Showing 117001 words to 120000 words out of 299804 words

Chapter 40 - GARKUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

17 Jul 2024

111383

ta kalli Shatu, murya a daƙike tace.
"Bakiyi sa'an mijiba, yarinya duk da gashi kamar kinada nitsuwa".
Ido Shatu ta jujjuya cikin hular al'kyabbar jikinta.
Shi kuwa Sheykh Jabeer, ko ta kan mgnar ta bai biba,
sabida ai dama ya tsammaci, hakan
kai ta juyo ta kalli Umaymah cikin ɗagawa tace.
"A buɗe min fuskar amaryar in ganta da kyau, inga wanne irin idone da ita".
Bata rufe bakintaba taji yana cewa.
"Baza'a buɗe ba!."
Murmushi Umaymah tayi sabida tsamar Sheykh Jabeer da Gimbiya Saudatu wani lokacin yadda kasan shi ubanta ne, haka yake mata mgna da yanke hukunci kai tsaye a karan kanta ma bare akan abinda ya shafeshi.
ita kuwa Shatu a hankali take juya ƙwayar idanunta, tana kallon sawun Gimbiya Saudatu.
cikin al'kyabbar ta ɗan juya idonta da kyau ta maidasu, kan kyawawan fararen sawun Sheykh, wanda suke tamkar ka taɓa jini yayi yo tsalle ya fito, sabida taushi da laushin fatar
Wanda duk mutun mai zama da al'wala da yawan karatun al'ƙur'ani tafin hannunshi da ƙafarshi sukanyi wani kala mai masifar kyau da ɗaukar hankali koda baƙin mutun ne sai fatar hannunshi dana ƙafarshi sunyi kyau na musamman, hakama kuma fatar jikinshi wannan shine baiyanennen darajar zama da al'wala da yawan ambaton Allah kenan.

Da ƙarfi ta rumtse idanunta tare da buɗe su.
kan babbar yatsar kafarshi ta zubawa ido, sosai da sosai.
wani ɗan zane baƙi mai suffar tafiyar maciji ta gani.
sai dai bata samu ganinshi ras yadda take soba, shiyasa taketa zare ido,
shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya ɗan turo ƙafar damanshi gaba.
Dan ya gyara zaman ɗayan a kanta.
Hakanne ya bawa Shatu damar zubawa yatsun nashi ido, suna nan zara-zara alamun mutum ne mai matsakaici tsawo.
Ras zanen bindin maciciyar nan yake kan babbar yatsarshi.
har zuwa bisa rumfar ƙafar kamar zanen dayis,
cikin tarin mamaki da al'ajabi take bin zanen da idanunta.
har inda igiyar takalminshi ya tsare zanen.
Wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe a hankali.
sabida rashin ganin ƙarshen wannan zanen, da kuma inda ya nufa, da kuma ganin ya saman zanen yake.
Hankalinta kab ya tafi ga zanen shiyasa bata jin ta ƙaddamar da Gimbiya Saudatu ke zubawa ba.
Muryar ta taji da ɗan ƙarfi tana cewa.
"Bata da sunane? Ke me sunanki".
Ta ɗago kai da nufin yin mgna kenan sai kuma tayi shiru.
jin Umaymah na cewa.
"Sai kisa mata naki sunan, ba sai kiji namu ba".
A gyatsine ta kalli Umaymah kana, ta ɗan matso bakin kujerar,
hannu tasa ta ɗauki tupa cikin jerin ƴaƴan itatuwan da aka jera a gaban Shatu.
miƙa wa Shatu tayi tare da cewa.
"Kici kada ki tafi bakici komaiba,".
A hankali tace.
"Alhamdulillah!". Cikin sauri Gimbiya Saudatu tace.
"A ni ba'a zuwa sashina a tafi ba abinda akaci".
Hannu ta miƙa ta amshi tupan kana ta riƙe shi.
Shi kuwa Sheykh Jabeer miƙewa tsaye yayi alamun tafiya hakane yasa.
Suma suka miƙa suka fita.


