Showing 276001 words to 279000 words out of 299804 words

Chapter 93 - GARKUWA COMPLETE HAUSA NOVEL

17 Jul 2024

111409

matuƙa Allah ya saka da al'khairi da kulawarka Alhamdulillah ga mahaifiyarku da ƙanwarku Allah ya bamu aron rai da lfy da ikon dawo muku dasu lfy".
Cikin jin daɗi Ummey tace.
"Bappa dani dasu ya kamata muyi godiya ba kuba kun gama min komai a duniya musamman Alhaji Abboi da matarsa Dedde sun min karar bani yar su duk da tarin son da sukeyi mata, suka amince muka dawo da ita nan, kana suka bawa Jabeer na aurenta."
Sai kuma ta juyo ta kalli Shatu tare da cewa.
"Kin min komai kin juya min Jabeer daga bauɗeɗɗen mutun zuwa dai-daice gashi yanzu har fara'a yakeyi ga Jalal na shima ya zama mai fara'a Jamil kuma ya nitsu.
Sai dai yanayin Affan nane ke min ciwo a rai, Affan ka dena kuka kajiko Shalelen Mamey".
Cikin rauni Affan ya matsota ɗaura kanshi bisa cinyarta yayi tare da sakin kuka.
Gaba ɗaya kowa yasan takaicin abinda mahaifiyarsa tayine yake sashi kukan.
A hankali Lamiɗo yace.
"Kayi shiru Affan ita rayuwa kowa abinda ya shuka zai girba".
Daga nan dai kuma akayi gaishe-gaishe.
Kana mazan duk suka tafi masallaci.
Matan masarautar Joɗa kuwa irinsu Gimbiya Saudatu da Gimbiya Aminatu dasu Mom da Samira duk ko wacce ta koma part ɗin ta cike da al'hinin sharrin ɗan Adam.

Matan kuma duk kowa tai al'wala sukayi salla, kana suka sake fitowa falo suka zauna suna cin abinci.

Affan kuwa Part ɗin shi ya koma ganin tashin hankali da yake cikine yasa Mami meda hankalinta gareshi.
Shi kuwa Rumaisa yayarshi ya kira tana ɗagawa yace.
"Uhummm tunda kullum kece kike zuga Hajia Mama kuna cutar waɗanda basu damu da kuba sai ki shirya kizo kiga halin da Mama ke ciki na girbar aiyukanta data shuka".
Cikin tashin hankali Rumaisa tace.
"Affan m.."
Bai bari ta ida zancenta ba ya katse kiran.

Su Sheykh kuwa dasu Haroon falon Sheykh Suka wuce.

Bayan anyi sallan la'asar ne,
Dedde ta kalli Ummey cikin kula tace.
"Toh Ummeyn Shatu mu zamu koma Rugar Bani, sai jibi zamu koma Cameroon da izinin ubangiji Allah ya kiyaye gaba ya tsaremu".
Cikin sauri Umaymah tace.
"Yanzu-yanzu zaku tafine?".
Cikin nitsuwa Dedde tace.
"Eh ai su tuni ma sun shiga mota nida su Khadijah suke jira".
Da sauri Umaymah tace.
"Ayyah ni kuwa ina son ku gaisa da Sittinmu da Jadda kafin ku tafi".
Da sauri Mamma tace.
"Ai sun iso suna Part ɗin Lamiɗo.
Amman yanzu zasu iso".
Da sauri Shatu tace.
"Toh Dedde am ki ɗan jira ku gaisa mana".

Suna cikin mgnar Sitti da Jadda suka shigo.
Allah sarki iyaye sai gashi Ummey a tsakiyarsu suna kuka gaba ɗayansu an rasa mai rarrashin wani.
A hankali Sheykh da Haroon suka shigo falon cikin tsiya Sheykh yace.
"Toh Alhamdulillah Jadda ni dai burina ya cika ko yau in kana son tafi ka gaida na gaba tunda kaga Mamey na ta dawo ta sameku cikar farin cikinta kusa mata al'barka".
Dariya sukayi baki ɗayansu kana su Dedde suka matso aka gaggaisa.
Sannan Jadda ya fita ya koma wurin su Lamiɗo.

