Showing 63001 words to 66000 words out of 110620 words
taji a wannan karon yana Ware yatsuntsa daya bayan daya kamin ya haɗa da nasa Hannun.......... Ɓoyayyen masoyi na........"
*🕊️FƳAƊE....!🕊️*
***Romantic love Sympathetic and Erotic Story.***
*AISHATU MAMAN TEDDY 🧸*
***30***
*Don Allah kar ki karanta mun Idan baki biyani ba , Littafin nan na kuɗi ne Regular group ₦500... VIP group ₦1000... Special payment ₦1500 via 6037312299 Mohammed A'isha keystone bank ko katin MTN ta Wannan number 08081202932...Idan VTU transfer ne sai ki tura kuɗin ki kai tsaye ta Wannan number 09061467409*
```~Tallah~```
To babban magana ina iyaye mata masu san kasancewa da mazajen su har Abada da'iman? Ina macen da matsaloli na Jinnu ko Sihiri yayi mata katutu ya addabi Zaman Auren ta ke dama Rayuwar ki baki ɗaya ...to Allah nacewa tashi in taimake ka . Mata masu fama da Rashin aure shekaru 30 ko sama da hakan duka a gaban iyayen ki abun tun bai damunki a yanzu dole ya fara damunki...” maza garzaya taskar Empire domin warwarewar duka matsalolin ki ...na duba kuma na gani , Maganin ta babu ɓata sam , da Ayar alƙu'ani take magani ba tsafi kawai Kunsan Magani da Ayar Allah , Allah na saurin amsa kamar yankar Wuƙa . Bhuzuwa Empire Aikin ta ya haɗa ta Hanyar alƙu'ani ,tana ma ƴammata marasa farin jini magani da zallar nono , ƙwai ... mallaka babu irin wanda bata yi , na suratul yaseen, Rahman , Izaja'a , jauharatul kalam da dai sauran su ...masu buƙatar ƙarin bayani ga nombobin su kamar Haka 08139762831 Allah ya taimaka Amin .
*Second advert*
*SUFY'S PRINT GRAPHICS DESIGN*
🏷️ PROVIDING A RANGE OF CONTEMPORARY AND TOP NOTCH CREATIVE DESIGN.....
*📍 OUR SERVICES*
✒️LOGO DESIGN
✒️LOGO PACKAGE
✒️ FLYER DESIGN
✒️ BIRTHDAY FLYER
✒️ INVITATION CARD
✒️ADVERT VEDIO
✒️ DIGITAL INVITATION
✒️ STICKERS DESIGN
✒️AND LOTS OF
📝DM NOW....TO GET A TOP NOTCH ATTRACTIVE AND PROFESSIONAL DESIGN
https://wa.me/message/NM3LPR5VMCG6P1
Thanks you for choosing us nd we appreciate refferals 🥰🤗.
Tambaya ta Farko akan Littafin Fƴaɗe.! Me yasa matan Aure da Mazajen su wasu ke bin Maza a waje? . Duk da akwai banbanci akwai gidadawa wanda ƙawa ce ta daura ki a wannan hanyar Halakar ? Kedai Burin kuɗi ko da tsoho ko da waye ma , Akwai kuma Wanda tsaban Son duniya ne yasa suke bin yara ƙanana masu kankantan shekaru daga 20 to 30 . Ga dukiyar suna da shi ,amma sun gummaci suyi zina da yara matasa masu jini a jika . Wallahi Wannan babban ƙalubale ne gare ku matasa , Wannan wallahi babban masifa ne , babba babba ma kuwa .! Don haka a wannan page din zakuji dalilin da yasa Wa'annan mata da suka kashi biyu suke zina da Auren su . Taku har Kullum mai kaunar ku Ayshatou Mamanteddy, da kuma bazarku masoya nake taka Rawa har na juya , na gode ...!
