Showing 270001 words to 273000 words out of 299804 words

Chapter 91 - GARKUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

17 Jul 2024

111428

kashe miki mijinki babban yayanmu Yah Aumalu mahaifinsu Hashim da Laminu wan dan Jafar ya gaji sarautar Galadima ko?".
Da sauri ta gyaɗa kanta.
Yayinda suma duk saura suka zuba mishi ido.
Cikin zubda hawaye yace.
"Toh kinga Yah Nasiru ɗan uwanmu uwa ɗaya uba ɗaya shine ya kashe miki mijinki uban ƴaƴanki sannan yanke ingizaki kan su Sheykh da mahaifiyarsu yasa miki tsanarsu kiketa haushi a kansu kamar karya.
Ita wannan muguwar kuwa Hajia Mama da Kamal da Hashim ɗanki da kuke gani kamar yana son Jabeer alhalin ya tsaneshi shi kuwa wai dan Lamiɗo yafi janshi a jikinshi.
Duk sai suka fake a bayanki sunayiwa Sheykh da ahlinsa mugunta yayinda kowani sai yayi zargin kece kinga kin zama bushiya kamar yadda Shatu ta faɗa a zahiri in anganki jiki duk ƙaya amman cikin bushiya namansa ma maganine su kuma suka kasance belbela siffarsa fara cikinta baƙiƙƙirin".
Cikin rauni Gimbiya Saudatu tace.
"Innalillahi wallahi ni dai Allah ya sani ko garin marke ban taɓa nemowa da niyar cutar dasuba..
Yanzu ashe Hashim kaima muguwar zuciya gareka ban saniba har zaka iya cutar da ɗan uwanka."
Ina Affan kam tuni yake kuka tamkar zai shiɗe dan baƙin ciki da takaicin abinda uwarsa ta aikata.

Yah Jafar ne ya gyara zamanshi tare da cewa.
"Tabbas kuwa Hajia Mama da Baba Kamal da Baba Nasiru da Hashim sune manyan Magautan mu".

Da sauri Sheykh ya miƙa tare da kamo hannun Hajia Mama da taketa son kwaɓe kayanta.
Da sauri ya nufi Side ɗinsa.
A wannan ɗaya ɗakin yasata ya rufeta bayan yayi mata allurar bacci.
Kana ya fito.
Nan ya samu Lamiɗo yasa Fadawan shi sun fita da Baba Kamal dake ta ihun hauka.
Sannan Jalal kuma ya miƙa ya damƙi Baba Nasiru dake son guduwa.
Ya miƙashi hannun abokanshi sojojin daya kira bisa laifin kisan kai.

Shi kuwa Yah Sheykh a hankali ya kalli Yah Hashim a hankali yace.
"Ashe harda kai a cikin magautana Yah Hashim. Kai lallai ɗan Adam darene babu mai saninsa sai Allah".
Lamiɗo ne ya kamo hannunshi ya zaunar dashi kana yace.
"Kai Hashim fice mana daga nan bama buƙatar mai muguwar zuciya ko ɗaya a nan".
Ai kuwa da gudu ya fice cike da kunya.

Shi kuwa Lamiɗo gyara zamanshi yayi tare da cewa.
"Jafar bamu lbrin meya faru da kai da mahaifiyarku a dare ɗaya ta sauya halitta daga mutun zuwa tsuntsuwar Boleru kai kuma ka dena mgn".

Gyara zamansu sukayi baki ɗayansu dan wannan itace tambayar da take cinsu a rai tsawon shekaru goma sha uku kenan gaba ɗayansu.

Cikin gyara zamanshi ya ya fuskancesu kana a hankali yace.
"A ranar...!






Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300 babbancinsu a posting ne 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Ta wannan ac no zaku tura kuɗin sai kiyi screenshort na Debit Alert ɗin ki turo min shaidar biyan ki ta whatsApp 09097853276 ku yan 300 in baku da damar biya ta Account zaki iya sayan katin mtn na ɗari uku kacal sai ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsApp 09097853276.



