Showing 90001 words to 93000 words out of 299804 words
ɗan buɗasu alamar, ban damuba.
Sarkin Shaɗi kuwa bai kallesu bama.
Wani irin zabura Jabeer yayi cikin tsananin firgici da kaɗuwa lokacin da yaga wani irin h ....!
By
*GARKUWAR FULANI*Ganin wani irin hayaƙi fari tas yana fitowa, tako wacce ƙofa na jikin curin.
Da sauri Galadima yasa hannunshi ya kamo hannun Jabeer yaja da ƙarfi.
Alamun ya nitsu ya zauna, cikin mamaki ya zubawa tarin hayaƙin dake bulbulowa daga ƙofofin ramin shirgegen curin.
Su kuwa ga ɗayansu hankali konce suke zaune.
Ido ya zuba musu tare da cewa.
"Me hakan?".
Da sauri Lamiɗo ya girgiza mishi kai hakanne ya sashi jan gajeren tsaki tare da cewa.
"Nifa ba son wannan soki burusun naku da surkunlenku nakeyi ba. Me gamina da ku da tsare-tsaren naku. Fisabilillahi me wannan?".
Cikin faɗa Lamiɗo ya sa hannu zai bugi bakinshi da sauri ya kauce.
Cikin hatsala Lamiɗo yace.
"Wannan bakin naka da baya mutuwa, komai sai kayi inkarin a kai tabbas sai na kashe bakin nan".
Wani kallo yayi mishi tare da cewa.
"Uhumm ai babu mai kashe bakin Muhammad Jabeer sai Allah".
Ganin zaija suma suyi surutune ya sasu kauda idonsu kanshi.
Bayan kusan mitinu goma, sai ga hayaƙin nan ya bar fitowa,
Sai wani irin huci.
Da sauri Jabeer yace.
"Nifa zan tafi, inma kun mance in tuna muku yau jumma'a ace, inada abinda yafi wannan abun naku mahimmanci a rayuwata ta duniya da ƙiyama, yanzu gashi har kusan sha biyu."
Murmushi sukayi baki ɗayansu ba tare da sunce mishi komaiba.
Sabida dama sun san za'ayi haka kam.
Sabida kowa ya sani shi Jabeer yana barranta da duk irin waɗannan ababen gado na sarauta shiyasa sarautar kanta shi bata ɗaɗashi da ƙasa ba.
Da sauri ya buɗe siraran idanunshi da kyau.
Sabida ganin wani irin ƙaton maciji ya sako kanshi cikin babban ramin da yafi girma.
Da sauri yace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun!."
Sai kuma ya zubawa maciyar nan idanu.
Tana fitowa cikin ramin ta, zuɗuɗuɗuɗuɗu. Haka yake zaro jikinshi.
Haƙiƙa dole duk wanda bai taɓa ganin macijinba bai kuma san da zamanshi ba, dole ya razana.
Dan ma shi zuciyarshi na cike da tsoron Allah so irin wadannan ababen ba kasafai suke firgitashiba.
tashinsa fahimtar ko wani ɗan abin sihirin za'ayi mishi ne.
Wani dagon numfashi yaja mai ƙarfi ya sauƙe ganin. Yadda macijiyarna taketa keta fitowa taƙi ƙarewa.
Su dai su Lamiɗo shiru sukayi a zaune.
Saida ta gama fitowane, ya rage iya bindinta sai gashi ta fito bindinta na kananmaɗe da wasu irin kitsastsun bulalin da ka gansu kasan tsoffine.
A hankali ya turo bindinshi gaban Lamiɗo,
Ya ajiyesu, sai kuma ya sumkuyo da kanshi ya zaro harshensa ya rinƙa lasar bulalin nan saida suka fito ras kamar an wonkesu.
Kana ta juya ta nufi cikin curin zuɗuɗuɗuɗuɗu ta koma,
Kamar forko sai ga hayaƙin.
Wani nannauyan numfashi Jabeer ya sauƙe tare da cewa.
"Uhum inda ranka kasha kallo. Oh ni Muhammad Jabeer an ɗauramin jakar tsaba za'a jazamin kaji su bini su tsastsageni.