**
Idanun A'isha Farida ne a wannan sa'ilin yayi dulu² Na tsaban kuka da tayi har ta gode Allah, kuma har a wannan lokacin idanun nata basu daina tsiyayar da Hawaye ba . Hannun sa ta kama tana masa Kallon Ƙurilla na Anya kai ne? Girgiza Kai tayi tana ƙanƙane Hannun sa tare da Fashewa da Kuka tana Faɗin " Kai ne Ɓoyayyen masoyi na , Amma ka bar Ni ? Me yasa ka tafi baka Dawo ba ? Me yasa ka tsane Ni a yanzu bayan ka san nice A'isha Farida. ? Me yasa ka lalata mun Rayuwa da tarbiyyan da Mama ta bani tun ina Ƙarama?. Dafe kan ta tayi da ke sara mata idanun ta na ganin duhu ,Wanda Ganin Hakan yasa shi Saurin Tallabo ta yana ƙoƙarin Hadata da jikin shi ne tayi Saurin yin baya . Na tsane ka Ya Aaaryaaan , Bana Son ka .! Ba zan taba Son ka ba har sai ka faɗa mun dalilin ka na keta mun haddi ,bayan kana tare da Mazinata.? Ta ƙare maganan cike da Karaji . Kallon sa tayi wasu irin zafafan Ƙwallah na Zuba mata , wai dama kai ne ? Ashe dama Ɓoyayyen masoyi Mama Gaskiya take faɗa mun akan kar Na yarda da ko wani Namiji wannan abun da kayi mun shine Mama ke yawon fadamin lalata? Wanda ban taba fahimta ba sai a yau . Me nayi maka ?. Kayi mun magana.....! Ta ƙare maganan a zafafe idanun ta na Rufewa na komai zai faru ya faru .
Gani tayi ya tako zuwa Gaban ta , A hankali ya sunkuya a gaban ta Gwiwowin sa ya sanya a ƙasa yana haɗawa da tiles . Idanun sa ne taga yana fidda zafafan Hawaye ,wanda tun da take ko tashin hankali bata taɓa Ganin sa a cikin irin wannan yanayi ba , amma kuma a yau ne yake Hawaye . A'isha Kar kice bakya so na . Tun baki iya Fadin kalmar So ba Nine koya miki. Ko zuwa inda kike nayi furucin ki na farko shine ....Saurin katse shi tayi tana cewa " Shine Ɓoyayyen masoyi ina Son ka , Amma kuma ada baya ne , A yanzu bani da makiyin da ya wuce ka . Malamin can ya fada mun komai , duk wanda yayi mun abin da kayi mun bani makiyin da ya wuce shi a duniya .." Rintse ido yayi kan sa na sara masa Babu shakka a yanzu yasan yaga likita to zai iya ce masa Jinin sa ya hau ko yayi ƙasa .
Rintse ido yayi da ƙarfi , Hannun sa yasa yana goge mata Hawayen fuskar ta . motsa laɓɓan sa yayi yana cewa kan sa tsaye "To muyi Aure . A'isha zaki Aure Ni.? . Cike da jin zafi Duk da idan ta tuna alherin sa sai zuciyar ta yayi mata ba dadi , A'a Ni bana Son ka Wallahi . Ɓoyayyen masoyi nake so , Amma kuma a yanzu na fahimta kaine , Kuma ba zan taba Son wanda ya lalata mun Rayuwa ba .
Kwantar da murya yayi ƙasa Yana cewa " A'isha ba'a son raina bane , ƙaddara ce , kuma Sannan Kaman taimakon ki nayi A wannan lokacin . Sakin baki tayi tana kallon sa ,jin furuncin taimako da yace yasa ka ta Daga Hannun ta tana Ɗaurawa a ka tana yanka uban ihu tare da Fadin " Wayyo Mama zai mun sharri. Hannun sa yasa yana Damƙo ta tare da kwantar da ta jikin sa yana matse ta , gam hannun sa ɗaya yana rufe bakin ta . Ni kika kira mazinaci bayan taimakon ki nayi ? . Kan A'isha Ne ya kulle , Taimako kaman ya kenan ? Yana nufin Nine na kawo masa kai na , nina ce ya lalata dani kaman yanda sauran matan ke yi dashi haka yake nufi?. Ba kuma zan faɗa Miki dalili ba , Amma dole ki So Ni , dole ki ƙi kowa , Idan na kuskura na Ganki da Wani Da sunan so gaba daya kamannin ki zan sauya . Tashi ki fice ki bani Wuri...!