By
*GARKUWAR FULANI*
[4/2, 7:41 AM] +234 806 559 0880: "Aranar wata jumma da da wanna Zazzafar ƙaddara ta rufta damu shekaru goma sha uku baya."
Sai kuma ya ɗan tsakaita
tare da jan
sassayan numfashi ya gyara
zamansa tare dasa tafin hannunshi ya share hawayensa.
Yayin da gaba
ɗayansu kacokam
suka mai da hankalin su kansa,
Duk sun ƙagu suji yadda a kayi a wannan ranar da basu manceba.
Shi kuwa Yah Jafar wani numfashin yakuma.
Saukewa kana yaci gaba da cewa.
"Ranar da dare bayan anyi sallan isha'i duk muna falon Mamey dani dasu Jalal Jamil Affan da Ummi da Imran yana ɗan sheksru takwas lokacin.
Anan mukaci abinci kana muka zauna muna hira.
Kasan cewar akwai shaƙuwa mai tarin yawa tsakanin Mamey da Affan da yake tana da son yara.
Amman son Affan da banne a wurinta har su Jamil kance wa Affan na hannun daman Mamey.
Takanyi Dariya tace.
"Eh ɗin ai ya fiku nitsuwa".
Muna zaune sai hamma Mamey keyi tare da miƙa da lumshe idonta hakane yasa tace mana.
Duk ta sallamemu saida safe tanajin bacci.
Ummi tace.
To.
Still Kuma sai mukaci gaba da hira.
Da ido muka bita ganin ta miƙa cikin sanyi tace.
"Kai zanje inyi bacci wlh wani irin bacci mai nauyi nakeji yana fuzgata tamkar zan faɗi.
Ni na shiga saida safenku".
Allah ya bamu al'khairi mukace dukanmu kana ta shiga.
Tana shiga kwanta ko second uku batayi da kwanciya ba tayi bacci.
Mu kuwa muna gama hira muka watse.
To su Jalal ne ƙarshen fita ashe basu tasheta ta rufe ƙofarta ba a famintata kenan fa?".
Ya ƙare mgnar yana kallon su Jamil.
Da sauri Jamil yace.
Eh.
Cikin sanyi ya kalli su Lamiɗo kana yaci gaba da cewa.
"Ina komawa ɗaki na kira Juwairiyya muka fara hira a waya kamar kullum.
To bayan mun gama
waya da Juwairiyya
har na kwanta sai na mike na nufi
ɗakin Mamey dan
inaso nayi mata magana a kan Juwairiyya fa tasanar wa mahaifin su maganar auren mu da ita, tun da lokacin takammala
karatun ta dan haka itama ta gayawa Abba na ayi batun aurenmu dan nima tuni lokacin na gama karatuna har na fara aiki.
Kuma a kwanakin ne aka bani sarautar Galadima wanda da mijin Gimbiya Saudatu ce mai matsayin to daya rasune Lamiɗo ya maida mulkin kaina.
A zatonshi ta hakane zaisa yaranshi bazasuyi faɗa da junaba tunda bazasuce ya baiwa wane ya hana waneba.
Ni a lokacin dagani har Mamey da Jabeer da baya ƙasar ma ba son wannan mulkin mukayiba bisa dole aka bani ita.
Sai kuma ya jingina bayanshi da kujera kana yaci gaba da cewa.

Ina isa bakin kofar
Mamey natura kofar da sallama nashiga ɗakinta.

Da sauri naja natsaya nan bakin kofar.
Can na hangi Mamey na kwance.
Bisa gado tana bacci da alamun baccin mai nauyi ne.
Hajiya mama kuwa na tsaye a kanta da wata iriyar shiga da tafi kama data bokaye ko ince matsafa.
Da mamaki nake kallon
Hajia Mama dake tsaye bakin gadon sanye da wasu irin jajayen kaya tun daga samanta har ƙasa,
kanta babu ko ɗan kwali
hannunta rike da wani ƙwarya.
Tana yayyafawa Mamey
wani ruwa dake cikin ƙwaryar tare da yin wasu surutai da sukafi kama da surkullen matsafa.

