Showing 279001 words to 282000 words out of 299804 words

Chapter 94 - GARKUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

17 Jul 2024

111386

cewa.
"Umaymah Ina su Ummey".
Kai Umaymah ta juya tana danne dariyarta tace.
"Sun tafi Side ɗin ta".
Da sauri tace.
"Harda Mamma".
Kai Ummi ta gyaɗa tare da cewa.
"Bakiga tun da yamma Mamma da Rahma sukaje suka gyara komai na Part ɗinta ɗinba.
Sabida Abban yasa an kawo mata sabbin kayan ɗaki sannan anyi duk abinda ya kamata".
Jinjina kai tayi tare da cewa.
"Ayyah".
Sai kuma tace.
"Bari inje in kwanta".
Sai da safe tayi musu.
Ta fita ta tafi.

Ishma da Hibba ta samu kwance bisa gadonta tuni sunyi bacci da alamun Hibba wayama takeyi tayi baccin.
Gefenta ta kwanta.

Su kuwa su Umaymah sukaci gaba da hira.
Sai kusan ƙarfe biyu ne da Afreen ta tashi Umaymah ta kaita ta bata mama tasha kana ta dawo da ita wai karta hana uwarta bacci.

Alhamdulillah fa komai na tafiya yadda ya kamata rayuwa ta miƙa.
Gsky tayi halinta.
Jadda da Sitti da Babansu Aunty Juwairiyya sun koma.
Haroon ma da Jannart sun da Hibba sun koma.

Saura Umaymah da Mamma Aunty Rahma.


Tuni Mamey ta koma Part ɗin ta.

Hajia Mama kuwa ta tabbata mai suffa hudu kafar ladin kogi, hannun fiffigen tsuntsuwar Boleru idanu na Duji, sauran jiki na mutun.

Ta zama abar kallo Abba kuwa ya danƙara mata saki.
Affan kuwa yana nan lfy da ƴan uwanshi.

Yanzu Shatu ta kusa wata ɗaya.

Wanda ya kama satin su Umaymah uku da zuwa kenan.

Abboi kuwa dasu Bappa sunje ga iyayen Rafi'a sun nemi aureta ga Al'ameen an basu kuma.
Kana su Bappa kuwa sun nemawa Salmanu auren Hasfi an kuma basu.

Zaune suke Umaymah Mamey Lamiɗo Galadima Abba
A hankali Lamiɗo ya gyara zamanshi tare da cewa.
"Toh Alhamdulillah komai ya wuce ya zama tarihi.
Manufar taruwarmu anan a kan Masarautar Joɗa ne.
Na gama zama da duk manyan fada mun gama tsaida zance duk kowa ya gamsu da batun Jabeer ya mulkin Masarautar Joɗa.
Toh amman inda gizo ke saƙan kun san ɗan naku, na kira sarki Jalaluddin akan batun to shi mgn ɗaya yayi cewa yasan Jabeer mai biyayya ne ga Khadijah da take ƙanwar mahaifiyarshi ma bare ke Aisha da Habibullah da kuke iyayensa yace ya sani tabbas in kuka cewa Sheykh ya mulki masarautar Joɗa ku bashi umarnine ba shawaraba tabbas zai yarda".
Cikin gamsuwa Galadima yace.
"Haƙƙun wannan haka yake tabbas zai yarda bisa dole bisa umarnin iyayenshi".
Cikin sanyi Mamey tace.
"In kuna son in bashi umarni zan bashi kuma nasan zai min biyayya to amman meyasa baza'a bawa wani cikin ƙannen mahaifinshi ba sai shi".
Shiru sukayi baki ɗayansu jin Lamiɗo na cewa.
"Sabida ina son masararutar Joɗa ta tsarkaka ta rabu da duk wata al'ada daba addiniba.
Na sani babu mai iya sarrafa Masarautar Joɗa ya juyata daga bahahuwa zuwa ba damiya ya kauda al'adar bidi'a ya wanzar da sunna sai shi.
Zai gyara masararutar ta yadda za'a dena zalama da son cutar da juna bisa kujerar zai sauyata ta yadda sai mai cikekken ilimin addini ne zai iya mulkarta."
Cikin gamsuwa Mamey tace.
"In sha Allah zaku sameni mai biyayya bisa umarnin ku na in bashi umarni kuma na sani zai min biyayya".
Cikin jin daɗi sukace to.
"Allah ya shige mana gaba".
Amin Amin sukace.