Du wai wadannan abubuwan na menene wai dan Allah".
Ya ƙarishe mgnar yana kallonsu baki ɗayansu,
fuskarshi cike da alamun fargaban gudun saɓawa ubamgijinshi.
Su kuwa saida hayaƙin ya gama ɓacewa baki ɗaya sannan Lamiɗo ya fara miƙewa kana suma duk suka miƙa.
Sarkin Shaɗi ruggume da bulalin.
Juyawa sukayi zasu nufi hanyar da zata ɓullo ta falon Lamiɗo,
da sauri ya ɗan motsosu tare da cewa.
"Dan Allah shi wannan abun me amfanin zamanshi a nan? Wurinda Kum san duk baƙin da suke zuwa tako wani sashi na duniya ganin abin tarihin masarautar Joɗa muna kawosu nan.
Yanzu in wata ran yunwa ta koroshi ya fito ya cutar da mutane fa me zakuce?".
Cikin ƙosawa da mgnar Galadima ya gyara riƙon da yayiwa sandarsa cikin sanyi yace.
"Bata tare da yunwa, macijiyar da duk wata sai an ajiye mata motar ƙwai a cikashi da kiret-kiret na ƙwai shine abincinsa".
Da sauri Galadima ya nufi hanyar fita.
Lamiɗo kuwa tuni sun tafi.
Ganin sun tafi sun barshi a nan a tsayene. Yasashi sauƙe numfashin tare da juyawa ya nufi, ƙofar da zata sadashi da falonshi.
A hankali yake taku, cikin kasala da mutuwar jiki, da mgnar zuci.
"Wai ya zanyine? Wanna wacce irinyar masifeffiyar rayuwace? Yaushe zamu samu Allah ya gama tsarkake mana wannan masarautar Joɗa ya rabata da wadannan tsarabe-tsaraben gargaji.
Wannan wacce iriyar fitinace?".
Dogon numfashi yaja lokacin da ya shigo falonshi,
babu kowa, can babban falo ma babu kowa bisa dukkan alamu duk sunje shirin sallan jumma'a ne.
A hankali ya kutsa kai cikin bedroom ɗin shi.
Kai tsaye bathroom ya wuce.
Jallabiyar jikinshi da hirami da vest ɗin ya cire,
Cillasu yayi cikin injin wonki.
A hankali yake taku kanshi a sunkuye dagashi sai boxes Sky blue.
A hankali ya shiga cikin wurin wonkan.
Kamar yadda ya saba haka yayi wonkan jumma'a anshi.
Bayan ya fitone ya nufi drower'n glass ɗin dake cikin bathroom ɗin.
Wani tattausan Baby towel ya ɗauka bisa saman kafaɗunshi ya ɗauri ya fara gogewa, yana tsane ruwan jikinshi.
Kana a hankali ya ɗauki wanni babban towel ɗin ya ɗaura daga saman ƙirjinshi.
Wanda ya sauƙo har guiwa shi, a hankali yasa hannun ta ciki ya fara murza boxes ɗin yayi ƙasa, dashi yana zuwa sharabanshi ya riƙe shi ya zare ƙafa ɗaya, kana ya zare ɗayar ma.
Lallaɓeshi yayi ya matse kana ya shanyashi kan ƙarfin silver da yake na shanya.
Farar jallabiya ya zura a jikinshi, kana ya kwance towel ɗin. Dashi ya goge suman kanshi.
Cikin hamzari ya fito bedroom,
Kai tsaye gaban dreesing mirror ya nufa, mai ya shafa a dukkan sashin jikinshi. Kana ya taje tattausan suman kanshi tare da shafa mishi manshi, wani Duaol jannah mai masifar daɗi ya shafawa jikinsa, kana ya ɗauki wani ƙaramin kum ya tace tattausan sajenshi ya kontar dashi lib-lib hakama gemunshi.
Saida ya gama komai na gaban Mirror kana ya nufi babban drower'nshi da sauri-sauri yakeyin komai.
Wani tattausan jallabiya mai masifar kyau da taushi fari ƙal ya zaro.