"Innalillahi wa'inanna ilaihirraji'un, nafurta da karfi.
Da sauri nanufo in da Hajia Mama'n ke tsaye cikin ruɗani da kiɗima ina faɗin.
Meye hakan Hajia Mama? me kike mata? me kike zuba mata a jiki haka?.
Dasauri tajuyo kaina tasaka hannunta cikin ƙwaryar taɗibo ruwan tashiga watsamin tana ƙara matsoni,
kaucewa nashiga yi ina matsowa in da Mamey take kwance kamar gawa ko matsi batayi,
itako Hajia Mama masoni tarikayi tana watsamin ruwan,
Baki na buɗe da karfi sabida wani irin masifeffen suka da naji duk inda ruwan ya taɓa a jikina yanayi.
Ƙara watsomin tayi wanda yasa na ƙara kaucewa da sauri tare da buɗe baki da nufin yin ihun zafin da nakeji da kuma fargabar halin da Mamey na ke ciki.
Sai kawai naji harshena yafurta Innalillahi wa'inanna ilaihirraji'un,wannan kalmar narika nanawata da karfi madadin inyi ihu."

Ita kuwa Hajia Mama da sauri tajuya cikin alamun tsoron tonuwar asirinta.
dan lokacin dare baiyi nisa sosai ba misalin ƙarfe goma ne,
da gudu tafita a ɗaki dan jin yadda na kara sautin salatin da nake.


Ita kuwa Hajia Mama tana fita part ɗinta ta nufa direct bathroom ɗinta ta shiga gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi number'n bokan ta takira yana ɗagawa cikin haki da fargabar a bin da zaije ya da wo tace.
"Boka yanzu nafito daga ɗakin matarnan na samu tayi bacci kamar yadda kace, kuma na watsa mata ruwan bata farka a sai daifa wani yaganni lokacin danake yayyafa mata ruwan maganin nan babban ɗanta Galadiman Masarautar Joɗa kenan ya ganni".
Wani irin dariya irin nasu na hatsabibai bokan yayi kana yace.
"Toh daya ganki me yakeyi? me kuma yake cewa?".
cikin rawar baki da soron da ya ziyarce ta gudun kada ai kin ya ɓaci tace.
"Sunan Allah yaketa ambata salati yaketayi babu ko kakkautawa da wasu addu'o'i".
Cikin ɗan tsagaita dariyar mugayen bokan yace
"To aiki kam zaici amma dai akwai nakasu aciki, amma kada kidamu yanzu shi yaron zamu rufemasa baki zai dauwama kurma ba mgna a bakinsa bazai iya yin maganaba bazai iya furta komai ba haka zai dauwama ba mgn saidai yayi ta mai-mai-ta abinda yake cewa.
Sannan daga nan tagwayen kuma zamu haɗa ɗaya da bin mata ɗaya shaye-shaye shi kuma babban kinga zai zama kamar Mahaukaci, shi kuma wancan Jabeer ɗin na gaya miki tun yana ƙaramin akwai sihirin da wani yayi mishi kada ki damu dashi bazai taɓa yin aureba har gaban abadan ko an mishi bazai zauna da matarba, kinga kenan duk sun zama suna da matsalar da dole baza'a basu mulkiba sai dai a bawa ɗanki Affan tunda kinga shi Imran ɗan ɗaya kishiyar taki shine ƙarami kan Affan."
Cikin sauƙe numfashi tace.
"Yauwa boka na gode ni dama fatana ɗana yayi mulki dan bana son mulkin ya bar ɗakina tunda dai kace min tabbas cikin yaran Habibullah ne mijin wani zai gaji kakansa sarauta.
Dariya yayi tare da cewa.
"Kada ki damu mulki na gareki da ɗanki".
Wa iyazubillah kaɗan kenan daga sharrin tsinannun shaiɗanu maƙiya Allah da Manzonsa bokaye taɓaɓɓu masu sa mai binsu ya taɓe ya gaza sauri a ranar da muminai ke sauri a bisa siraɗi.