Daga nan kai tsaye Side ɗin.
Baba Nasiru suka nufa.
A falo suka samu matarshi da yaranshi dama shi kanshi.
Bayan sun zaunane.
ya kallesu sama da ƙasa yace.
"Dama baku zauna ba, a hakama na ganku.
ba sai kun zauna ba".
Cikin sanyi ƴarshi Jamila ta ɗanyi ƙasa da murya tare da cewa.
"Ayyah Baba ka barsu mu gaisa".
Haɗe fuskarshi yayi sabida yasan irin masifeffen son da Jamila keyiwa Jabeer lokuta da dama, takanyi ta kuka in taji abubuwan da mahaifinta yakeyi mishi.
shi kuwa Sheykh Jabeer tuni ya zauna ya harɗe ƙafa,
Jamila kuwa cikin nitsuwa ta gaidasu kana.
Ta kawo musu abin sha,
Ummanta ku ko kallo Bata ishesuba yadda itama bata lallesu ba.

Haka dai suka fita suka tafi.
gidan Baba Basiru kuwa suna shiga ya tashi ya bar musu wojen.

Daga nan suka shiga gidan Barrister Kamal
Baba Kamal kenan.

Yana ganinsu ya tashi ya ruggume Sheykh tare da cewa.
"Masha Allah, Alhamdulillah yau dai Allah ya nuna min ɗana da matarsa".
Zama sukayi bayan sun gaisane yayi musu addu'o'in al'khairi.
Daga gidanshi gidan Dr Aliyu sukaje,
wanda yake mutun mai mutunci da kamar Barrister Kamal.
Sosai suka jima a sashinsa,
yayi musu addu'o'in da sanya al'khairi da al'barka.

Daga nan kuma sai Sashin Mom tsakar gidan Abbanshi.
Maman Imran, ba yabo ba fallasa ta amsa musu.
Daga nan wurin Amryar Abbansu sukaje, wanda suka sameshi a can.

Daga nan sukaje gidan Ya Hashim da sauran ƴan bappanunsu.
Gida na ƙarshe dai gidan Aunty Juwairiyya ne, can suka samu Hibba da Ya Jafar.
Bayan sun gaisane,
Umaymah ta ɗan matso kusa da ita cikin sauƙe numfashin gajiya tace.
"Ɗago kanki Shatu kinga nan ƙofar Aunty Juwairiyya ce, ga mijinta shine babban yayan Jabeer, kuma yanada matsalar ƙwoƙolwa.
Yanzu daga nan Side ɗinkin zamu wuce, wanda yana nan kusa da nasun. Sai gefen nakun kuma nasu Jalal ne."
A hankali ta ɗago kanta ta kalli Ya Jafar, yana riƙe da hannun Jabeer yana karatun shi a hankali.
Cikin sanyi tace.
"Ina kwana yaya!".
Kafaɗarta Umaymah ta dafa tare da cewa.
"Baya mgnar komai a duniya inba karatuba, sai dai yanajin komai kuma yana gane komai in an gaya mishi amman fa baya mgna kam in ba karatuba."
Cikin tsananin rauni da tausayawa,
idonta cike da ƙwalla tace.
"Allah sarki, Allah ya bashi lfy".
Karon forko kenan tunda suko fito dashi taji ya amsa addu'a duk da tarin addu'o'in da akayi ta musu sai yanzu taji yace.
"Amin ya Allah". Hakama Umaymah da Jakadiyarsu da Hibba sai dai duk ya riga su amsawa.
A hankali take ɗan satan kallonshi a fakaice.

Hibba ce ta janye mata hankali da cewa.
"Aunty Shatu kin gaji kam. muje ki huta, gashi azahar ta kusa ma."
Ɗan guntun murmushi tayi tare da cewa.
"Uhum".
Umaymah ce ta miƙe ita da Ummi kana sukace.
Taso mu tafi, yanzu Hibba zata cikaki dan zance."
Cikin murmushi Aunty Juwairiyya tace.
"Ayyah Umaymah ku bar mana ita mana".
Ummi ce tace.
"Lokacin sallafa ya ƙara to".
"Hakane kam". Juwairiyya tace tare da ɗaukar Foodflaks dake kan dinning table, tabi bayansu tana cewa.
"Hibba ɗauko sauran!".
To tace kana ta suggumi sauran tabi bayansu.

Nan suka bar Jabeer da Ya Jafar ɗin.