Ya kare maganan yana Miƙewa tare da miƙar da ita yana nufar Hanyar ficewa daga Rest Room ɗin . Tsayawa tayi tana kallon sa idanun ta na cigaba da fidda ƙwallah . Kaman mai Jinnu gani tayi ya tako inda take cikin sanyi yana saka hannayen sa tare da share mata Hawayen idanun ta . Bana Son kukan ki ,ki dai na shi Kinji?. Kallon sa take yi tare da tunani iri² . Me ke faruwa ne ? .
Muryar Mama ya katse su ,wanda basu san lokacin da ta shugo ba sai dai Muryar ta da suka ji . Saurin juyowa Yayi yana kallon Mama Kamin ya kalli A'isha da Har a lokacin take kuka kaman ranta zai fita . Muryar Mama ne ya kuma katse su tana cewa " Naga Yanzu wucewar ta da gudu tayo part ɗin nan a lokacin da suke karatu me ya faru A'isha .?
Cike da matsanancin Kuka Ta buɗe baki tana shirin fada mawa Mama Abun da ya faru , Amma sai kallon ta Aaaryaaan yayi yana hada hannun ta da nashi idanun sa ta kalla , yanda taga tsantsan tashin hankali yasa ta jin wani iri a zuciyar ta . Mama Ɓoyayyen masoyi wai tazo tana mun maganan shi , tana So Gan shi ne .
Cike da shan Jinin jiki Cikin kuma rashin gamsuwa da maganea nasa mama ta dake dai tana cewa " Ayyya A'isha Ki ƙara Hakuri ,za muyi magana da Ya Aaaryaaan akan ɓoyayyen masoyi n....kamin Mama ta ƙare maganan ne ta juya da gudu tana ficewa daga Dakin . Kallon Aaaryaaan mama tayi tana cewa " Ban yarda da maganar ka ba Aaaryaaan, Meke tsakanin ka da A'isha ?. Faɗa mun yanzu naji daga Bakin ka , idan kuma ka ki to zan ji yanzu daga bakin ta ita . Kallon Mama yayi yana kai hannun sa tare da sawa a cikin Sumar kan sa yana ɗan sosa Sumar nasa , Wani irin Ajiyar zuciya ya ja kamin ya ce " Mama Ina mahaukacin Son A'isha Farida. Mama don Allah ki bani Auren ta , tace bata SO na .' idanun sa mama ta kalla nan take jikin ta yayi Sanyi . Kasa masa magana tayi tuno da Maganan da ɗazu Yusrah ta gama faɗa mata , Mama Ina Son Ya Aaaryaaan.! Tsayawa tayi yana kallon ta tana kallon sa . Kamin ta girgiza Kai tana cewa " Aaaryaaan wannan ba mai yiwuwa bace ,ka cire soyayyar A'isha Farida a zuciyar ka." Tana Gama faɗin masa hakan ta juya tare da barin sa anan Wurin a tsaye . Hannun sa yakai yana dukan bangon wurin tare da Furta " Mommy , Mommy Kice kadai zaki iya karba mun A'isha daga Hannun kowa ta so Ni dole . Komai zai iya faruwa dani indai ban Mallake ta ba .
A'isha me yasa kika kasa yafe mun? Ina soyayyar da kullum yake a zuciyar ki a kaina? Dai dai da rana daya ban taba mafarkin Wata ba da jin son kowa sai ke , me kike nufi ? Mahaukaci kika mai dani? Dole ki so Ni....! Duka maganan yake tamkar zautacce .
**
Bayan Fitan A'isha Farida kai tsaye Part ɗin Su Maryamu ta nufa don ta kasa nufar Na mama . hankalin ta a tashe yake , to mene Aaaryaaan zai faɗa mata .? Tun da ta shiga Dakin Yaya Maryamu ta tadda babu kowa anan ta kwanta taci kukan ta har Gari ya fara rufawa . Shigowar Maryamu yasa A'isha Farida Miƙewa jiki a sanyaye tana cewa " Yaya Maryamu bari na tafi Sai da Safe . "
**
Kwance Yusraht take a saman Ƙayataccen Gadon ta . Idanun ta na akan laptop ɗin gaban ta da take karatun distance learning. Mommy Lubnah ce ta shigo Hannun ta dauke da coffee tana faɗin " Har yanzu dai baki fito ba Yusra? To ga Cofee na kawo miki . Juyawa tayi tana muskutawa tare da Fuskar Mumy tana kai hannun ta tare da karbar cup din tana furta " Ohhh thnkyou Mom .