Acan cikin ɗakin Mamey kuwa.
Sosai sautin addu'a da karatun da Jafar keyi yatsanan ta yana kankame da Mamey, wacce ke ƙwance ida nunta a rufe, har lokacin bata farka daga.
Baccin sihirin da akasa takeyi ba saboda nauyin. Baccin da suka je fata ciki.
Sheko bakinsa baya iya furta komai sai addu'o'in sai kuma hawaye da keta tsatstsafowa daga cikin ida nunsa sabida fargarba da kuma zafin da yakeji,
Abba kuwa dake can part ɗinsa da yake Part ɗin shi na natsakanin na matan nashi ne.
Yana cikin ɗakinsa dake sama.
Haka yasa yarinƙa jiyo muryar Jafar da irin addu'o'in dayake cikin kiɗima, da kajin addu'ar kasan acikin tsananin firgici da tashin hankali yake yinsa,
Wuf yamike yanufo part in Mamey kasan cewar babu wata tazara sakaninsu.
Gudu-gudu sauri-sauri ya isa.
Cikin hanzari yatura kofar bedroom ɗin Mamey cikin sananin tashin hankali da kaɗuwa ganin yadda Yah Jafar ke rungume da Mamey sai innalillahi yake da karfi hawaye yagama wanke fuskarsa idanunsa sun yi jazir saboda kuka da zafin da yakeji da fargabar ganin tamkar Mamey a mace take a kiɗime yanufo in da suke yana faɗin.
"Subahanallahi kai Jafar meya farune me ya sameta?".
Yayi tambayar hankali a tashe, tare da miƙa hannu ya ɗago kan Mamey dake kan kafar Ya Jafar yashiga girgizata yana kiran sunan ta.
"Aisha! Aisha!! Ummu Jabeer!.
Gani shiru bata ko matsi sai dai tana numfashi ya tsananta firgicinsa.

Hankali a tashe yakuma kallon ya Jafar wanda keta addu'o'in babu ko kakkautawa.
Mai da kan Mamey'n yayi ya kwantar kan cinyar kafar Jafar.
Kana ya juya a kiɗime ya fita a ɗakin da sauri ya nufi sashin mahaifinsa Lamiɗo.

Shi ko ya Jafar cigaba da maimata innalillahi yakeyi yana zubda hawayen.

A can ɓangaren Hajia Mama kuwa.
fitowar ta daga ɗakinta kenan cike da jin daɗin yadda bokan ya karfafa mata guiwa tanajin daɗi a ranta yanzu komai zai tafi mata yadda take bukata zata rabu da zugar yayan Mamey da ita duk kowa ya huta, tana fita ta hangi Abba ta window yafita daga cikin part ɗinsa hankali a tashe.

Fuska ta ɗan yamusa tazauna saman ɗaya daga cikin kujerun parlour'n, can kuma tamike kamar an tsikareta tabi bayansa da sauri.

Acan shashin Lamiɗo kuwa.
Da sauri Lamiɗo da Galadima suka mike, bayan Abba yagama sanar musu abin da ke faruwa.
A tare suka fito suka nufi part ɗin Mamey'n.

Lamiɗo na gaba Galadima da Abba na biye dashi suka shiga ɗakin, in da Abba yabar Yah Jafar a haka suka iske shi yana ganinsu ya miƙe da sauri Mamey yashiga nuna wasu Lamiɗo da hannu yana kuka yana nuna musu ita da kwatanta musu yadda Hajia Mama tayi mata.

Da sauri Hajia Mama ta turo kofar dan taga shigowar su Lamiɗo'n.
Jafar kuwa yana ganinta yashiga nunata da hannu sai kuma ya nuna Mamey'n yana cigaba da ƙwatanta yadda tayi matan shidai baki kam babu shi sai dai addu'o'in da kuma kukan dayake tayi.