Kana ya ɗan yi sama da kanshi ya kalli cikin tsep ɗin ƙarshe na drower'n inda al'kyabbanshi suke jere a kimtse tamkar shagon saidasu.
Hannu yasa ya zaro wata sabuwa dal tana cikin ledanta tana haɗe da hiramin ta da komai.
Rufe wannan wurin yayi kana, ya buɗe wani sashin inda ƙananan kayan shi ke jere, boxes and singlet ya zaro farara ƙal suma sabbi ne.
Da sauri ya rufe drower'n kana yazo ya ajiyesu bakin gadonshi.
Ba tare da ya cire jallabiyar jikinshi ba, ya saka boxes ɗinshi saida ya dai-dai-ta zamanta a jikinshi da kyau ya kimtsa komai nashi yadda zaiji daɗi tafiya, kana ya zare jallabiyar ya ajiyeta bakin gadon
Singlet ɗin ya yasa, sannan ya ɗauki farar tattausar jallabiya mai dogon hannun ya saka, jallabiyar daya cire ya ɗauka ya gaban ƙaton drower'n nashi ya nufa, wani side ɗin ya buɗe nan ya saƙalata.
Kana ya dawo bakin gadon.
Ledan al'kyabbar ya farka da ƙarfi da kuma sauri sabida ganin tuni ƙarfe ɗaya da rabi tayi, yasan yanzu masallacin ya cika maƙil da mutane.
Ɗan gajeren tsaki yaja, tare da ci gaba da warware al'kyabbar.
Yana gamawa ya zurata a jikinshi, al'kyabbar baƙace, sai gefen bakinta da akayiwa kolliya da wani zare mai masifar kyau Golding color irin mai sheƙi da ɗaukar ido, hakama, kan kafaɗunsa har zuwa hannunta anja zirin irin wannan kolliyar.
da sauri ya dai-dai-ta zamanta a jikinshi, kana
Ya juya ya nufi, gaban dreesing mirror da hiraminshi a hannunshi,
Yana isa ya ajiye baƙin abin, kana ya ware farin hiramin shima da kolliyar Golding color a jikinshi, ya ninkeshi kamar yadda muke ninke dankwali, bayan ya gama ne.
Ya ɗaurashi a kanshi ya dai-dai-ta zamanshi kana, ya ɗauki baƙin abin wanda shima an zagayeshi da Golding color ya sakashi a akanshi, ya fito ras tamkar a Saudia.
Allah ya sani yana masifar son wannan shigar da jin daɗinta a jikinshi babu takura babu matsi gashi ka suturtu da kyau mayu masu kallon tsiya irinsu Jazrahda Batool duk basa iya ganin komai a jikinshi ba.
Da sauri ya nufi wurin aje takalma shi wanda yake na glass ne marfin ya buɗe kana, ya ɗauki wasu takalma irin nasu na sarauta Golding color ne kuma half cover ne, zura jajayen sawunshi yayi a ciki, kana ya koma gaban mirror, wani kolba turaren OudKareem mai masifar ƙamshi mai sanyi, ya fesa a duk sashin jikinsa.
Kana yasa hannunshi ya ɗauki carbinshi. Farin galashi ɗan siriri ya manna a idonshi.
Kana ya juyo da sauri zai fita, sai kuma ya tsaya cike da mamakin ganin. Haroon tsaye ya zuba mishi ido.
Ya buɗi baki zaiyi faɗa sai kuma yayi shiru jin Haroon na cewa.
"Kada kace zakayi faɗa Lamiɗo ne yace inzo in kiraka, lokaci na tafiya fa."
Bai kulashi ba kawai yayi gaba, da sauri Haroon ya bishi tare da cewa.
"Wannan baza ƙamshi haka sai kace wurin amarya zakaje, gsky kayi kyau sosai masha Allah".
Bai kula Haroon ba sabida addu'o'in da yakeyi.
Amman duk da haka saida ya bawa Haroon amsa a zuciyarshi, yake cewa.