A babban falon suka zauna.
Aunty Juwairiyya da Hibba suka ajiye Foodflaks ɗin bisa Dinning table,
kana suka dawo tsakiyar falon.
Umaymah ce ta miƙe tare da kallon Shatu, tace.
"Taso mushiga ciki, kiga tsarin wurin naku".
Miƙewa tayi cikin alamun gajiya, domin zagaye masarautar Joɗa babban aikine mai zaman kanshi. Donma su sun saba, ita kuma bafulatanar dajine tafiya baya bamu tsoro.
Bayan Umaymah tabi, ta gefen Dinning area ta ɗan ratsa da ita,
Suka shiga cikin kitchen, juyowa tayi ta kallesu Ita da Hibba,
"Nan shine babban kitchen ɗin ki, dake babban falonki.
Shine wanda in kinada aiki mai yawa, kamar na salla ko azumi, ko zakiyi ki aikawa surakanki.
Hadimai zasu iya shigowa su tayaki."
cikin fahimta tace.
"Toh". Hibba ce ta ɗan ƙara so shigowa ciki tare da cewa.
"Kai wanga kitchen badai girmaba, gashi komai a tsare gonin kyau. Kalarsa green and white komai na ciki gwanin kyau".
Murmushi suka ɗan yi kana, Umaymah ta juya dasu.
Daga nan cikin kitchen ɗin ta gefen dama akwai wata ƙofar da sai ka hau stpes huɗu.
A gefen ƙofarne wani datsetstsen Fridge mai girma yake kwance.
Haurawa sukayi kana Umaymah ta tura ƙofar ta shiga.
Store ne mai zaman kanshi.
akwai komai na buƙatar rayuwa, sai dai ba mai yawa bane.
Shatu ta ɗan kalla tare da cewa.
"Ga kuma store ɗinki. Nan za'a ke aje miki duk wani abun buƙata".
Kai ta gyaɗa, kana suka fito.
Wata ƙofar daketa hannun hagu ta nuna mata suna buɗe wa suka fito.
Sai gasu bisa wata baranɗa mai girma, kana can ƙasan barandar fulawine da kuma pompona ke jere iya ganinka,
Daga sama kuma igiyoyin shanya ne da a ƙalla sun kai huɗu.
sai saman barandar kuwa, injin wanki ne.
Nan dai ta nuna mata komai na wurin kana suka dawo cikin gida.

Suna shigowa falo. Sheykh na shigowa.
A nitse yake taku, kanshi na sunkuye yana kallon wayarshi da yake lallatsawa.
Umaymah ce ta ɗan bi bayanshi tare da cewa.
"Zo nan Shatu".
Cikin zuba bayansu ido. Ta ɗan gyaɗa kai, tare da taka sawunta a hankali tabisu.
Hibba kuwa gefen Aunty Juwairiyya ta zauna.
Shi kuwa yana shiga falon nashi, ya juyo ya ɗan kalli Umaymah cikin kwaɓe fuska yace.
"Umaymah, Dan Allah ni bana son ana shigomin da wasu ababen cikin Side na, bare rayuwata, me wancan abun da kika kira zaizo yi anan?".
Ido ta kafeshi dasu hakane, yasa yayi ƙasa da kanshi.
tare da shigewa bedroom yana cewa.
"Dan Allah iya kar abun can falo".
Ƙeyanshi Umaymah ta zubawa ido.
"Wato ma wai wancan abun, lallai ma Jazlaan".
Juyawa tayi ta ɗan leƙo a corridor ta hangota, murmushi tayi tare da cewa.
"Taho mana".
Kai ta kuma gyaɗawa tare da ƙara saurinta tafiyarta a hankali.

Suna shiga falon, tayi wani irin ɓoyeyyen ajiyan zuciya mai sanyi,
sabida wani irin masifeffen sanyi mai gauraye da ƙamshi mai ɗan karen daɗi da taji ya bugu jiki da zuciyarta.
lumshe idonta tayi, kana ta buɗe su a hankali jin Umaymah na ce mata.
"Nan falonshi ne, namusamman ba kowa ke shigo mishi wurin kai tsaye ba.
dan ko Juwairiyya bata shigo mishi nan, kana akwai ƙannenshi ƴan uba maza da kuma Jalal basa shigo mishi nan.
Jamil kan shiga in baya nan in zai dawo shikeyi mishi shara da gyaran wurin.
Jalal kuwa yakan iya shekara ƙafarshi bata tako nanba.
Sai kuma Ya Jafar ɗin sa, shi kam bashi da hijabi da Side ɗin Jabeer, yakan shiga har cikin Bedroom nashi wani zubin har bathroom.
Sai kuma Haroon da Ibrahim su dama, dan su yasa aka gina sama wai masauƙinsu in sunxo.
To ammanfa in sunzo a ɗakinshi suke ko motsi zasuyi tare zasuyishi.