Gaba ɗaya su suka maida kallonsu kan Hajia Mama nan take Lamiɗo da Galadima da Abba suka ɗiga ayar tambaya a kanta.
itako ganin bawai magana Jafar ɗin keyiba sai bata damuba bata kuma fahimci cewa sun zargi meyafaru ba kuma basu gane me. Jafar ɗin yake cewa ba da hakan ba.
Hajia mama kuwa cikeda da karfin hali irin nata na makiran mugaye mata tafara tafa hannu tana masar kwalla tana faɗin
"Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un Jafar me nake gani haka me yasami Mamey'n ku? kayi magana mana".

Sai kuma tasaki kuka mai haɗe da salati.
Lamiɗo ne yaɗanyi gyaran murya ganin Mamey'n tafara motsawa alamar tafarka daga nannauyan Baccin da take mikewa tayi zaune tare da zuba musu ido.
Da sauri suka ɗan matso gareta kana duk suka mai da hankalin su kanta.
Suna ce mata sannu Aisha, Amman shiru ba amsa.
Cikin tsananin sauri da tsoro Abba ya matso kusa da ita tare da zubawa yatsun kafarta ido mamaki cike da kiɗima yake kallon yatsun kafarta da suka fara sauya kamannin halitta suka koma kamar na tsuntsu.

Cike da alhini suma su Lamiɗo suke kallon yatsun kafar nata, hankali a tashe.
Cikin gigita Abba ya kamo hannunta tare da nunawa Lamiɗo murya a daburce yace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun Lamiɗo kalli yatsunta".
wani matsanancin tashin hankalin ne yakuma dabaibayesu lokacin da suka ga yatsun hannunta yafara komawa irinna fiffiken tsuntsu.
Gaba ki ɗaya su haɗa baki sukayi wajan furta "innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un hasbullahu wani'imalwakin". Sabida tsananin firgici da tashin hankali gaba ɗaya jikinsu rawa yakeyi.

Cikin matsanan cin tashin hankali Lamiɗo da cushewar tunani Lamiɗo ya juyo ya kalli Galadima murya a hargitse yace.
"Subahanallahi maza a kira Malam Musa yanzu nan".
Cikin hanzari Galadima ya amsa da. "To". Kana yajuya da sauri yafita.

Kan kace me labari yabaza masarautar Joɗo,
Batare da bata lokaci ba sakon kiran da Lamiɗo yayiwa Malam Musa ya isa gareshi.

Cikin ƴan daƙiƙu malam Musa ya iso cikin masarautar Joɗa Lamiɗo yabada umurnin a shigo dashi har cikin ɗakin Mamey.

Yana shiga kallonta malam Musa yayi cikin tashin hankali ya girgizata kai kana yakallesu Lamiɗo yace.
"Sihirine a kamata mai haɗe da tsafi kuma daga yanzu zuwa ko yaushe ko wanne lokacin zata iya juyewa daga mutun ta dawo tsunsuwa".
Salati suka ɗauka baki ɗayansu nan kuma ɗakin yakacame da koke-koke su Jamil da Jalal Affan Ummi Jafar yayin da duk muryar Hajia Mama yafi amo wajen kuka da shiga tashin hankali ziraran miraran.
(uhum makircin mugu kenan.)
(Sai daifa akwai kishiyoyi na gari da matsalar kishiya kan sasu kukan gaske wlh.)

Ranar kuwa wannan masarautar taga tashin hankali mara misaltuwa,
Jiƙe-jiƙe da hayaƙi da shafe-shafen magungun gargajiya babu wanda malam Musa baiba, kiɗima yasa sun mance da suyi amfanin da ayatul shifa.
Ganin anyi duk abinda za'ayi na gargaji abin yaci tura ne yasa hankalin.
Dr Aliyu yakasa ƙwanciya gani yake ko wata cutarce ta da ban haka yasa ya fitadaga ɗakin yatafi part ɗin sa,
kiran wasu manyan likitoci a bokansa.
Yasanar musu koda wani shawarin da zasu basu bayan sun gama wayar kuwa.
Kayan ai kinsa ya ɗauko yakomo ɗakin Mamey'n yayi iya gwaje-gwajen sa babu abinda ya gane na wani cuta ko wani abu.
Cikin takaici Malam Musa yace.
"Kama bar gwada ta babu wani cuta face sihiri".
Daga karshe dai dole ya hakura.
Ranar babu wanda ya rumtsa kusan a tsaye suka kwana nan cikin ɗakin Mamey'n ganin yadda gaba ɗaya kamannin halittarta ke juyewa, Gimbiya Aminatu tayi kuka iya kuka.
Lamiɗo ya kira Jadda ya sanar mishi halin da ake ciki tashin hankali iya tashin hankali Jadda da Sitti sun shigeshi nan suka fara shirin tahowa.