"Akwai wani wuri da yafi cancanta da ɗan adam yayi shiga ta tsabta da kyan shiga da ƙamshi sama da masallacin ne? Innal masajida lillafa, duk duniya da babu wurin da Allah ya keɓanta yace dakinshine sai masallatai. Nan zamu gana dashi. Domin idan mu bama ganinshi ai shi yana ganin mu".
Murmushi Haroon yayi, dan Jabeer bai san mgnar da yakeyi a zuci ta fito filiba.
A haka dai suka shiga Masallaci.
Dole yau a gaggauce yayi Kudbar jumma'a dududu 15 minutes yayi yana kudbar kan halaccin mace ta kalli mijin da yakeson aurenta, kamar dai yadda yayi al-ƙawari a wancan satin.
Daga nan aka kabbarta sallah.
A can Rugar Bani kuwa.
A hankali Shatu ta ɗago kanta ta kalli Ba'ana jin tunda suka tsaya baice mata komaiba, ganin yadda ya zuba mata idone yasata, saurin yin ƙasa da kanta,
cikin sanyi muryar tace.
"Ya Ba'ana zamu tafi rana tanayi fa!".
Wani dogon numfashi ya ja ya sauƙe da ƙarfi, kana a hankali ya ƙara matsowa kusa da ita da sauri tayi baya cikin tsoro, hannunshi ya ɗaga mata alamun karta gudu, kai ta jujjuya tare da ƙara matsawa cikin rawan murya tace.
"Ba kyau ina tsoro".
Kanshi ya jingina da jikin bishiyar gamjin da suke ƙasanta, ido a rufe yace.
"Da dai inada niyar cutar dake, da bamu kawo zuwa yau ban cutar dakeba Shatu, kadafa ki mance tun kina ƴar tatsitsiyarki nake sonki kuma nake tare dake, dare da rana, kada ki mance kullum sai kinje gidanmu da dare da asuban fari kin amsowa Ummey mgninta, da har ina son cutar dake da tun wancan lokacin zan cutar dake.
To amman bani da niyar cutarki, ina sonki ne sabida Allah, da kuma gsky da zuciya ɗaya, Shatu koda zaki ƙi yarda dani a kan komai dan Allah ki yarda dani cewa ina sonki, na kuma soki a baya zan soki har gaban abadan, wlh babu ƙarya a cikin soyayyarki a zuciyata, Shatu sonki shine babban raunina a duniya.
Har yau babu wani abu dake firgitani da bani tsoro sai rasaki.
Babu wani abu na duniya daya taɓa sani zubda hawaye sai soyayyarki, dan Allah ki dena zaton dan na matso kusa dake zan cutar dake, ki amince dani in baki abinda idonki zai buɗu da gane sihiri duk ƙanƙantarshi".
A hankali take juya mishi kai cikin sanyi tace.
"Na sani Ya Ba'ana wlh na yarda da kai akan soyayyata, na sani bazaka cutar daniba, tunda baka cutar dani a bayaba, nasan kana sona, na kuma yarda da son gsky kakemin, to amman ni bana son wadannan abubuwa asirce-asircen sabida haramun ne.
A hankali ya zame jikinshi ya zauna kan jijiyan bishiyar.
Ganin haka itama tayi sauri ta zauna bisa guiwowinta ta durƙushe a ƙasa.
Cikin mamaki tace.
"Dan Allah ya Ba'ana meyasa kwanan nan duka sai kayi ta zubda hawaye a gabana, hankalina yana tashi."
Kanshi ya ɗan ɗaga ya kalli sama, a hankali yace.
"Shatu ina sonki zan kuma soki har iya numfashin na, bazan bari wani abu ya rabani da keba, in kuma akasamu wani ya zama ƙaddarar rabani dake, to shi kuwa tabbas zan rabashi da rayuwarshi, kiyi haƙuri in dai a kanki ne zan iya yin komai, na kuwa san duk duniya babu wanda yasan hanyar da za'abi a kamani ko aci galaba a kaina, sai ke ranki ke ɗaya tak ce kikasan duk wani sirrina ban saniba ko zaki iya min halacci ki sirranta min rayuwata".
Da sauri tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa.