Cikin sanyi Shatu ta kalli Deddenta Aunty Amina Hafsi Khadijah waɗanda duk suke cikin shirin tafiya.
A hankali tace.
"Allah sarki da mu ƙara kwana mana, yanzu kuma in kun tafi shikenan sai yaushe ni na zama a nan ina gefe duk ƴan uwa suna Cameroon".
Da sauri Ummi tace.
"Kema kina tare da yan uwanki ga Ummeynki ta dawo kusa dake ga kuma Junainah gani ga Hibba".
Da sauri suka kalli Jamil da ke cewa.
"Kuma zan auro mana Khadijah ma ta dawo nan zaku bani ita ai ko Dedde".
Ya ƙare mgnar cikin yanayinsa na wasa da dariya da kowa.
Murmushi Dedde tayi tare da cewa.
"Ai an baka ma Jamilu".
Dariya mai sauti yayi tare da cewa.
"Alhamdulillah".
Junainah kuwa a hankali ta matso kusa da Ya Giɗi tare da cewa.
"Ummey ni dai zan tafi tare dasu Yah Giɗi ban gaji da ganinsu ba".
Cikin jin kewar juna Ummey tace.
"Kije Junainah nima in Sitti na da Jadda sun tafi zamuzo tasu Mamma".
Da sauri tace to.
Kana ta kalli Shatu da tai shiru tana kallonta tare da cewa.
"Kada ki damu Addana nima zanke zuwa masarautar Joɗa".
Da sauri Jalal yace.
"Zaki dawo dai Junnu gamu ga Abbanmu ga Adda Shatunki ga Ummey".
Da sauri ta kalli Sheykh tare da cewa.
"Toh Yan Junaidun fa".
Dariya mai sauti Sheykh ya ɗan yi tare da cewa.
"Shima zai dawo nan".
Nan dai suka fito gaba dayansu dan yiwa su Dedde rakiya.
Jadda kuwa harda kuka yayi yana yiwa su Abboi da Bappa godiya.

A hankali Salmanu wanda yazo wurin ɗan Hafsi ne ya ɗan matso kusa da Ummey ƙasa yayi da murya tare da cewa.
"Ummey ki roƙa min su Abboi a bar mana Hafsi mana".
Dariya Ummey tayi tare da cewa.
"Alhamdulillah kuce duk ma zamu kwasosu mu dawo nan dasu".
Da sauri Salmanu ya shiga mota.
Shi kuwa Yah Al'ameen gefen Shatu ya ɗan kalla tare da yafitota.
Bayan Sheykh suna ɗan ratsa a hankali yace.
"Wannan ƙawar taki Rafi'a fa, da batunta yasa su Abboi zuwa gobe zasuje su zanta da manyanta sai jibi zamu koma".
Cike da mamaki tace.
"Lahh Yah Al'ameen ashe mgnar taku har ta kankama".
Da sauri yace.
"Ke da Allah ni kada kimin shele".
Baki ta ɗan tura tare da cewa.
"Toh sai na gaya ma kowa yaji".

Da sauri ya biyota ita kuwa cikin dariya tace.
"Ummey ashe Yah Al'ameen da Rafi'a munahikai ne soyayyar sirri sukeyi".
Dariya Sheykh yayi tare da juya mata ido alamun ai kema soyayyar sirri kikayi.

Haka dai suka shiga motocin suka tafi cikin farin ciki da kewar juna.


Cike da farin ciki suka koma cikin falon.
Da sauri Umaymah ta amshi wayarta da Ishma ke miƙa mata.
Amsa kiran tai da sauri ganin Abbansu Sheykh ne.
"Assalamu alaikum Abban Jazlaan".
Da sauri Abba dake part ɗin shi ya ɗan gyara zamanshi tare da cewa.
"Toh wai Umaymah ni sai yaushe zan samu in gaisa da Yayar takune kun taru kun riƙe min ita da hira".
Dariya mai sauti Umaymah tayi tare da cewa.
"A a sai mun koma mana".
Da sauri yace.
"A a dan Allah kada muyi haka dake, kinga yara na cike nan ki kirata gefe kice mata ina kiranta".
Murmushi tai tare da cewa.
"Nawa zaka biya".
Dariyar jin daɗi yayi tare da cewa.
"Kujerar hajji tayi miki".
Da sauri tace.
"Sosai ma kuwa yanzu kuwa zan cika aiki".