Sai kuma yayan Hibba, Hibbab shi na hannun damanshi ne.

Dan haka daga yanzu in dai yayi tafiya kece, zakiyi aikin da Jamil keyi".
A hankali tace "to".
Haura step ɗin Dinning area ɗin shi dake falon wanda akayiwa ƙawanya da wani irin labule mai masifar kyau.
Labulen ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu kama dana Daimond. wasu farare wasu Sky blue wasu Royal blue. suna da wani irin haske mai wal-wal. Cikinsa kuma.
Wani badaidaicin Dinning table ne mai kujeru shida nan uku nanma uku sai wani fridge ma daidaici. Gefensa show glass ne mai kyau wanda yake ɗauke da cups and plates and spoons and forks Mug. Da dai sauran ƙananan abeben buƙata.
sai woshing hand Baby, dake liƙe a can gefe.

sosai tsaruwan wurin yayi kyau, komai Sky blue and white. Abun sai ya zama kamar a duniyar taurarin yake yadda walwalin ke haska ko ina.
Falon kuma yanada ɗan karen duhu, domin saida Umaymah ta kunna musu wuta.

Bedroom nashi ta nuna mata da yatsa.
"Ga makwancinsa, sai kuma wancan ɗakin shi ba mai kwana a cikin ɗakine na musamman babu mai shiga ciki sai shi ni Lamiɗo Galadima, domin ɗakin aikinshi ne".
Ita dai da to take bin Umaymah, sabida sanyin falon yana gab da sata kuka.
Allah ya sani bata son sanyi ko kaɗan. Ta kuma lura su kuma mayun sanyi ne.

Falon suka fito. Nan dai suka samu su Hibba nata hira da Ummi.
Side ɗin ta suka nufa.
Cikin kula tace.
"Ga Side ɗinki ga falonki ga kitchen ɗinki."
Ta ƙarishe mgnar suna shiga kitchen ɗin. A hankali take kallon komai na Kitchen ɗin kalarsa Pink and white. Sosai tsarin wurin yayi kyau.
daga nan Dinning area Suka shiga ta nuna mata kana suka fito falon.
Suka shiga bedroom ɗinta komai ya tsaru.
Kuma komai sabone fil gwanin burgewa.
juyawa Umaymah tayi tare da cewa.
"Wancan ɗakin kuma masauƙi nane in nazo."
Cikin ɗan murmushi tace.
"Ayyah". Ƙofar Bathroom Umaymah ta nuna mata tare da cewa.
"Azahar tayi shiga kiyi al'wala kiyi salla sai kizo muyi Lunch".
to tace kana Umaymah ta juya ta fita.


Shi kuwa Sheykh Jabeer, yana shiga ya maida ƙofar Bedroom ɗin ya rufe shiyasa Umaymah bata gwada shiga da itaba.

Shi kuwa bathroom ya wuce wonka da al'wala yayi, ya sauya kaya. Kana ya fito cikin shigarsa ta musamman ya nufi. Masallaci.


Koda sukayi salla suka fito.
Falon ganin bata fito bane yasa, Umaymah cewa Hibba.
"Jeki kiramin ɗiyata". Da sauri Hibba ta juya ta nufi ɗakinta.
Kwance ta sameta bisa sallayar da tayi salla, ta kife kanta cikin hijabin jikin nata,
bisa dukkan alamu kuka takeyi.
jin shigowar Hibba ne yasa tayi saurin share hawayenta,
tare da juyowa,
cikin mamaki Hibba ta zuba mata ido.
A hankali tace.
"Aunty Shatu meya sameki kike kuka".
Murmushin ƙarfin hali ta ƙaƙalo tare da cewa.
"Kuka kuma Hibba".
Cikin sauri tace.
"Eh mana gashi idonki yayi ja".
Miƙewa zaune tayi da kyau cikin sanyi tace.
"No bacci na fara, shiyasa kikaga hakan".
Kai Hibba ta gyaɗa kana tace.
"To taso mu tafi falo Umaymah tace kizo muyi Lunch".
Hannu tasa ta ɗan shafa cikinta tare da cewa.
"Kamar na ƙoshi fa".
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
"Tab ai Wlh taso kawai mu tafi, dan Umsymah bazata barki bakici abinci ba".
To tace kana ta miƙe ta ninke sallayan. Sabida gajiya ne da bege da kewar yan uwanta ne ya sata kuka da kuma jin yunwar ta mutu a cikinta.