Sai kuma suka nitsu jin Lamiɗo na cewa.
"Alhamdulillah yanzu Ita matarshi ta kusa gama wonka tana gamawa zukjne Rugar Bani suyi kwana ɗaya daga nan su dawo su shirya suje Ƙasar Cameroon wurin iyayen Shatu kuma zasuje da Aliyu (Dr Aliyu) kenan da Basiru da Galadima domin su nemawa Jamilu auren Khadijah ƙanwar Shatu".
Cikin jin daɗi Mamey tace.
"Alhamdulillah to Allah ya kaimu".
Amin Amin sukace.
Sai kuma Abba yace.
"Jalal kuwa mun gama mgna da Abban Haroon kan batun Jalal da Hibba".
Cikin tsananin jin daɗi sukace.
"Alhamdulillah daga nan suka watse taron.

Washe gari su Umaymah suka koma.


Alhamdulillah yau Shatu ta gama arba'in.

Sosai Afreen tayi kuɓul-kuɓul da ita gwanin burgewa ta cika tayi kyau in ka ganta kamar yar wata biyu.

Sosai kuwa Shatu tasha gyara na musamman daga wurin Ummi da Mameynta.


A can ƙasar Cameroon kuwa.
Ba'ana ya gama shirin dawowarsa kab.

Wanda da azatonsa zai kaishi watanni uku sai gashi cikin wata biyu ya gama shirinsa.
Kana ya kamo hanya.

Yau Alhamis da misalin ƙarfe tara na dare yayiwa Rugar Bani diran miki...!






Ban samu nayi editing ba


By
*GARKUWAR FULANI*[4/3, 8:36 PM] +234 806 559 0880: Dirar mikiya tare da tawagar shi wanda Baroon na ciki.

A bakin titi motar ta sauƙesu kana suka ƙaraso cikin Rugar tasu da ƙafa.
Dai-dai bakin mashigar Rugar Bani ɗin suka tsaya, sabida ganin uban gayan tafiyar ya tsaya.
A hankali ya lumshe idonshi, tare da shaƙan sassayan iskan garin dake kaɗawa yana ratsa jiki.
Hannunshi ya buɗe ya waresu, ya tanƙwashe kansa bisa wuyanshi cikin muryar dake nuni da gskyar abin dake binne can ƙasan zuciyarsa yace.
"Uhummmmmmm ko wani ɗan adam yanada yanki na musamman da yake cikin bugun zuciyarsa.
Ni kuwa Rugar Bani ce bugun zuciya ta.
RUGAR BANI itace mahaɗin soyayya da Mata. Allah ka sani kaine ma sannin sirrin zuciyata ina son Shatu son da ni kaina ban san adadinshi ba.
Son da bana yiwa kaina shi.
Mata itace cikon farin cikina ban taɓa son wani abu a duniya sama da Shatu ba ya Allah ka yafe min kura-kuraina na baya, ka bani ikon samun Shatu, ka tsare min imanina duk da nasan.
Ban fiye aikata aiyukan gsky ba a rayuwata.
Amman son Shatu gsky ne a cikin zuciyata kuma tuban da nayi gsky ne.
Ya Allah ka jiƙaina ka tausaya min ka cika min burina ka ƙaddara Mata ta tabbata matar aure na, in rayu da ita inuwa ɗaya.
Domin itace sanyin idaniyata in ka samar min ita rayuwata zata inƙanta."
Ya ƙarashe mgnar cikin rauni da rawan muryar kana wasu irin tafasassun hawaye suna masu kwarya mishi.

Sheykh kuwa dake jin duk abinda Ba'ana yake faɗa bisa kiran da Baroon yayi mishi.
Da ƙarfi ya rumtse idanunshi, yana mai jin wani irin azabebben kishi mai masifar zafi da ƙuna yana caccakar zuciyarsa.

So yake ya tashi yaje suyi hira da Mamey'nshi Amman gaba ɗaya yanayi shi ya hautsine kishi ajalin maza.
Domin in mu mata kumallonmu ne tofa su maza yakan iya karsu.