Tana gama wayar ta yafito Mamey suka tafi ɗakin Ummi ta gaya mata.
Cikin jin kunya Mamey tace.
"A'a kinga dama ke tsiyarki yawane da ita Khadijah ya da girmana kuma ana cike yarana da jikoki ku wani kawo min batun inje gareshi".
Dariya Umaymah tayi tare da cewa.
"Toh shike nan ni dai yar aikece.
Cikin yanayin tarin shaƙuwarsu ta ya da ƙanwa Mamey tace.
"To ai dai ya bari sai dare ko".
Da sauri Umaymah tace.
"Ohoh anaso ana kaiwa kasuwa".
Hararan wasa tayi mata kana ta fito.

Nanfa sukaci gaba da hira.
Ana gab da kiran sallan magriba.
Suka juyo ehu da kururuwar Hajia Mama da faɗe-faɗen da takeyi.
Da sauri Sheykh ya nufi ɗakin daya rufeta, yana buɗeta.
Ta fito tanata yayyarfa hannunta tare da cewa.
"Wayyoooooooo zan zama tsuntsuwar Boleru".
Da sauri yabi bayanta tuni ta iso falo.
Tana kaɗan yatsun hannunta da sun fara komawa na tsuntsuwar Boleru.
Cikin tsoro da mamaki da tausayi Mamey tace.
"Innalillahi Jabeer kamanninta fa na sauyawa".
Da sauri ya iso, yana mai kara wayarshi a kunne sabida kiran da yayiwa Affan.
Yana ɗagawa yace.
"Affan kazo kayi maza kazo".
Cikin tashin hankali da tsoro Affan yace.
"Toh".
Yana fitowa yayi kiciɓis da Rumaisa a tare suka nufi.
Part ɗin Sheykhhhh.

Umaymah kuwa Abba da Lamiɗo ta kira ta gayawa.
Kusan duk a tare suka iso.
A tsakiyar falon suka sameta.
Tana yayyarfa hannunta tare da cewa.
"Na ji daɗi zan zama tsuntsuwar Boleru zanyi ta firewa kamar jirgi".
Sai kuma ta kalli Sheykh da yake ta karanto Ayatul shifa yana tofa mata. Dariya tayi tare da cewa.
"Kai bar ɓata lokacin ka a kaina ai al'haƙine kuikuyo ya dawo kaina wayyo ni Halima naga ta kaina".
Da sauri Rumaisa ta iso gareta ihu tasa tare da kururuwar ganin yadda kafafunta duk suka zama cingil-cingil kamar na tsuntsuwar ladin kogii.

Da sauri Rumaisa tace.
"Dan Allah Affan mu kaita gidan bokan ya karya sihirin".
Cikin tarin takaici da zubda hawaye Affan yace.
"Banza mahaukaciya gafalelliya ni nan Affan babu gidan wani mushirkin mugun kafurin bokan da zanje.
Anayi mata addu'o'in kina batun aje gidan boka".
Cikin ihu tace.
"Abba dan Allah mu kaita".
Da sauri Abba yace.
"In kika sake kirana kika haɗani da Allah dan inje inda zan tsaɓa mishi zan tsine miki shasha mara hankali".
Sheykh ne ya ɗan kalleta cikin sanyi yace.
"Aunty Rumaisa ki bari ki nitsu muyi mata addu'a in sha Allah zata samu lfy".
Da sauri tace.
"An ƙi ɗin sabida ba uwarka bace ai shiyasa zakace haka".
Sai kuma ta zaro wayarta ta kira bokan bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga cikin kurma ihu da kururuwa yace.
"Nima ƙonewa nakeyi, ita kuma a haka zataci gaba da rayuwa ita ba mutumba ita ba tsuntsuwar Boleru ba, zata zama aya ta yadda duk wanda ya ganta sai ya tambayi mai tayi. Domin dama shi mugunta ɗan aikene yakan iya dawowa wurin wanda ya aikeshi.
Sai kuma ya kurma ihu da ƙarfi.
A nan ya faɗi yana burburwa.
Ya shiga gudu yana kwaɓe kayansa yana cewa wuta na ƙonashi ya zama mahaukaci tubran.

Ita kuwa Rumaisa kamo Hannun Hajia Mama tayi suka tafi Part ɗin ta.
Lamiɗo kuwa kai ya jinnina tare da cewa.
"Ƙarshen mugu kena".

