Showing 3001 words to 6000 words out of 120733 words

Chapter 2 - SANADIN-LABARINA BY HAFSAT RANO

04 Jul 2024

38891

tana dariya.

"Anty wace wannan?"

Amira ta tambaya tana leken fuskar Jidda da ta rakube a bayan Antyn.

"Ina ruwan ki Amira? Bana son shishigi fa."

Hajjajun dake hakimce ta tsawatar mata tana jan tsaki, murmushi Antyn tayi kawai ta girgiza kai sannan tace

"Yar uwa kuma kawa na kawo muku Amira, gata nan sunan ta Jidda."

Shiru Amiran bata ce komai ba tana tsoron sake magana tasan halin Mama sarai zata iya bugunta akn haka.

"Muje Jidda, naji ma an soma kiran magriba." .
Suka wuce su zuwa wani dogon corridor da zai sada su da bangaren Antyn, daidai lokacin aka kawo wuta, Abu ta ajiye kayan Saudan sannan tace

"An gama tuwon Anty, na fadawa Mama dai a zato na ko har na tafi baki dawo ba."

"Sannu da aiki, kin yi saurin gamawa ma."

"Wallahi, gani nayi garin damina, gwara kayi da wuri kafin ruwa ya sakko."

"Gaskia kam."

"Akwai abinda zaa yi ne kuma?"

"Umm, babu gaskia,zaki tafi ko?"

"Eh idan ba abinda za'a yi ba."

"Babu, bari na diba miki yar tsarabar kauye ba dai yawa."

"Aikuwa nagode Anty."

"Zo Jiddah." ..

Ta yafito ta da hannu, suka shiga daya daga cikin dakuna ukun dake dan madaidacin falon Antyn.

"Ga dakinki kinji, zauna bari na sallami Abu nazo sai na nuna miki yadda komai yake, ki saki jikinki kinji?"

Da kai ta amsa tana kallon dakin, fita tayi taje ta sallami Abun sannan ta dawo tace tayi alwala, itama taje dakin ta, tayi alwala sukayi sallar a tare, sannan ta kunna mata kallo tace tana zuwa.
Part din Maigidan ta nufa bayan ta dora ruwa a saman gas din dake kitchen din bangaren nata, ta gyara masa dakin duk da kafin ta tafi ma sai da ta gyara amma tasan da gayya Maman zata bata musamman toilet, haka ko yaushe take sake gyarawa idan zata shiga ta bata sau dubu bata kuma taba tanka mata ba, yau din ma sai da ta sake gyarawa ta kunna turare sannan ta fito, ta dawo ta samu ruwan ya tafasa ta cika flask sannan tayi masa tuwon alkama wanda zai ci yanzu da kuma safe, ta zubawa Saudah a ciki ta kirawo ta kitchen din duk dan ta sake da ita, ta karba ta fita, Usman da ya gama zaman falon ya shigo ya haye kafar Jidda yana mata magana

"Kece Yayarmu da Anty tace zata kawo mana ke?"

Gid'a masa kai Jidda tayi, sannan tayi masa murmushi

"Zaka ci tuwo?" Tace masa tana kallon plate din dake gabanta.

"Naci tare da Muhammad, amma zan kara naki."

"Toh muci."

Ta tankwashe kafarta shima sai yayi yadda tayi, suka shiga cin tuwon a tare, har suka gama Anty na ta kaiwa da komowa a tsakankanin bangaren Maigidan da nata, sai da ta gama hada masa komai sannan ta nutsu ta zauna taci abincin ta watsa ruwa dan a gajiye take jin ta sosai dan ba wani zama tayi ba tunda suka shigo. Wajen takwas da arba'in Baban ya dawo, sun idar da Isha Usman yayi bacci, Antyn tace itama Jiddan taje ta kwanta, ta rakata har daki ta nuna mata duk abinda zata bukata ta kawo mata ruwa saboda dare sannan ta dauko Usman ta dawo dashi dakin tayi musu addua sannan ta kashe musu wutar dakin ta nufi bangaren Baba.

***A zaune ta samesu da Mama, ta bararraje tamkar kwananta ne ranar, ta bude masa abincin har ya soma ci yana bata labarin kasuwa, wani banzan kallo maman ta watsa mata, tayi tsaye ranta na sosuwa da abinda ake mata, dagowa yayi ya kalle ta,

"Halima, karaso mana kika ja tunga anan, kinga yayarki ko? Wai kin sha wahalar hanya shine take taimaka miki da wannan babban aikin."