A can Rugar Bani kuwa, cikin rauni Ba'ana yaci gaba da magana cikin sanyin jiki da raunin da bai taɓa riskar shi ba yace.
"Na sani na yarda akan komai ni bazan amsa sunan mai gsky ba ko mai tausayi amman akan tubana da Shatu ni mai gsky ne! Ya Allah ka mallaka min Shatu na yarda na gane babu wani sihiri ko tsafi ko boka ko dodon tsafin da zai mallaka min ita sai kai sarkin da bashi da tamka sarki buwayi gagara misali sarkin kowa na Annabi baban zara".
Kawai sai ga hawaye shar-shar suna kwaranya daga idanunsa rusunawa yayi ya durƙusa bisa guiwowinsa ya kafa kanshi cikin sassayan yashin garin.
Ya saki wani irin raunataccen kuka.

Gaba ɗaya yaran nashi shiru sukayi cikin tarin mamaki da tsantsar gaskata soyayya ba ƙarya bace shirya kuma ta Allah ce dan tuni sun san yabar komai na tsafi saidai wasu abubuwan dake jikinsa basu karyeba kamar ɓacewa har yanzu yana iya ɓacewa.

Saida yayi kuka mai tarin yawa kana suka miƙe suka nufi cikin gari.

A tsakiyar wurin garken al'ummar Rugar Bani ɗin ya tsaya ya juya gabas da yamma kudu da arewa.
Kana a hankali yace.
"Duk da son hanaku ci gaba da nakeyi, ya rigada Allah ya lamunce muku kuna ci gaba da izininsa."

Kai tsaye garken Bappa ya nufa bayan duk ya sallamesu sai Baroon kawai.
A hankali yasa ƙafarshi ya ratsa tsakiyar garken cikin ɗan ɗaga murya yace.
"Bappa".
Cikin wani irin masifeffen tashin hankali da firgici Bappa ya miƙa tsaye.
Tare da cewa.
"Na'am Ba'ana".

Giɗi da Seyo ne dake gefenshi suma suka miƙe da sauri cike da tsoron me zai faru.

A hankali ya zame ya zauna gaban Bappa kana a hankali yace.
"A nan a tsakiyar garken nan na rayu da ita tsawon shekaru goma sha biyu, na rayu da sonta kan gsky.
Koda komai ƙaryane Bappa ka yarda ina son Shatu son da bana yiwa kaina".
Cikin sauƙe ajiyan zuciya Bappa ya zauna jiki a mace hakama su Gidi da Baroon.
Cikin nitsuwa yace.
"Ba'ana yaushe ka dawo?".
Murya na rawa yace.
"Bappa yanzu na shigo Rugar Bani ko gidanmu ban jeba, ina so ka yarda cewa da gaske ina son Shatu".
Yadda yayi mgnar yasa Bappa jin wani irin rauni da tausayinsa a hankali yace.
"Na yarda Ba'ana na sani kana son Shatu".
Da sauri yace.
"Bappa ka tuna kun min al'ƙawarin aura min ita".
Da sauri Bappa yace.
"Na tuna Ba'ana ban manceba to amman al'ƙawarin Allah ya ture namu ya rigada Allah ya tsara Shatu ba matarka bace."
Cikin sauri ya miƙe yana cewa.
"A'a a'a bana son jin haka".
Yana faɗin haka yana yarfa hannun a haka ya nufi cikin gari Baroon na biye dashi a baya.

Shiru Bappa da su Giɗi sukayi cikin tarin rauni.

Shi kuwa Ba'ana a tsakiyar gidansu ya zauna gaban Bukar da Bugulu mahaifiyarshi.
Cike da mamaki suke kallonsa jin yadda yake kuka babu sassauci.
Cikin tsananin tausayi da so irin na iyaye da yaransu.
Sukayi kanshi cikin kula Bugulu tace.
"Ba'ana yau ranar farin cikine a garemu ba ranar kuka ba.
Kada kayi kuka muna cikin farin cikin ganin juna".
Ba mgn sai kuka.
Da sauri Bukar ya jawoshi jikinshi tare da cewa.
"Gaya min me ya saka kuka haka?".
Cike da rauni yace.
"Karo na forko dai a rayuwata Baba zan roƙeku in kuna da hali ku aura min Shatu ku dawo da ita gareni".
Ganin tsananin tashin hankali da yake cikine yasa sukace.
"To kwantar da hankalinka ina shine kawai burinka zamu dawo maka da farin cikin ka".
Da sauri yace.
"Allah Baba?".
Kai ya gyaɗa mishi cikin tausayinsa.
Shi kuwa jin hakane ya zame ya kwanta ya ɗaura kansa bisa cinyar babanshi yana sauƙe numfashin kuka shima Baroon gefe ya zauna.