"Ya Ba'ana ai rayuwa a hannun Allah take, wata ƙilma in rigaka mutuwa, kuma in dai nice in sha Allah bazan baiyana sirrinka dan a cutar da kaiba, ko ba komai kana soma kuma kace dan zaka nemo su ya Gaini ne kayi wannan tsarin gudun kada mugaye su cutar da kai, Ni na sani Ya Ba'ana waɗannan layun bazasu kareka ba, sabida ba hanyar Allah ka biba amman ni zanyi ta maka addu'a".
Ido ya zuba mata a zahiri da baɗininta gsky ta faɗi dan yaga hakan cikin ƙwayar idanunta.
A hankali ya jawo tandun duma dake rataye a kafaɗunshi, cikin sanyi yace.
"Ga ruwa kisha".
Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa.
"Bana jin ƙishi".
Tura mata tandun yayi gabanta tare da cewa.
"Eh ba mgnin ƙishi bane, kishi dan kiji sanyi a zuciyarki naga kina kuka".
Cikin share hawayenta tace.
"Ba kai bane ka sani kukan kana ta barmin amanar sirrikanka bayan kuma shi amana rikeshi nada girma da nauyi da wuya".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Zaiyi wuya ki riƙe kenan?".
Da sauri tace.
"In sha Allah zan riƙe".
Kanshi ya gyaɗa tare da cewa.
"Bazaki sha bako?".
Kanta ta gyaɗa mishi alamar eh.
Kana ta miƙa tsaye, gaba ta ɗan yi kusa da Rafi'a, tace.
"Rafi'a mu tafi".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Rafi'a ku tsaya".
Cikin tsoronshi Rafi'a tace.
"To Ya Ba'ana".
Da sauri ya ƙara so gabansu, tare da cewa.
"Mata ɗago hannunki mu gani kinada zobene?".
Kai ta girgiza alamar a a babu.
kana ta ɗaga hannunta na dama,
Yatsarshi ya karkaɗa mata tare da cewa.
"Lalala ɗago hannun hagu mu gani".
Cikin gajiya ta ɗago hannunta, fararen tausasan zara-zaran yatsunta suka zubawa ido gaba ɗayansu.
Babu zobe ko ɗaya a yatsunta,
Murmushi yayi kana yace.
"To bari in baki zoben ziyara, koda bakya tare dani, duk lokacin da na nake kusa dake kawai zakiga zoben a yatsunki".
Da sauri ta buɗe baki da nufin cewa a a.
Kawai sai tayi shiru ganin wani irin zoben azurfa mai masifar ƙyalli da sheƙi sai ɗauke ido yakeyi.
Ta juyo zata ce mishi a a Ya cire sai kuma tayi shiru ganin ya ɓace daga gabansu.
Yatsunta tasa da nufin cire zoben da sauri ta barshi jin tamkar yatsunta zasu tsinke.
Rafi'a kam tuni tayi gaba, haka yasa itama tabi bayanta.
Suna zuwa bakin titin suka samu motar zuwa cikin Ɓadamaya.
A can cikin masarautar Joɗa kuwa,
Bayan an idar da salla, kamar kullum Lamiɗo ya gaggaisa da mutane, talakawan garinshi.
Shi kuwa Jabeer dashi da tawagarsa duk sun nufi cikin gida.
Sabida Galadima nata ce mishi su tafi cikin gida su fara shirin tafiya.
Haka yasa duk suka nufi cikin gidan masarauta.
A nan babban farfajiyar suka ɗan tsaya.
Ido Jabeer ya ɗan zubawa jerin motocin da a ƙalla sun kai ashirin da biyar zuwa talatin an bisa alamu anyi manyan baƙi ne ko kuma za'ayi fita mai mahimmanci.
Cikin suka wuce a falo suka samu Umaymah, Hajia Mama, Aunty Juwairiyya, da Ummi, duk suna zaune suna ɗan hira.
Hibba kuwa tana kitchen.
Suna isowa ta fito da sauri jin muryarsu.
A hankali ta isa gefen Jalal cikin yin ƙasa da murya tace.
"Ya Jalal kazo kaci abinci karku tafi bakaci komaiba".
Kanshi ya ɗan gyaɗa mata,
Jamil ne ya hararesu tare da cewa.