Yake tayi ta karaso ta zauna daga kubin damar sa, ta gaishe shi a ladafce ya amsa mata yana tambayar yadda ta baro su

"Ina fatan dai kafar Yaya da sauki."

"Alhamdulillah dai toh.

"Allah ya bashi lafiya, zan yi kokari a weekend din nan naje na sake dubo sa, ina yar taki? Kin taho da ita ice ko?"

"Eh tayi bacci."

"Ok madallah, na ganta gobe idan Allah ya kaimu."

"Amin." Tace sai ta mike ta shige bedroom din ta zauna a sanyaye, sama-sama take jiyo hirar su har wajejen goma na dare sannan taji tafiyar Maman. Kwanciya kawai tayi dan babu kuma bukatar ta sake komawa falon.



_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

_BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_

_4 BOOKS  4500_
_3 BOOKS : 3500_
_2 BOOKS : 2500_
_1 BOOK: 1500_

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107
[11/25, 3:54 PM] Rano2: Sanadin
             Labarina
               
                   Free Page ( 3)


©®Hafsat Rano

***

***Kiran farko akan kunnen ta, saboda yadda jikinta ya saba da tashin wuri, dan tun bata iya tashi ba har ya zame mata jiki, ko bata ji kira ba zata mike, wataran ko sallah Lami bata barin ta tayi zata fara sakata aiki, itace dauko itace, itace debo ruwa da sharar gidan baki daya dan duk sai tayi su kafin ta tafi makaranta wadda take da yar tafiya tsakanin su, haka ta saba ta goge tun shekarun ta basu kai haka ba, babu wani aiki da yake bata wahala sai dai idan ba sunan sa aiki ba. Zama tayi jugum tana kallon yanayin dakin, ta kalli Usman da yake bacci a gefenta, tana matukar son yara, haka take ko a gida bata da aiki sai jajibo yaran makota kafin Lami ta hanata. Turo kofar akayi, Anty ta shigo sanye da Hijabi, ganin ta a zaune ya bata maki

"Har kin tashi Jiddah?" Tace tana karasowa cikin dakin

"Tun dazu na tashi."

"Toh maza tashi kije kiyi alwala muyi sallah, Usman be yi kuka ba ko?"

"A ah be yi ba."

"Toh yi alwalar maza kizo muyi sallah."

"Toh." Tace ta sakko, taje tayo alwala suka fara yin raka'atanil fajr sannan sukayi subh. Al'kurani ta dauko suka fara daga Falak da Nasi, zuwa in da Jiddan ta tsaya a karatun, ta yaba sosai da yadda take karatun dan batayi tunanin hakan ba duk da baffa ba daga nan ba wajen riko da addini. Suna zaune tare har garin yayi sha, tace mata ta koma ta kwanta, ita kuma ta fita zuwa shashen Baban dan tasan zuwa lokacin ya dawo daga masallaci. Tana fita ta fito itama ta je kitchen ta dauko tsintsiya da faka dan ko ta kwanta ba wai iya baccin zatayi ba, bata saba ba, ta share falon tas ta gyara kitchen ta wanke kwanukan da suka bata jiya da daddare sannan ta wanke toilet, bayan ta gama usman ya tashi, ta rakashi bandakin tayi masa alwala da brush sannan tace yayi sallah, be iya ba tunda karami ne haka yayi tana kallon sa.
  Wajen takwas Antyn ta dawo shashen sai dai tsananin mamaki ya kamata, ganin yadda ta gyara ko ina kamar ba ita ba, murmushi kawai ta dinga yi tana wa Allah godiya da ya duba ta ya bata 'ya me taimaka mata. Kunun da Abu ta dama tazo kawo wa kawai taga yadda ta gyara ko ina, albarka ta dinga saka mata sannan tace taje tayi wanka zata je ta gaida Baba idan sun gama karyawa.
   A babban falon suke karyawa gaba dayan su, har Baban dan yace cin abinci a tare yana kara shakuwa, shiyasa suke zama kowa yaci da dan uwansa musamman weekend da baya fita da wuri sai rana ta daga. Fitowar ta kenan daga wanka ta gama saka kayanta tana goge ruwan da yake akan fuskar ta Amira da ta sato hanya ta leko dakin fuskarta a sake,

"Kawata." Tace tana sako jikinta cikin dakin

"Amira." Ta kira sunan ta da taji Antyn ta fada jiya, hakan yayi ma Amiran dadi

"Jiddah ko?" Kai ta daga Mata

"Kizo muje mu karya, kinsan gaba daya muke yin breakfast har Baba."