Sheykh kuwa da Mamey da sauri suka zauna gefen Affan dayake kuka kamar ya haɗiyi zuciya cikin sanyi Sheykh yace.
"Affan kayi haƙuri ka bar kuka in Sha Allah zamu dage da addu'a zata samu lfy".
Cikin shassheƙan kuka. Ya tashi yabi bayansu.
Sabida ita dai uwa duk yadda take uwace.


Abba kam juyawa yayi ya fita ko a jikinsa.
Domin shi tausayin Affan ne kawai ke cinsa a rai.
Lamiɗo da Gimbiya Aminatu da Galadima ma kwaffa kawai sukayi suka fita.

Umaymah kuwa cikin zafin zuciya tace.
"Wlh Ni dai ko duk zaku yafe mata ni ba yafewa zanyi ba".
Da sauri Sheykh ya kalleta idonshi cike da hawaye.
Sai kuma ya kalli Mamma da Aunty Rahma dasu Yah Jafar da suma suke cewa basu yafe mata ba.

Jin an kira sallan magriba ne yasa duk suka miƙe suka tafi masallaci.


Ana idar da sallan Isha'i Sheykh ya nufi Part ɗin Hajia Mama kuka sosai ya sameta tanayi Affan na gefenta shima kukan yakeyi

Addu'o'in ya rinƙa tofa mata.
Har saida yaga tayi bacci kana ya fita.
har yaje bakin ƙofar fita sai kuma ya juyo jin Affan ya ruggumeshi ta baya yana kuka tare da cewa.
"Ngd matuƙa Hamma Jabeer Allah ya bar zumunci da ƙauna".
Cikin rauni yace.
"Amin Amin Affan".
Daga nan suka fita kowa yayi Part ɗinsa.


Hira sosai sukayi ranar hirar yaushe gamo kusan sai gab da kiran sallan forko kana duk suka tashi sukayo al'wala sukayi ta nafila suna godewa Allah.

Washe gari da safe gaba ɗayansu suna falon Abba ya shigo.
Suna gaisawa yana kallon Umaymah dake mishi dariya ƙasa-ƙasa.

Hajia Mama kuwa da taimakon addu'o'in da Sheykh yake mata hankalinta ya ɗan dai-dai-ta yadda zata fi jin ciwo da zafin sauyawar halittarta, da gaba ɗaya yanzu kafafunta sun zama na tsuntsuwar ladin kogi, yatsun hannunta kuma sun zama fiffizgewa tsuntsuwar Boleru, idanunta kuwa kamar na tsuntsuwar Duji sunyi ƙuru-ƙuru tamkar an taka kwaɗo.

Wannan al'amarin yasa Lugga da saƙo mutanen masarartar Joɗa shigowa sunayi mata kallon sabuwar halitta masu dariya nayi.
Tsananin tsoron Allah ya wadaci zuƙatan mata da mazan Masarautar.

Bayan Aunty Juwairiyya ta dawone take suffantawa su Mamma yadda Allah ya maida Hajia Mama.
Sosai jikinsu yayi tsanyi.