Suna fitowa su Umaymah duk suka miƙa, Dinning area suka nufa.

Bayan duk sun zaunane, Ummi, ta miƙe da nufin saka musu abincin.
Da sauri Aunty Juwairiyya ta miƙe tare da cewa.
"A a Ummi ki huta bari in saka mana".
Foodflaks ɗin dake kusa da ita ta ture tare da jawo wanda suka shigo dasu.
Ummi ce ta ɗan kalleta tare da cewa.
"Ya kika ture wancan?".
Baki ta ɗan taɓe tare da cewa.
"Uhummm wai fa Gimbiya Saudatu ce, ta turowa amarya abinci dan salon munafurci".
Wani irin kallon ƙasa-ƙasa Shatu tayi mata tare da zuwa abincin data buɗe ido, cikin mgnar zuciya take cewa.
"Uhumm wai zata cewa wata muna fuka, muguwa Itan ko meye sunanta!?".
Sai kuma ta kalli Umaymah jin tana cewa Juwairiyya.
"Ni zubo min na gidan Hajia Mama naga tuƙeƙƙen tuwone da biyar zogale".
To Aunty Juwairiyya tace kana ta zuba mata.
da sauri Shatu ta ɗan kalli Umaymah lokacin da aka saka mata mal-malan tuwon farar ɗanyar shinkafa,
tare da miyar a side sup.

Sai kuma ta juyo ta kalli Hibba da Ummi da tuni sun ja plate ɗin da Aunty Juwairiyya ta saka musu. Couscous and vegetables sup, mai ɗan karen kyau da ƙamshi.

Da sauri ta jujjuya kanta lokacin da Aunty Juwairiyya ta turo mata na plate ɗin gabanta, cikin sanyi tace.
"La da baki saminba". Da mamaki Umaymah tace.
"Sabida me?". Sunkuyar da kanta tayi tana tunanin.
suma ta yaya zata hanasu cin abincin. jin Ummi ta kuma mata tambayar da Umaymah tayi matane yasa ta ɗan kallesu.
Ta buɗe baki zatayi mgnar kenan.
Sheykh ya shigo da sallama, a bakisa.
kusan a tare, suka amsa masa.
A fakaice ya ɗan kalli Aunty Juwairiyya kana yace.
"Kije ki bawa Ya Jafar mgninshi".
To tace tare da miƙewa da sauri ta fita.
Ita kuwa Shatu, wata nannauyan ajiyar zuciya ta sauƙe.
Kana tasa hannunta ta ture plate ɗin gaban Umaymah tare da jawo na gaban Ummi da Hibba,
Ido suka zuba mata cike da mamaki.
Ita kuwa cikin sanyi ta kallesu tare da cewa.
"Dan Allah kada kuci wannan abincin.
Kuci wancan ne".
Jabeer dake ƙoƙarin shigewa falonshi ne, a ranshi yace.
"Uhumm lallai kam wannan abun wato itace ma zata zaɓa musu abinda zasuci".

Hibba kuwa da sauri tace.
"Aunty Shatu abincin gidan Gimbiya Saudatu fa kike cewa muci."
Ganin kallon mamaki da tuhuma da Umaymah da Ummi keyi matane yasata yin ƙasa da kanta cikin jin tausayinsu a ranta tace.
"To in bazaku cishiba, Umaymah bari ni in shiga kitchen nida Hibba yanzu zan girka muku duk abinda kukeso".
Ko inda suke Sheykh Jabeer da yanzu ya fito zai wuce baiba, yacewa Umaymah.
"Zan fita".
Juyowa tayi ta kalleshi tare da cewa.
"Allah kiyaye hanya, ya bada Sa'a".
Amin Amin yace, hakama Ummi tai mishi addu'a.

Ita kuwa Shatu kanta na sunkuye,
Umaymah ce ta ɗan kalleta cikin nazartan yanayin ta, da yin tunani hakafa ɗazuma taƙi shan madarar Barka da shigowa masarautar Joɗa da Hajia Mama ta bata,
ta kuma amshi tuppar da Gimbiya Saudatu ta bata,
yanzu kuma tace kada suci abinci Juwairiyya.
Wannan abun shi yafi komai tsayawa Umaymah a rai.
Yaya daga shigowarta zata kasabto wasu hasashen a ƙwaƙwalensu.