Shafa Fuskar Yusra Mommy tayi a zuciyar ta tana tunanin kwalafaci irin Na Daddyn nasu da Har yanzu ya kasa manta rai daya da yake tsitson shi bayan Allah ya bashi yaya har biyu mace dana miji . Mommy tunanin mene kike yi haka?. Yusrah ta katse Mommy Lubnah wanda tayi saurin sakin fuska tare da ƙaƙaro murmushin dole tana cewa " Ba komai Yusrah , Kawai dai ɗazu na lura kaman bakya cikin Mood me dadi ne ?.
Hummm Sauke Ajiyar zuciya Yusra tayi tare da kallon Hajiya Lubna tana cewa " Mommy ina Wannan yarinyar , wacce ba Maman Aaryaann ta haife ta ba ,wace take ? A'isha ne ko Farida oho dai . Shiiii ya isa Yusraht, kar na sake jin wannan magana daga Bakin ki , don wannan sirri ne babba , babu Wanda yasan A'isha ba Yar Daddy marshal bane . Don haka mu ba kananun mutane bane . Ki natsu . Wani irin kallon Cofee din Hannun ta tayi ji take kamar ta sheƙar a wurin don ɓacin rai . Mommy to kuna shirme ne , don kuwa soyayya ce tsakanin Aaaryaaan da kuma A'isha kun san da haka ..? Tsayawa Mommy tayi tana kallon Yusrah kamin tace " a'a Yusra , babu soyayya tsakanin su , idan kuma akwai to sai dai idan ita A'isha ke son Aaaryaaan ,shi kuma yasan babu Aure tsakanin su . Juyar da kai Yusraht tayi tana cewa " Humm Mommy kenan , To dai suna soyayya kuma a gaskiya ai da Aure tsakanin su a Karyar zance ne dai babu Aure a tsakanin su .kuma ba zan bari haka ta faru ba , Saboda Mommy ina Son ya Aaaryaaan.'
Jin wannan furuncin na Yusra yasa Mommy Lubnah dariya tana cewa " Kin ga inda matsalar taki take nan , don haka kisa ma ranki basa soyayya . Kinji Yusra ta?.
**
A wannan rana kuwa a dinner table Sam A'isha ta kasa hada ido Da Aaaryaan duk kuwa yanda yaso da hakan . Haka a washe gari da safe Naawaaz yazo Gidan wuraren 10am . Fitowar Aaaryaan yasa shi yi masa Wani irin kallo gaisuwar ma sama² suka yi , Magana mama ne yasa shi fahimtar da Yusra suka zo ,kuma wai taje kirar masa A'isha . Nufar hanyar da zai sada shi da Bedroom din A'isha yayi . Inda da idan sa bakin ƙofan yaji Muryar Yusra tana cewa " Kina da labarin cewa ke tsintacciya ce....?
```Fyaɗe.!```
*(Erotic and Sympathetic Story)*
Ayshatou Mamanteddy
***31***
*SUFY'S PRINT GRAPHICS DESIGN*
🏷️ PROVIDING A RANGE OF CONTEMPORARY AND TOP NOTCH CREATIVE DESIGN.....
*📍 OUR SERVICES*
✒️LOGO DESIGN
✒️LOGO PACKAGE
✒️ FLYER DESIGN
✒️ BIRTHDAY FLYER
✒️ INVITATION CARD
✒️ADVERT VEDIO
✒️ DIGITAL INVITATION
✒️ STICKERS DESIGN
✒️AND LOTS OF
📝DM NOW....TO GET A TOP NOTCH ATTRACTIVE AND PROFESSIONAL DESIGN
Whatsapp:07045125150
Thanks you for choosing us nd we appreciate refferals 🥰🤗.
Kina da Wannan labarin kuwa ? . Yusrah ta kuma maimaita mata tana sama da Muryar ta ganin Yanda A'isha Farida Tayi mata shiru idanun ta na kallon ƙasa , Ƙwallah ne suka ciko Ƙwarmin idon ta , A hankali ta motsa laɓɓan ta zata yi magana dai dai Aaaryaan na shigowa Bedroom din . Kallo Ɗaya yayi ma Yusra ya kauda kan sa gyefe tare da kallon A'isha Farida yana cewa " Yusrah me kike faɗa mata? Yayi maganan idanun sa na akan Yusrah wanda Itama shi take kallo tana yin fiƙi² da Ido . Idanun A'isha ne Suka fara Fidda Hawaye masu raɗaɗi domin kuwa bata taɓa fuskantar Wannan ƙalubalen ba a rayuwar ta .