"Allah shi ƙara, ai in dai Jalal ne kaɗan kika gani da gwatsalel, mutumin da ba'a iya masa bare a masa gwaninta".
Haroon ne ya ɗanyi dariya tare da cewa.
"Haka suke shida Jabeer yadda suke kamanninsu iri ɗaya hakama halinsu".
Da sauri Jamil ya zare ido tare da ɗan ja da baya yace.
"Tab a a Ni dai wlh bance hakaba".
Jabeer kanshi Jamil ya bashi dariyar da dole ya ɗan murmusa, tuni sukuma sauran dariya sukeyi.
Ya Jafar kuwa shi ganin murmushin Jabeer shine ke sashi murmusawa.
Ita kuwa Hibba tura baki tayi ta koma gefe ta zauna alamun tayi fushi, baibi ta kantaba, sai Jamil ɗin ne ya ɗan lallasheta, haka dai sukayi ta yar raha, saida Lamiɗo ya aiko su fito kafin.
Suka miƙa duk suka fita, shi kuwa Sheykh Jabeer gefensu Hajia Mama da Umaymah ya ɗan rusuna kusa da Umaymah a hankali yace.
"To Umaymah bari inje bisa umarnku ba don raina yaso ba".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Allah ya bada Sa'a ya kaiku lfy ya kuma dawo daku lfy, Allah ya tabbatar mana da al'khairan dake cikin wannan tafiyar, al'farma Annabi da Alqur'ani".
Amin Amin suka amsa baki ɗayansu, Hajia Mama dasu Ummi ma duk sukayi mishi addu'a, kafin ya fito.
Yauma kamar ranar mota ɗaya suka shiga da Haroon da Lamiɗo da Ya Hashim da Laminu.
Kana sauran tawagar sarki.
Daga nan suka nufi hanyar fita gari su nufi garin Shikan.
A cikin motocinsu kamar na ranan.
A tsakiyar garin Ɓadamaya ne suke tafiya sun zo dai-dai bakin Genaral Hospital Ɓadawaya.
Lamiɗo ya bada umarnin cewa su shiga cikin asibitin zai kai ziyarar dubiya wa marasa lfya.
Nan take kuwa suka jujjuya akalan motocin.
Suka fara kutsa kai cikin asibitin.
Da ƙarfi Jabeer ya rumtse idanunshi tare da furta.
"Lahaulawalaqutailla billah".
A hankali sabida wani irin masifeffen bugu da zuciyarshi tayi da ƙarfin masifa.
Wani irin taraddadi ya diro masa.
Ya ilahi shine abinda ya ambata a saman lips ɗin shi.
Dip dab dip dab dip dab dip dab haka zuciyarshi ke harbawa da bugawa a tare a tare,
addu'o'in ya fara karantowa a zuciyarshi da harshenshi, yadda suke ƙara kutsawa cikin asibitin haka bugun zuciyarshin ke ƙaruwa.
Anan cikin asibitin kuwa, A maraba da baƙi Shatu take tun zuwanta sabida, anan aka juye duk fulanin da suka samu rauni sanadin wannan faɗan,
an zubesu a wurin gwamnatin jiha kuma tayi burus da batunsu sam bata bawa likitoci damar dubasuba,
Sai ma cewa sukayi sai fulanin sun nemo polices kafin a karɓesu.
Su kuma dama ƴan agaji ne ma suka taimaka suka kawosu nan ɗin ma.
Zuwan Shatu ne da Rafi'a da ta samesu a yashe hankalinta ya tashi.
Ranta yayi matuƙar ɓaci nan ta haura gidan sama inda can jerin jadawalin officer's ɗin DOCTOR'S suke.
Rafi'a na biye da ita tana rabka mata kira.
"Garkuwa! Garkuwa!! Ke GARKUWA!!! Ina zakije ne wai?".
Sam bata kula Rafi'a ba sabida abin da akayiwa ƴan uwanta yayi masifar ci mata rai.
Ganin yadda take gudu-gudu da sassarfa ne yasa itama Rafi'a ta fara Binta da gudu-gudu