Can gabanin kiran sallar asuba lamari ya ƙara munana dan a lokacin suffar Mamey ta gama juyewa izuwa na tsunsuwar Boleru a gabana a gabansu Lamiɗo a gaban mafiya yawan al'ummar Masarautar Joɗa.
nan take kuwa Abba ya yanke jiki yafaɗi yasuma.
Cikin kiɗima Dr Aliyu yayi kansa yafara bashi taimakon gaggawa.
Mamey kuwa da yanzu takoma tsuntsuwa fara kaɗa fiffikenta tayi alamun son tashi take.

Ai kuwa tamkar al'mara sai gashi ta tashi firr ta fire tabi ta window dake a buɗe tayi tacikin Garden tashige cikin tawagarsa tsuntsayen dake wurin.

Innalillahi Jamil Jalal kuwa suma sumewa sukayi.
Cikin hanzari da kiɗima Lamiɗo da Galadima suka zo jikin window nan suka hango ta ta sauka cikin tsuntsayen kawai sai suka fashe da kukan tsoron al'amarin duniya.

Wani irin kuka Hajia Mama tasaka tana faɗin "wayyo Allah na waishin meke faruwa damune kam".
sai kawai ta yanke jiki tafaɗi ta kakkafe idanunta kamar wacce ta suma.

Ranar Hajia Mama haka tawuni tana kuka ta rungume Jamil da Jalal dasuke keta kuka kamar ransu zai fita.

Jadda da Sitti da Umaymah da Aunty Juwairiyya da babanta duk a ranar sukazo.
An kamo tsuntsuwar Boleru suna killaceta, yayinda aketa tururuwan zuwa ganin tsuntsuwar.

Ido da ido da Gimbiya Saudatu tazo da yake sokuwace.
Sai cewa tayi.
"Allah sarki wato al'haƙi kuikuyo ko sharrinta ya dawo kanta, ohoho larabawa an zama tsuntsuwar Boleru".
Toh fa daga nanne Magautan su Sheykh duk suka samu suka fake suka laɓe a bayanta.

Su kuwa haka sukaci gaba da kukan Hajia Mama ko uwartace ta mutu sai haka, duk wanda yaganta sai ta bashi tausayi akasin Lamiɗo da Galadima da suka sa zargi a kanta duk abin da take shirine da zallar iya tuggu munafurci da makirci.

Tun daga lokacin tsuntsuwar nan ko ince Mamey ko yaushe sai ana kamata ita kuwa tana firewa tana komawa cikin tsuntsaye ƴan uwanta.
Al'amarin ya magaga ya tada hankalin kowa.
Ana kamata zata zille ta fire ta koma cikin Garden ta zauna cikin tsuntsayen cikin masarautar Joɗa.

Duk wannan tashin hankali da ake ciki Sheykh Jabeer bashida labari dan lokacin yana karatu a jami'ar Madina sai dai kwata-kwata a lokacin hankalinsa yakasa ƙwanciya idan yakira wayar Mamey'n sai asa Aunty Rahma ta ɗauka tayi mishi mgn wanda ita kuma dama lokacin sun zo suna nan da Mamma.
Yadda Hajia Mama ke nuna tashin hankali tane yasa suka yarda da ita.

Wannan juyewar Mamey shine.
Sanadin da Jadda ya samu hawan jini kenan.

A ranar da dare Umaymah Mamma Aunty Rahma Aunty Juwairiyya Sitti duk sun gaza bacci, sun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login