Sheykh kuwa cikin tsananin tashin hankali na kishi ya rumtse idanunshi da ƙarfi.
Kana ya taune lip ɗinsa na ƙasa.


Shatu ce zaune ita da Mamey har cikin ɗakinta Afreen na hannun Ummi.
A hankali Mamey tace.
"Shatu".
Da sauri ta ɗago kanta ta kalli Mamey tare da cewa.
"Na'am Mamey na".
Gyara zama tayi tare da cewa.
"Shatu batun mijinki ne, nake son kisa baki a lamuransa".
A hankali tace.
"Mamey waɗannen lamuran ne?".

"Shin kina son Mijinki ya mulki masarautar Joɗa?".
Ta jefa mata tambayar kai tsaye.
Da sauri Shatu ta zubawa Ummey nata ido ta karanci yanayinta na ƴan wasu daƙiƙu kana a hankali tace.
"Mamey in dai kuna so ya mulka to nima zanso, hakan sai dai ina tsoro kada a sabautamu".
Da sauri Abba dake shigowa yace.
"A'a Shatu in sha Allah babu komai babu abinda zai faru sai al'khairi.
Burinmu ya mulki masarautar Joɗa ne dan ya gyara ta zama Tsarkakkiyar masarauta mai wadatar sunna da ƙarancin al'adun bidi'a".
A hankali ta gyaɗa kanta tare da cewa.
"Shi kenan Abba Allah ya sanya al'khairi yasa hakan ya zama ci gaba ga Musulunci da musulmai".
Amin Amin sukace.
Kana ta ɗan yunƙura zata tashi.
Ganin Abba ya shigo yana amsar Afreen tare da cewa.
"Ƴar lukuta".
Murmushi tayi kana ta kalli Mamey dake cewa.
"Ki fara nuna mishi amfanin ya mulki masarautar bisa hikima ta yadda zaki sa mishi abin a ransa ba tare da yaji dole akayi mishi ba".
Da sauri tace.
"Toh Ummeyna".
Har ta isa bakin ƙofar kuma sai ta tsaya jin Mameyn na cewa.
"Umurnine fa Shatu ki fara daga yau".
Ajiyan zuciya mai sauƙi ta sauƙe tare da cewa.
"In sha Allah kuwa Mamey".
Tana fita Ummi na biye da ita a baya.

A bakin ƙofar shigowa suka haɗu da Sheykh shida Affan.
Wuce sukayi kana su kuma suka fita.

Kai tsaye har bedroom ɗin suka wuce.
Suna hira ta tsakanin iyaye da yaransu.
Da sauri Sheykh ya ɗan ɗago ya kalli Mameynshi tare da sakin murmushi jin tana cewa.
"Jabeer wannan gemun haka ka ɗan rageshi mana ga saje ga gemu".
A hankali yace.
"Mamey bai min kyau bane?".
Da sauri tace.
"A'a wlh yayi maka kyau sosai ma fiye da zaton mai zato sai dai yasa kayi kwarjini da yawa ni kaina sai inji kana min kwarjini".
Dariya mai sauti yayi tare da cewa.
"Uwa mai daɗi Allah ya bar mana ke Mameynmu".
Dariya Abba da Affan sukayi tare zubawa Sheykh ɗin ido jin yana cewa.
"Toh gemu da saje ku kiyayi kanku da sa Mameyn Jabeer ganin kwarjini mai yawa".

Jamil da Jalal da Yah Jafar Imran dake shigowa ne suka haɗa baki wurin cewa.
"A to a haɗa harda mu dan muma kansu mana kwarjini yana mana yawa Hamma Jabeer".
Murmushi yayi kana suka shigo suka zauna suna hira cikin jin daɗi.
So a nanne yaji kaso 30 cikin 100 na azabebben kishin daya cakeshi ɗazu ya ragu.