"Hadda ni?"

"Eh, kema kin zama yar gidan nan ai, taho muje."

Ta ja hannun ta suka fito, bata so ba dan tana da jin kunya sosai da rashin saurin sabo, bata kuma saba da mutane da yawa ba daga ita sai baffanta sai Inna Lami. Sun firfito dukkan su kowa na zaune wasu a kasa wasu a saman kujera, su biyu ne mata a zaune Maryam, sai Safiyya wajen su Amiran ta jasu, tace

"Ya Sofy, Mero, ga Jiddah."

"Sannun ta."

Safiyyan tace tana danna wayarta, babba ce dan da alama duk ta girme su,  murmushi sauran sukayi mata hakan ya sakata sakin jikinta kadan ta zauna a gefen Amiran ta makale. Maman su ce ta fito ta wata kofa taci ado sosai, kamar wadda zata tafi gasar kyau, babba ce dan akalla shekarun ta zasu kai arba'in da biyar amma ba zaka taba cewa ta kai ba saboda gyara da kyawun jiki. Duk suka gaishe ta ta amsa idon ta akan Jiddan, da sauri tace

"Ina kwana?"

"Lafiya lou bararoji."

Tace tana wucewa kujerar da Muhammad da Usman suke zaune,
Suka tashi ta zauna tana hararar Amira. Bararojin ne ya dinga yawo a kwakwalwarta har akayi sallama aka shigo falon. Baba ne ya shigo Anty na biye dashi itama tayi wanka sai dai shigarta very simple ba kamar Mama ba, gaishe da Maman tayi da yake a gaban Baba ne ta amsa a sake, zama sukayi dukka sauran yaran suka gaida Antyn da Baban itama sai tabi sahun su ta gaida Baban.

"Zo 'yata,yanzu nake shirin tambayar ki dama."

Tashi tayi a kunyace taje gabansa ta durkusa ya shafa kanta

"Ki saki jikinki kinji, nan gidanku ne ga yan uwanki nan dukkansu,duk abinda kike bukata ki sanar dani kinji?"

Daga kanta tayi alamar toh, ya sake shafa kanta yace

"Yawwa, Allah yayi muku albarka baki dayan ku."

"Amin."

Suka amsa gaba daya, ran Mama ya baci sosai amma bata so ta nuna ta danne tana kallon Safiyya da itama ita take kallo.

"Maryama jeki kira yayanku, bansan me suke ba na kuma fada musu da wuri zamu fita."

"Wani wajen zaku ne?"

"Eh zamu je a dauko Yaya, hutun ya isa haka gashi lokacin komawa ganin likitan ta yayi."

"Gaskia."

Tace a kasan ranta kamar ta kurma ihu, bata san zaman Yayan tare dasu musamman tun bayan da ta tirsasawa Baban ya kara aure tun daga sannan ta tsane ta, dan tun asali dama Yaya bata son ta, shiyasa sai da tayi yadda tayi ta saka ya auro mata wadda ko a mafarki bata taba kawo ta a matsayin kishiyar ta ba,yar kauye kuma yar talakawa, ita din yar masu kudi ce sannan tana business dinta tana samun kudi sosai, tun daga sannan ta kullaci Yayan, tafiyar da tayi tsawon wata guda ya bata damar sakewa a cikin gidan, jin zata dawo yanzu ya saka ta kasa ko sakewa taci abincin, ta tashi tace zata tafi, Safiyya ce ta rike mata jaka suka fice tare.
A harabar gidan ta hadu dasu, Fauwaz ne a gaba sai shi a baya yana nannade hannun rigar sa zuwa sama, kansa kasa fuskar sa babu yabo babu fallasa Safiyya ta kira sunan sa ganin zai wuce su

"Ya Tariq!" Tsayawa yayi yana kallon ta, kafin yace

"Mah, fita zakuyi?"

"Eh, zamu je cikin gida."

"This early?"