Kai ta jinjina tare da cewa.
"Hibba sa mana abincin Gimbiya Saudatu, muci".
Jin hajane yasa Shatu jawo Foodflaks ɗin ta fara saka musu.
Ita kuwa Hibba ta kwashe plate ɗin da Juwairiyya tasa musu ta kaisu kitchen.

Nan sukaci abincin kowa da abinda ke ransa.

Ita Shatu bataci na kirki bama.
Sabida ta lura da kallon da Umaymah keyi mata kamar da tuhuma.

Suna gamawa suka tattare wurin ita da Hibba.
tuni su Umaymah kuwa suna falon.


Suna gamawa suka fito falo.
da sauri ta kamo hannun Hibba suka wuce falonta har bedroom ɗinta.

Suna shiga Haroon, Jamil, suka shigo.
Shigarsu ba jimawa Jalal ma ya shigo.
Nan sukayi ta hira.
to ganin yanzu ta shigane yasa Umaymah bata kirata dan tazo taga ƙannen mijin mataba.

Suko. Suna cin abinci suka fita sabida kiran sallan la'asar,
daga nan kuma basu kuma shigowa falonba sai kusa goma na dare kafin nan kuwa tuni Shatu da Hibba sunyi bacci ma.


Washe gari ranar Laraba, da safe.
Aunty Juwairiyya ta shirya musu breakfast kamar yadda ta saba, koda su Umaymah basa nan, abincin Sheykh a sashinta yake duk da ma, yakan iya wata biyar baisa abincin nata a bakinshi ba.
sai dai Ummi Jakadiyarsu ta ɗan dafa mishi irin ababen da yafi so yaci lokuta da dama kuma na rayuwarshi da Lamiɗo yake cin abinci a Side ɗin kakarsa Gimbiya Aminatu shiyasa bai fiye cin wanda ake kawowa sashinsa ba.
Jalal Jamil Ummin suke cin wannan abincin.
To sashin Hajia Mama kullum za'a kawo Side ɗin shi.
Hakama gidan Barrister Kamal da Dr Aliyu yawanci suma sunasa ana kawo mishi.
kana gidan Baba Nasiru ma,
yawanci ana kawowa.
Especially kamar yanzu da su Umaymah ke nan.

To yauma haka abin yake tako ina an kawo musu breakfast, na maraba da zuwan amarya.

Koda suka zauna cin abinci.
Kamar jiya da dare, haka yauma Shatu ta ɗan kalli Aunty Juwairiyya cikin hikima tace.
"Aunty Juwairiyya asaka mana na gidan Gimbiya Aminatu".
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Wato kema irin mijin nakine, kuna son girkin Gimbiya, kunsan nata yafi naku na zamani daɗi da lfy".
Murmushi Shatu tayi cikin jin sanyi da daɗin basu fahimci manufarta ba.

Sun fara ci kenan.
Jalal Jamil suka shigo.

Dama Haroon, Ya Jafar, oga Sheykh Jabeer suna falonshi.
can Ummi ta kai musu nasu karin.

Cikin murmushin Umaymah tace.
"Yauwa Jalal kuzo nan, kuga Aunty Amaryankun."
Matsowa gefenta Jalal yayi tare da kallon Shatu a fakaice kana yace.
"Uhumm aini na santa, taje ta tasa min ɗan uwa gaba har cikin Office dinshi tana mishi ihu a kai".
Cikin sauri ta ɗan kalleshi tabbas ta ganeshi ta kuma tunashi Umaymah ta ɗan kalla tare da cewa.
"Sherri ne, Umaymah ni banyi ihuba".
Murmushi Jamil yayi tare da cewa.
"Eh ai ba ihun kukaba, shi da mijin naki duk bauɗaɗɗun mutanene, da zaran kin ɗan yi musu mgna da murya a sama to cewa sukeyi, wai kayi musu ihu".
Ya ƙarishe mgnar yana kallon corridor fitowa falonshi.
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
"Ga baki ga tsoro".
Aunty Juwairiyya ce ta nuna musu wurin zama tare da fara zuba musu abincin.
Ita kuwa Shatu murmushi kawai ta ɗan yi, sai taji hawaye

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login