Umaymah ce ta ɗan kalli Shatu da yanzu ta fito wonka cikin shirin baccinta.
"Naji kamar Jazlaan ke kiranki".
Umaymah ta faɗa cikin kulawa.
Da sauri tace to kana ta miƙe ta funi Side ɗinsa.
A falo ta sameshi gaban steps ɗin hawa wurin Dinning area.
Hannunshi na cikin zirin zirin igiyoyi dake sarƙafe da duwatsu masu daraja sheƙin Daimond.
Wanda a ciki yake liƙe da CCTV camera ta sama wanda da wuya mutun ya iya ganeshi.
Ruggume shi tayi ta baya tare da cewa.
"I miss you so much Sheykh Malam akarmakallu Dr Hamma Jabeer".
Murmushi mai cike da jin daɗi yayi kana ya juyo ya ruggumeta.
A hankali tasa tafin sawunta saman rumfar sawunshi kana tasa hannun ta saƙalo wuyanshi.
Ya zama tana lafe a jikinsa.
A hankali ya fara taku a haka ya nufi Bedroom.
Suna shiga ya maida ƙofar ya rufe.
Da cikin tsokana tace.
"Yah Sheykh Haroon".
Baki ya ɗan taɓe tare da cewa.
"Wannan jarabebben tun yaushe yaja Ƴar mutane suka shiga ɗakin nan suka rufe ko kunya babu".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Mutun da matarsa".
A hankali ya sunkuyo kan gadon ya kwantar da ita tare da yi mata rumfa da ƙirjinshi kana yace.
"Okay to ai nima gani da matata".
Da sauri tace.
"Yah Sheykh jego nakeyi, kwana Afreen goma kacal fa".
Hancinsa ya manna da wuyarta tare da cewa.
"Eh mu samo mata ƙanwa ko ƙani mu samu irin tagwayen Nana Faɗima".
Da sauri tace.
"Uhum wuya".
Kissing lips ɗin ta yayi tare da cewa.
"Ke ai yar baiwa ce nine zanke mana laulayi da naƙuda".
Murmushi tayi tare dasa tafin hannunta ta tallabe kanshi a hankali tace.
"Harda naƙudar ma Yah Sheykh".
Da sauri yace.
"Sosai ma kuwa ai na Afreen ɗinma ni nayi naƙudar ke ba kallonki kikeyi hankali konceba..".
Dariya mai sauti tayi sabida lbarta mata yadda yaji a lokacin da karayar da yayi ya ƙara da cewa.
"Mata kuna jin azabar duniya akan hayhuwa bamu da abinda zamuyi muku kuji sanyi sai kyautata muku da nuna muku soyayya in kuna matsayin matanmu iyaye kuwa ayi musu biyayya da tausayawa da kulawa shine kaɗai tukuicin wahalarsu dan bazamu taɓa iya biyansu ba inaji kamar ko wuta Mamey tace in shiga zan shiga dan biyayya sabida azabar da naji wanda nasa irinshi koma fiye da haka taji.
In matsayin yarane kuma mu jiƙansu mu sosu mu kula da amanarsu da Allah ya bamu".
Cikin sauƙe numfashi tace.
"Yauwa niko Yah Sheykh inada tambaya".
Rigarta ya fara turawa sama yana shafa cikinta tare da cewa.
"Allah yasa na sani Boɗɗona".
Juyowa tayi ta ɗan kalleshi tare da yin murmushi kana tace.
"In sha Allah ma ka sani".
Murmushi yayi tare dasa yatsarshi cikin hudar jibiyarta tare da cewa.
"Uhum ina jinki".
Kai ta gyaɗa kana tace.
"Yauwa Dr dama ina son kayi min ƙarin bayani ne kan batun laulayi cikin Afreen da kai tayi."
Murmushi yayi tare da cewa.
"To ina jinki tambayi in baki amsa in na sani".
Muskutawa tayi ta fuskanceshi da kyau tare da cewa.
"Bayanin sanadin faruwar haka.
Nake son sani.
Don yana da kyeu mugane dalilin hakan.
Shin yawan shaƙuwace da soyayya tsakanin ma'aurata kawai ke sa hakan ya faru.
Ko kuma wani biology ne na Ubangiji?.
Yake sa miji yayiwa matarsa laulayin ciki a wasu lokuta?".
Murmushi mai cike da shauƙi yayi tare da cewa.
"Eh wato kina son kiji ba'asin miki laulayi ko irin kin huta ɗin nan".
Kai ta gyaɗa mishi tare da cewa.
"Eh mana kaga in zakayi ta mana laulayi da naƙuda to ko duk shekara zan haihu ba matsala."
Lakace hancinta yayi tare da cewa.
"Uhum".
Kiss ta manna mishi a goshinsa tare da cewa.
"Dan Allah gaya min".
Zamanshi ya gyara kana yace.
"Toh Aish ba yawan shuƙuwa ko soyayya ba ne ke sa miji yayiwa matarsa laulayi.
Asali ma ai dangantakar ba tsakanin matar da mijin ba ne.
Dangantakar tsakanin ɗan ne da ubansa."

Sai kuma ya ɗan ƙara jawota jikinshi tare da cewa.
"Samuwar ɗan, ana nufin kamar yadda ya shafi uwar kai tsaye, to haka kuma ya shafi uban.
Don haka, irin yanayin da ta ji saboda zuwan yaron, shi ma yakan iya jin hakan.
Sai dai kawai nasa bazai kai yawan na uwar ba, saboda ta fi shi kusance da ɗan, kasancewar yana jikinta kin gane ko?."
Cikin gamsuwa ta gyaɗa kai tare da cewa.
"Na gane na gamsu.
To kuma batun naƙuda fa da kace kayi min.
Shin dama na miji kan ji ciwon naƙudan matarsa kamar yadda wasu mazan ke jin ciwon laulayi ciki ne?
Ko dai kwatakwata babu wannan!?".