"Past 9 fa, kai kake ganin yayi wuri."

"Ok a gaida su."

Ya sa kai ya cigaba da tafiya zuwa main part din, mota suka shiga Fauwaz ya bi bayan sa, ya sameshi har ya zauna a gefen Baban suna magana, Zama yayi shima ya gaishe da Baban dan shi kadai ya rage a falon duk sun shige ciki. Breakfast din sukayi a tare, sannan Baba yace Tariq yaje ya sauya zuwa manyan kaya, ba a san ransa ba ya chanja zuwa shadda dinkin rigar da kadan ta wuce guiwar sa, ya rike hular a hannu ya fito yana jin shi a takure.
   Cikin gidan ya shiga, ya bi corridor din da zai kaishi part din Antyn, ya shiga bakin sa dauke da sallama kasa-kasa. Su uku ne a zaune a falon, Saudah, Amira da Umaima. Fitar Mama ya basu damar biyo Saudan suka zauna suna janta da hira, Amira ta saka musu waka suna ji ya shigo, a rikice ta danne power botton din wayar ta kashe ta gaba daya, kallon ta yayi ,yayi kamar be ji komai ba, ya wuce ya zauna a cikin daya daga kujerun falon yana ciro wayar sa. A tare suka hada baki da Umaima suka gaishe shi, yayi kamar be ji ba, yana cigaba da danna wayar sa. Sum sum sum suka fice ya zama sai Jiddah kawai a falon

"Ke je ki kira min Anty."

Yace be ko dago ba, ta mike ta nufi dakin Antyn ta kwankwasa, daga ciki tace mata ehem alamun tana toilet, dawowa tayi ta tsaya daga bayan kujerar tace

"Tana bayan gida."

Dagowa yayi jin abinda ta fada, sai a lokacin ya ganta, fuskarta fiki fiki, yar firit kamar ka hureta ta fadi saboda rama, mamaki ya kamashi ganin ta

"Wacece ke?"

Yace yana kafe ta da ido, sosai ta duburburce ganin yadda ya kafe ta da ido, idanun sa manya sosai masu ban tsoro

"Na'am?"

Tace cikin hada kalmonin

"Who are you? Daga ina kika zo?"

Ya sake tambayar ta har lokacin kallon ta yake,be taba ganin ramammiya karmashashiyar yarinya irin ta ba, shi ya zata ma aljana ce, saboda tsabar rama har wani rami ne a fuskarta ya shiga ciki. Bata san amsar da zata bashi ba, sai kawai tayi shiru tana wasa da hannun ta. Anty ce ta fito a daidai lokacin

"A ah, Yaya boss yaushe ka shigo?"

"Ban dade ba, ina kwana?"

Yace yana dauke kansa dga kallon yarinyar

"Lafiya lou, baku tafi ba ashe."

"Eh Baba be gama shiryawa ba, shine nace bari na shigo mu gaisa,wacece wannan Anty?"

"Auw wai Jidda? Jiya na taho da ita yata ce, yar wana ce amma ta dawo hannu na da zama."

"Ok."  Kawai yace yana tabe bakin sa, sai ya mike

"Nima gobe zan koma in sha Allah, zan dade wannan karon har sai na kammala sannan zan dawo."

"Wai, Masha Allah, zamuyi kewa. Allah ya bada saa da nasarar abinda aka je nema."

"In sha Allah Amin."

Yace yana ficewa, d'aga murya tayi tace masa a dawo lafiya ya amsa daga chan ya karasa ficewa.

_ZAFAFA BIYAR_

*_INAYAH_*
_MamuhGee_

*_GURBIN IDO_*
_Safiya Huguma_

*_SANADIN LABARINA_*
_Hafsat Rano_

*_FARHATAL QALB_*
_(Miss Xoxo)_

*_BABU SO_*
_Billyn Abdul_

_*Littafi daya 300*_
*_Littafi biyu 400_*
*_Littafi uku 500_*
*_Littafi hudu 700_*
*_Littafi biyar 1k_*