Ita kuwa Shatu suna shiga kai tsaye bedroom nashi ta wuce.
Ta gyara komai ta killace komai ta ɗan ƙara gudun AC kana tasa turaren ɗaki Tuch me mai sassayan ƙamshi.

Kana ta dawo ɗakinta, kamar kullum bayan tayi wonka ta fitone.

Ummi ta shigo riƙe da kasko da rushi kaɗan a ciki.
Gaban gadon ta ajiye kaskon tare da jawo kujerar ƴar tsuguno mai rami ta turaren gyara ta ɗaura kujerar kana ta jawo wani kolba dake kan mirror ta buɗe tasa hayaƙi mai ƙamshi ya fara tashi.
"Zauna". Tace tana fita.
Da sauri Shatu ta zauna bisa kujerar tana mai jin yadda ƙamshin yake game jikinta,
Tabbas wannan turaren tana jin daɗin shi ita da kanta da kanta.
Dan ko fitsari tayi sai taji yana ƙamashi sai dai tana ji yana tsuketa.
Bayan kamar 30 minute Ummi ta kuma shigowa riƙe da cup da madarar gongoni a ciki mai sanyi da haɗin *Garin maɗi.*
Motsashi tayi da cokali tare da cewa.
"Yauwa amshi ki shanye".
Ba musu ta amsa sabida tana masifar jin daɗin haɗin.
Bayan ta shane ta ajiye cup ɗin kana ta matso gaban dreesing mirror'n humra mai sanyin ƙamshi ta murza a jikinta tare da zura wata tattausar rigar bacci royal blue mai ɗigo-ɗigon fari.
Rigar iya karya guiwa.
Turaren laylaytul sahrah ta fesa.
Kana ta zura jibajinta har ƙasa.

Su Sheykh kuwa bayan sun gama hirane.
Yasa hannunshi ya amshi Afreen da Mamey ke miƙa mishi tare da cewa.
"Kaita tasha mama".
To yace.
Tare da amsarta ruggume ta yayi a jikinshi tare da cewa.
"Sai da safe".

"Allah ya bamu al'khairi".

Amin yace yana mai fita, sai kuma ya tsaya jin Abbanshi na cewa.
"Kaje wurin Lamiɗo akwai takardun aiken masarautu da yakeso ya baka".
Cikin bin umarni yace.
"Toh".

Yana fita Part ɗin Lamiɗo ya nufa.

Gefenshi ya zauna ruggume da ƴarsa cikin kula Gimbiya Aminatu tace.
"Kai ɗa da daɗi ko Sheykh".
Murmushi yayi tare da kallon Afreen dake jujjuya ido tana lumshesu alamun bacci zatayi yace.
"Uhumm sosai ma kuwa ɗa kam da daɗi Gimbiya Aminatu".
Dariya sukayi baki ɗayansu.
Shi kuwa kissing goshinta yayi tare da sa mata al'barka.
Kana ya kalli Lamiɗo a fakaice yace.
"Abba yace akwai takardun da zaka bani".
Eh yace tare da miƙo mishi wasu takardu liƙe cikin wani, kekkyawan mazauni tare da tambarin hatimin masarautar Joɗa a jiki.
Hannu yasa ya amsa tare da cewa.
"Toh na menene?".

Cikin tsareshi da ido Lamiɗo yace.
"Aiken Masarautar Joɗa ce zuwa ga sauran masarautun gargajiya na Arewacin Nigeria, zaka kai musu ɗaya baya ɗaya".
Da sauri yace.
"Yaushe kuma aiken menene?".
A daƙile Lamiɗo yace.
"Gobe sai kaje ka dawo zan gaya maka na menene.
Waziri, Wambai, Galadima, Chiroma, Durbi, duk sun sa hannun".
Taɓe baki yayi tare da cewa.
"Sai dai kuma ai kai ba ubana bane da zaka wani tirsasani ka sani abu dole.
Harda wani wai gobe".
Ya ƙarashe zancen yana miƙewa tsaye riƙe da takardun.

Shi kam Lamiɗo murmushi kawai yayi ya bishi da ido.

Kai tsaye Part ɗin su ya nufa.
Ba kowa a falon haka yasa ya rufe ko ina ya kashe duk kayan wuta.
Kana ya wuce Side ɗinsa ruggume da Afreen.