Kanshi ya ɗan cusa tsakanin wuyanta da kafaɗarta tare da shaƙar ƙamshin jikinta cikin fahimtarwa yace.
"A dai iyakar abinda muka sani zuwa yanzu, wanda kuma bincike da gwaje-gwace likitocin duniya suka tabbatar shi ne, namiji ba ya iya jin ciwon naƙuda.
Sai dai yakan jin tsananin damuwa da ciwon rai ne, maimakon ciwon jiki da raɗaɗi da mai naƙudar take ji.
Sai dai bincike ya tabbbatar da cewa yana da tasiri sosai wurin sauƙaƙa wa matar ciwon naƙudar, idan zai kasance tare da ita har ta haihu".
Da sauri tace.
"Kamar yaya to dan yana kusa da ita zataji ciwon ya sauƙaƙa?".
Kai ya ɗan ɗago ya kalleta tare da cewa.
"Domin idan ya zauna a gunta, musamman in zai riƙe mata hannunta ko ya riƙa ɗan shafa goshinta yana yi mata sannu kamar dai yadda nai miki ta miki lokacin kina naƙudar gab da haihuwar.
To tabbas zataji sauƙi da sassaucin naƙudar da samun haihuwa a sauƙaƙe da izinin ubangiji.
Saboda yayin da suka kasance a haka, jikin matar yana samar da wani sinadari da ake cewa oxytocin , wanda yake sanadin tsattsafowar wannan ruwa mai tsantsi to zai sauƙaƙa fitar yaron daga jikinta.
Da iznin Allah".
Cikin gamsuwa ta sauƙe numfashi tare da cewa.
"To kai kuma kace harda ciwon baya kaji ranar da zan haihu a lokacin ma meya kawo hakan?".
Cikin sanyi ya jujjuya kanshi tare da cewa.
"Allahu ahlamu, kawai abinda nasa a raina wannan wani ikone da ƙudurar ubangiji daya gwada a kanmu wanda tabbas na taɓa riskar makamancin lbrin miji yayiwa matarsa naƙuda, to amman dai a likitance bamu ganoba tukun, dan haka wannan fagene na ubangijin sammai bakwai da ƙassai bakwai, shiyasa nasan zafi da ciwon da mata kanji yayin haihuwa".
Cikin gamsuwa tace.
"Ayyah sannu Yah Sheykh".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Ke kam ba cewa kikayi in dan zanci gaba dayi miki laulayin ciki da naƙuda ba, ko duk shekarama ki haihu ba matsala ko".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Eh mana".
Murmushi yayi tare da jawota jikinshi yana mai sa hannunshi ɗaya zai zare boxes ɗinsa.
Fahimtar inda ya dosane yasa ta miƙe da sauri tare da cewa.
"Bari inje wurin Ummey na naji alamun Afreen ta farka".
Fuskarshi ya kwaɓe tare da cewa.
"Kai Aish ni dai banjiba".
Cikin son zille mishi tace.
"Kaji can muryarta tana kuka".
Komawa yayi ya kwanta
Cikin jinjina ƙudurar ubangiji yace.
"Toh ɗaukota kuzo".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Toh". Kana ta fita.

Tana fita ya maida kanshi bisa pillow'nshi yana tasbihi da girman zatin Allah daya samar da cikekkiyar dangantaka tsakanin uwa da ɗanta ta yadda ko bata tare dashi in zaiyi kuka ko ya tashi bacci.
Mamanta zai sanar mata.

Ita kuwa Shatu tana zuwa ta wuce bedroom ɗin Ummi.
Umaymah da Ummin kawai ta samu sunata hira da dariyar Abba daya shigo da kansa ya kira Mamey wai tazo su gaisa da abokanshi, daga nan yayi Part ɗin shi da ita wanda yake kusa da nata.
Umaymah na kwance Afreen na gabanta Ummi kuwa zaune.
A hankali ta zauna gefensu tare da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login