_BREAKDOWN OF ZAFAFA BIYAR VVIP SINGLE PAID BOOK_

_4 BOOKS  4500_
_3 BOOKS : 3500_
_2 BOOKS : 2500_
_1 BOOK: 1500_

YADDA ZAKU BIYA KUDIN BOOKS👇🏾👇🏾👇🏾

ZENITH BANK
HAFSAT UMAR KABIR
2270637070

SEKU TURA SHEDAR BIYA TA:
07040727902

IDAN KUMA KATI NE SEKU TURAWA👇
09134848107

    
[11/25, 3:54 PM] Rano2: *Sanadin*

               *Labarina*

                     Free Page (4)

©®_Hafsat Rano_

** Tariq ne yake tuka motar Fauwaz na gefen sa,Baba a baya yana duba labarai a wayar sa jefi jefi suna hira da Fauwaz wanda shima rabin hankalin sa yana kan wayar sa yana duba wani pdf. Be fi sau biyu Tariq ya saka musu baki a hirar da suke ba har suka isa garin su Baban in da zasu dauko Hajiya Yaya
A kasan wata bishiya yayi faking kannen Baban dake zazzaune suna shan inuwa suka mike dukka suka yo wajen motar. Fauwaz ne ya bude ma Baba kofa ya matsa baya ya fito, ya shiga mika musu hannu suna gaisawa, kananan kuma suka russuna suna gaishe shi.

Cikin gidan suka dunguma suka shiga gaba daya, zuwa tsohon shashen Yayan kafin ta koma birni tun daga zuwa wani asibiti da tayi Baban yace tazo kenan, bata son birni sam amma babu yadda ta iya haka dai ta hakura bayan ya samu wasu daga cikin yan uwanta sun saka baki, duk da haka bata son zaman ta a cikin gidan sa dan ba wani shiri suke da Mama ba, ita Yaya dama bakin ta baya shiru bata gani bata tanka ba shiyasa tasu sam bata zo daya da Maman ba, tace Maman ta fiya isa da izza dan iyayenta wasu ne, shiyasa da Baba yazo mata da maganar auren Halima ta bada goyon baya dari bisa dari dan a ganin ta a lokacin ne zai auri daidai dashi.
Hayaniyar Yayan suka fara ji tana ta fada da sababi, muryar ta a sama sosai ta dage tana fada bilhakki da gaskiya, murmushi Baba yayi, ya girgiza kansa yayi sallama a tsakar gidan, muryar sa ta sakata yin shiru ta amsa sallamar tana jefar da sandar da yake hannun ta. Fuskar Tariq a hade dan shi ba kasafai ya fiya son hayaniya da shiga cikin mutane ba duk da Baba yana tirsasa masa shiga cikin yan uwan sa dan suna da matukar yawa, yanayin sa ne a hakan kamar Safiyya, su suko yo Mama dan itama bata cika son mutane ba sai wanda tayi mugun sabo dashi.
Shima kamar Maman ba shiri suke da Yayah ba, dan kullum yi masa korafi take bashi da sakin fuska, surutun ta shi yafi komai damun sa, dan idan ta fara magana baya jin ko hadiyar yawu tana yi. Fauwaz ne dan dakin ta da Amira, sune suka yo ta a surutu da kwashe kwashen mutane kowa nasu ne.
Tabarma ta dauko zata shinfida musu fauwaz ya karba ya tayata, ta zauna a gefen gadon ta suka gaisa da Baban sannan su Fauwaz din suka gaishe ta ta amsa tana ficewa taje ta kawo musu ruwa ta ajiye sannan tace

"Ashe zaku zo, na dauka fa sai wani satin wallahi, ban gama abubuwan da nake anan din ba."

"Menene baki gama ba Yaya?"

"Em.. em akwai wani biki na yar Hajara nan kasa damu, babu dadi ace ban tsaya an yi bikin dani ba."

"Ayya, sai a basu hakuri Yaya, kinga fa lokacin komawar ki wajen likita yayi har yana neman wucewa."

"A ah gaskia ba zaa basu hakuri ba, sai dai a bani gudunmawa me tsoka na bata, sai kuma ka aiko matar ka itama tazo ranar bikin da gudunmawar ta."

Tace tana yin kicin-kicin da fuska, murmushi Baba yayi yace

"An gama Yaya, sai kuma me?"

"Shikenan, sai mu tafi tun da kayi niyya, ni wallahi dan ba yadda zan ne, a kai mutum a ajiye shi waje daya haba!"

"Kiyi hakuri Yaya."

"Idan ban hakuri ba ya zanyi toh? Fatan dayafi karfin ka ai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login