauri ya kwaɓe fuskarsa tare da cewa.
"Bazaki bari sai na nitsuwa ba dan in baki amsa mai kyau".
Cikin narke mishi a jiki tace.
"Afwan kada in mance ne ai, kuma tambayar ba tsawo".
Hannunshi yasa yana jan zariyar wondonsa tare da cewa.
"Toh ina jinki".
Cikin maida nitsuwarta gareshi tace.
"Menene ma'anar *(Y.M.D.G?)*".
Wani irin kekkyawan murmushi yayi mai cike da shauƙi yace.
"Sirri nane kalmar".
Cikin fara murzashi tace.
"Dan Allah ka gaya min".
Wani sassayan numfashi yaja jin salon da ta fara yi mishi.
Murya a narke yace.
"Sai in kinyi al'ƙawarin bazaki gayawa kowa ba".
Da sauri tace.
"Nayi".
Murmushi yayi tare da zare rigarta ya ture gefa.
Cikin raɗa yace.
"Zan gaya miki harufa ukun na huɗun na ƙarshe ki ƙarasa da kanki".
Cikin zaƙuwa tace.
"Toh ina jinka menene ma'anar Y.M.D.G. Please bani amsa da sauri na zaƙu?".
"Matso da bakinshi yayi kusa da kunnenta a hankali murya can ƙasan maƙoshi yace.
"Y. Yana nufin *Yarinya* M yana nufin *Mai* D yana nufin *Daɗin* G ɗin kuma ki gane kinga ukun dai suna nufin
(Ƴarinya mai Daɗin...".)
Narkewa jikinshi tayi tare da cewa.
"Please na tuba gaya min".
Murmushi yayi tare da kai bakinshi bisa kunnenta a hankali cikin raɗa yace.
"Ƴarinya mai daɗin G..."
Da sauri ta rumtse idanunta sabida wani irin masifeffen kunyan kalmar da ya rufeta.
Haka nan taji kanta na huruwa yana sama tana jinta a saman gajimare ashe waɗannan harufan abinda kenan suke nufi, iya wannan sunan da yake kiranta ya isheta gane matsayin yadda Yah Sheykh ɗinta ke gamsuwa da ita ɗari bisa ɗari.
Shi kuwa ya Sheykh cikin tsananin so, bege, shauƙi, kauna, yace.
"Allah sarki *ƳAR FULANI* mai kunya Alhamdulillah da Na samu sa'ar samunki dan da na rasaki to tabbas da *NAYI NADAMA (MI WASMITI)* kinga ko lallai na yarda shi *NAMIJI BAYA KAƊAN* dan da shawarar Affan na fara gano magautan mu.
Gashi a hankali muka samu Kekkyawan shaƙuwa da *TAUSAYAWA JUNA* sai daga baya na gano ashema ke *BANDIRAWO* ce a gareni tunda uwa ɗaya ce ta bamu tarbiya.
Gashi cikin ikon Allah *RUBUTACCEN AL'AMARI* ya ƙaddara saduwarmu da aurenmu cikin *HUKUNCIN ALLAH* harda yara.
GASHI MUN ZAMO tamkar hanta da jini.
Tsorona ɗaya a duniya kada *RIGAR KOWA* ta fara ɗaukanki ta barni."
Wani sassayan numfashi ta fesar a hankali tana maijin tattausan kalamansa gareta. Shi kuwa Sheykh cikin gsky da gsky yaci gaba da cewa.
"Gwara ta ɗaukeni ta barki.
Domin duk da nasan cewa *NAKASA BA KASAWA BACE* tofa in ta ɗauke min ke ta barni zan rabu da rayuwar farin ciki domin Shatu kece *GARKUWA* a gareni sabida sam Rashin ki *BA KASON ƊAUKA BANE* Agareni.
Ya karashe mgnar tare da yujowa yayi mata rumfa da ƙirjinsa tare da jawo tattausan blanket ya rufesu yana mai cewa.
"Mu ɓuya Shatu na kada wannan ƴar darun Hammanta AYSHA ALIYU GARKUWA, ta hangomu ta samu abin rubutawa makarantanta. iyayen son ganin ƙoƙob sai kuma ya fara tasbihai tamkar yadda ya saba.
Subahanallahi Alhamdulillah wa la'ilahaillahu, Allahu Akbar Astagafirullaha..............................!


Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Allah na gode maka da ka bani aron rai da lfy da nitsuwa da kwanciyar hankali ka bani iko da dama na kare wannan littafina mai suna GARKUWA lfy kamar yadda na farashi lfy dani da makaranta shi baki ɗayansu.
Yah ka jiƙaina ka gafarta min al'farma Annabi da al'ƙur'ani a duk abinda nai kuskure, ka tsare min al'ƙalamina a karo na gaba.
Abinda nayi dai-dai ya Allah ka taramu bisa ladan nida masoyan Manzon Allah waɗanda in an haɗa su da Allah da manzo kan kada suyi abu bazasuyi shiba.

Afwan! Afwan!! Afwan!!!
Masoya na makarantana, na nesa dana kusa waɗanda na sani da waɗanda ban saniba waɗanda suka biya da masu karanta na sata, wanda na taɓa mgn dasu da waɗanda ban taɓa mgn da suba.
Dan Allah ku gafarceni in akwai wani abu da nayi miki/ka bisa rashin sani da ajizanci na ɗan adam ko kuma gajiya da yawan jama'a da rashin hutu yasa kinyi mgn ban kulaba kuyi haƙuri ku yafe min abubuwan ne suna min yawa. Ina mai fatan Allah ya ƙaddara saduwarmu a wani littafina lfy al'farmar Annabi da al'ƙur'ani.

Godiya ta musamman gareku wadanda suka biya kuɗin littafin suka karanta da kuɗinsu ba na sataba yan na sata ba sai na ƙarasa ba yaseen doguwa bullulutu baƙar mutuwa🤣🤣🤣.

*Alhamdulillah na godewa Allah da ya bani ikon cika alƙawarin da nayi ko ince yarjejeniya da nayi daku ƴan special Group, na posting PAGE bibbiyun kullum Alhamdulillah ina al'fahari yadda ko rana ɗaya rak rana ɗaya kacal dai cikin rakun littafin ban taɓa tsallakewa ko ƙetarewa banyi muku posting ba Alhamdulillah nayi al'ƙawari kuma na, cika wannan ma yana ɗaya daga cikin manyan nasarorin da na samu a littafin GARKUWA. Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah zanyi bacci hankali konce in tashi sanda nakeso*




Littafin GARKUWA na kuɗine idan kinaso ki karanta wa, bada haƙƙin na a kankiba, ki sai katin Mtn na ɗari uku kacal, ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsApp number na 09097853276. Sai in saki a group kota ac no 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa.






By
*GARKUWAR FULANI*

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login