A hankali yaja sassayan numfashi tare da shaƙar ƙamshin ɗakin.
Wutan ya kunna,
ido ya lumshe ganin komai fes-fes.

A can tsakiyar gado ya kwantar da Afreen tare da gyara mata kwanciyarta dan tuni tayi baccinta.

Addu'o'in yayi ya tofa a tafin hannunsa ya shafa mata.
Bathroom ya wuce.
Wonka yayi mai rai da lfy kana ya kimtsa cikin wasu tattausan riga da wondo pink guava color da ratsin Royal blue masu ɗan karen taushi.
OudKareem ɗinsa ya fesa kana ya fito.

A hankali ya ɗan zauna bakin gadon ba tare daya kashe wutanba.

Miƙe sawunshi yayi bisa gadon tare da ɗan zamewa ya kwanta rigingine.
Ido ya rumtse a hankali tuno kalaman Ba'ana a kan Shatu.

Ita kuwa Shatu a hankali taja ƙofar ɗakinta ta rufe Sannan ta nufi Side ɗinsa.

A hankali ta tura ƙofar tare da cewa.
"Assalamu alaikum".
buɗe idonshi yayi tare da zuba mata su.
Murya can ƙasa yadda bata jiba yace.
"Wa alaikassalam".
A zahiri kuma sai ya haɗe fuska tare da tsuke bakinshi.

Motsowa ta inda yake tayi tare da cewa.
"Yah Sheykh kayi bacci ne?".
Bai kulata ba kuma bai ɗauke idonshi a kanta ba.
Ƙara matsoshi tayi tare da zare hijabin ta ninkeshi tana cewa.
"Hamma Jabeer yau ba mgna ne".
Bakinshi ya taɓe mata.
Wanda hakan ya tabbatar mata yana fushi da itane wanda tasan fushin bai rasa nasaba da yadda yake buƙace da ita take kauce mishi.

Ajiye hijabin tayi a gefe. Sannan ta ɗan matso gaban shi.
Yatsun ƙafarshi ta ɗan ja tare da cewa.
"Nooryat".
Idonshi ya cire a kanta, yana mai ji kamar ya ruggumeta.
Fahimtar dafa gaskene fushin yasa ta ɗan hauro saman gadon.
A hankali ta sunkuyo kanshi tabi tsawon shi.

Hannunta ta cusa cikin rigar tashi, ta fara mishi tafiyar tsutsa ta gefe da gefen cikinsa.

Kana ta haɗa fuskarshi da nata.
A hankali ta kamo lip ɗinshi na ƙasa ta tsotsa tare da fidda sautin.
"Shyyyyuuyyh Yan Sheykh na tuba".
Miƙa mai tsawo yayi jin yadda takeyin ƙasa da hannunta.
Kana ta haɗe bakinsu wuri guda.
Wani irin lasa tayiwa harshensa wanda yasa yaji.
Sheykh ɗin shi ya amsa amo ya miƙe cike da zalama.
Da sauri yace.
"Barni".
Cikin raɗa tace.
"Naƙi".
Kanshi ya ɗan ɗago tare da tsareta da ido.
"Sai kuma ya tashi zaune yana riƙo hannunta jin tana kwance mishi zariyar wondo.
Da sauri yace.
"Wai menene hakan?".
Cikin tura baki tace.
"Abuna zan nema".
Bai san lokacin da dariya ta kubce mishi ba ganin yadda tayi mgnar cikin dariyar yace.
"Abun naki kuma babu inda zaki nemo shi sai cikin wondona?".
Ya ƙare mgnar tare da jawota jikinshi ya ruggumeta gam-gam yana kissing wuyanta.

Cikin jin daɗin ya huce da kuma son fara shigar mishi da ra'ayin sarauta tace.
"Mai martaba Lamiɗo Jabeer.
Allah ya nuna min randa zaka mulki masarautar Joɗa ka rabamu da duk wasu al'adu marasa kan gado".
Cikin yi mata kallon shauƙi yace.
"Yoh al'adun gida nama ai kin nuna ban isa in hanasuba bare na masarautar Joɗa".
Cikin cusa hannunta cikin ƙugunshi tace.
"Al'adar gidanka kuma wacce ta isa tafi ƙarfin ka hanata".
Hannunshi yasa yana kunce

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login