Me kika faɗa mata Shashasha kawai . Ke wacce irin mara Hankali ne , Kina son saka A'isha a tension ne ? Ko kuwa Ƙwaƙwalwar ki matsala ta fara Samu? Ok Lemme told you one thing ,Wallahi kikayi kuskuren Jefa A'isha A cikin wani Hali , Halin da zan saka ki ciki sai yafi na tsanani . Kallon Aaaryan Yusra tayi da take jin tamkar ta kashe A'isha Farida ta huta don tarin bakin cikin ta da take ji da takaici . Ya Aaaryaaan duka abun da nace na kuma faɗi yanzu , shin ba Gaskiya bane? Na faɗa mata ne don tun Wurin tasan inda dare yayi mata...! Tassss Aaaryaan ya Dauke fuskar Yusrah da Mari wanda sai da ta saki yar ƙara tana kifawa tare da dafe Kuncin ta . Yah Aaaryaan Mari na fa kayi ? . Juyawa A'isha Tayi da Sauri cikin matsanancin kuka mai tattare da damuwa tana ficewa daga Bedroom din nata . Bata ko kallon Gaban ta tafiya kawai take har ta isa Falon Mama , inda Hankalin ta ya tashi Ganin Hawaye daga Idanun A'isha Farida . Assalamu alaikum." Sallaman Aslaam da Sadeeq ya katse su . Naawaaz ne ya amsa masu shima ba tare da ya kalle su ba ,don kuwa ganin A'isha yayi masifar daga masa Hankali .
A'isha Meke faruwa ? Hawaye fa nake Gani na zuba daga Idanun ki." Mama tayi maganan cike da Damuwa da kuma son sanin meke faruwa da Ɗiyar nata . Cikin dashashiyar murya A'isha ta kalli Mama Lantana tare da cewa " Mama dama ke ba Mahaifiya ta Bace? . Wani irin bugawa Ƙirjin Mama Lantana yayi saurin dafe Ƙirjin ta tayi tana faɗin " Innalillahi wainna ilaihir raji'un . Naawaaz kuwa saurin miƙewa yayi Don yasan da maganan Amma kuma tuni su Daddy da Hajiya kaka suka ce a rufe wannan maganan?. Mama ba Salati zaki yi ba , Da kunne na naji Inna Hansai tana faɗa mawa Yah Aaaryaan , A wannan lokacin ganin Abin nayi kamar ba gaskiya ba ,kamar a mafarki . Amma kuma a yau ne naji kuma na gasgata Cewa " Mama Ke ba mahaifiya ta bace , Yusrah yanzu take faɗa mun . Mama don Allah Kice mu karya ne ba gaskiya bane ,kece kika haife ki ,kece kika kawo Ni duniya a cikin cikin ki nayi rayuwa na kwanta har na tsawon wata tara . Kuka A'isha Farida keyi cike da ficewar Hayyaci take maganan ko ina na jikin ta Kaɗawa yake Yi , Irin yanda take ihu yasa Aaaryaan Fitowa da Sauri yayin da Yusra ke bin sa a baya . Mama Ke nake So mama,bana Son kowa ta kasance Uwa gare Ni mama Ki faɗa mun mafarki nake yi ne ko Gaske?. Mama Wannan Rikita²n yafi kama mun da mafarki ba Gaskiya bace. Kuka mama ta fashe dashi tare da kamo A'isha Farida tana Rungume ta tsam a jikin ta ,jin ta take tamkar ta maida ta ciki . Ina Mugun Masifar Ƙaunar ki A'isha ta . Ban san ya akayi Haka ba ,ban san ya akayi na kasance ba mahaifiyar ki ba , Amma Allah yafi mu sanin komai . Saurin Ɗagowa A'isha tayi tana kallon Mama ido cikin ido Ƙwallah na cigaba da Kwaranya mata . Mama Da gaske ne kenan ,